Showing 162001 words to 165000 words out of 245004 words

Chapter 55 - Abban Sojoji Book 2 Complete Pdf Download

17 Mar 2025

25267

ƙaunarshi takeji kamar kamar me,fiye da yarda take jin ya omar ma lokacin da taso shi,saboda shi son da tayi mashi hada ƙarin don ta kyautata mashi ne akan irin ɗawainiyar da yake yi dasu,shi kuma kalar son da take yi ma junaid kallo ɗaya tayi ma kyakkyawar fuskarshi tabi ta rikice,kuma tunda Omar ya furta cewa ƙaninshi ne nan take taji ya kwanta mata aranta,sai dai abunda jahad bata sani ba shine,junaid ba babba bane kamar yarda take tunani,

**********haroon
Gaba ɗaya ya rikita ɗakin nashi wurin neman kuɗin da su Twins suka bashi,sam hankalin shi ya gaza kwanciya yama rasa inda zaisa kanshi,wata irin zufa ce ke gangaro mashi a fuskarshi saboda tsabar 6acin rai,yafi ƙarfin awa 2 yana neman jakar kuɗin amma babu ita ƙasa ko sama,an ɗauke ta daga ɗakinshi babu ita babu alamarta,yayi ma bedroom ɗin nashi kaca kaca wurin binciken inda jakar kuɗin take,kamar zaiyi hauka saboda yarda ya zauce,sun rigada sun gama tsara plan ɗinsu,
shirin tafiya kawai ya rage mashi daga zuwa ya ɗauki jakar kuɗin an ɗauketa daga ɗakinshi,gashi ya rasa wanda ya shigo har cikin bedroom ɗinshi ya ɗaukar mashi ita,komawa yayi gefen gadonshi ya zauna yana faman huci kamar wani zaki,tunani ya shiga yi wanene zai iya shigowa ɗakinshi ya ɗaukar mashi jakar kuɗin shi?kodai su twins ne suka yi mashi wayau,don sunsan cewa ya goge videon shine suka ɗauke jakar kuɗin,tabbas kuwa sune saboda su kaɗai ne suka san da kuɗin acikin bedroom ɗinshi,
Jinjina kanshi yayi yana huci yace"yara kenan harni zakuyiwa wayau,ƙananun ƴan iska kawai masu kwana da wando,saboda sun mayar dani shashasha shine suka zagayo ta bayan idona suka ɗauki jakar kuɗin,wlh sai kunyi danasani saina illata rayuwarku gaba ɗaya muddin baku maido mun da kuɗina ba,"ya faɗi a lokacin da ya miƙe tsaye zumbur yana faman naushin tafin hannunshi na dama da hannunshi na hagu,tashin hankali da ba'a sama shi date,

**********************Amani
Zaune take saman 3 seater,yayin da Amal ke zaune kusa da ita,ta fito fess abunta tayi wanka ta bata kaya ta canza duk da rigar tayi mata yawa saboda kayanta ne taba ma amal ɗin ta sanya kafin zuwa gobe zata je da ita shopping mall ta zabi abunda take so,ta kuma yi mata siyayyar kayan sawa da sauran abubuwa na rayuwa wanda zata buƙata,
Hannunta na ruƙe da wayarta,shiga contact ɗinta tayi tare da nemo numbar Aunty babba ta buga mata call,nan take wayar tashiga ringing,

Hafsat na faman zarya acikin parlourn nasu taji shigowar kira a wayar mommynta dake ajiye saman hannun kujera,cikin sauri takai hannu tare da ɗaukar wayar,ganin sunan Amani ya bayyana ne yasa ta juya tare da tunkarar kitchen ɗin,tunkan taƙarasa aunty babba tafito daga kitchen din jin ringing ɗin wayarta,miƙa mata wayarta tayi tare da cewa"Amani ce ke kira,"
Yatsina fuska tayi tare dasa hannu ta kar6i wayar bayan tayi picking ta kara wayar a kunnanta tana cewa"Sai yau kika tuna dani"?_
on the other hand Amani tace"Am really sorry auntyna takaina,kullum kina araina,kawai abubuwane sunyi mun yawa,"
tsoki aunty babba taja tare da cewa"Abubuwa su kayi maki yawa,ciki gare ki ko goyo"?_
Amani tace"ko ɗaya daga cikinsu babu,pls mubar zancen ae nabaki haƙuri,yanzu akwai maganar da nakeso nayi maki pls,"
Aunty babba tace"kunne ke ji,"
"dama maganar Amal ne!wai har yanzu ba labarinta?ba'asan inda take ba?nagaza samun kwanciyar hankaline saboda mafarkin da nayi jiya agame da ita,"
Shu'umin murmushi Aunty babba tasaki tare da cewa"Yawwa dama inaso nayi maki magana game da Zancen neman Amal,munyi waya da mammy ta sanar dani cewa an samu wasu malaman da zasuyi mata sauka,manyan malamai ne na addini kuma da zarar sunyi saukar nan ake cin sa'a buƙata ta biya,"
Ƙiriss ya rage Amani ta saki dariya,don tsabar takaici da ban haushi,aranta tace wai sai yaushe matar nan,zata daina ƙarya ne?
Juyawa tayi ta ɗan kalli Amal dake zaune hankalinta kwance idonta na kallon plasma tv ɗin dake facing dinsu,tana kallon tashar mbc 3,
gyara murya Amani tayi tare da cewa"Masha Allah,gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba auntyna takaina,ashe ansamu wasu malaman ae ni indai akan Amal ne ko nawa ne zan iya badawa,ko bani dasu zan nemo ne,'_
Jin haka yasa aunty babba,janye wayar daga kunnanta tana faman 6a66aka dariyar mugunta,duk hafsat na tsaye tana kallonta baki asake saboda tasan da zancen neman Amal ɗin,kuma a gabanta Jiya abra ta kira mommyn nata tana sanar da ita cewa Amal ta gudu,sarai tasan cewa yarinyar ta gudu shine kuma takeson ƙara cutar da Amani saboda tsabar son abun duniya?
"Yanzu nawa zan tura kenan"?acewar Amani,
Aunty babba tace"ba wasu kuɗine masu yawa ba,dubu ɗari takwas ne,ae ni nayi mamakin ma yarda suka faɗi kuɗin da sauƙi har haka,"
murmushin takaici amani ta saki kafin tace"okey,zanyi maki magana indae na samu kuɗin,yanzu dae mu koma zancen Hayaam,shin har yanzu tana maid ne ko tazo Abujan nan"?
"Tun jiya fa ta ƙaraso,yanzu ae ta jima da zama ƴar gida,"ta ƙarasa maganar tana washe baki,anzo inda tafi auki,
ɗan ta6e baki amani tayi tace"Okey yayi kyau,yanzu komai zai fara tafiya dai dai,akwai wani albishir da zanyi maki,"
Natsuwa Aunty babba tayi tare da cewa"ina sauraronki ƙanwata,faɗamun albishir ɗin,"
Shu'umin murmushi Amani tasaki tare da miƙewa daga saman sofa ɗin tabar Amal zaune tana kallo,takawa tayi nesa da falon,sannan tace"Nasan inna faɗa maki albishirin nan ko bacci ba zaki iya yi ba saboda tsabar farin ciki,"
A ƙagare Aunty babba tace"dan Allah shaƙamun mana kanwata wane irin albishir ne wannan,
Murmushi Amani ta kuma yi sannan tace"nasamo ma Hayaam maganin mallaka a wurin wani hamshaƙin boka,aikin shi tamkar yankan wuƙa yake,saboda Ni shaidace akan idona aka ta6a amfani da maganin kuma yaci,"
Cike da farin ciki Aunty babba tace"Wai dagaske"?
dariya amani tayi tare da cewa"dagaske mana!,wata neigbour ɗinace keson ƙanwarta ta auri ƙanin mijinta,sun rasa yarda zasu jawo hankalinshi acikin gidannan saboda mutunne mai matuƙar ji dakai,kamar dai sgr,ina baki labari kwatsam sai ga wata ƙawarmu ta bamu labari akan wani shu'umin boka,agabana aka shirya zuwa wurin bokan suka amso maganin,a yanzu dai labarin da nake baki,yarinyar na nan ta aure shi hada ciki ma sai faman shan soyayya suke abun gwanin burgewa,"_
Saboda tsabar Murna Aunty babba ta gaza rufe bakinta dakyar ta iya cewa"Yanzu ya za'ae kenan asama ma Hayaam maganin?nawa zamu nema"?
"Ko sisi basai kin bada ba Auntyna,fisabilillah na amso ma hayaam maganin da kuɗina ai nima kanwata ce ko,nidae burina shine inga ta auri sgr Abra kuma ta auri marshal Omar,"
washe baki Aunty babba tashiga yi tana cewa"Allah sarki Amani,ashe haka kika damu da ƙannen namu?gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba,yanzu kenan Hayaam zatazo ta kar6i maganin gidanki kenan"?
Amani tace"eh,in ma batasamu zuwa ba ni zanje nakai mata shi,babu damuwa,"_
Sun jima suna waya kafin daga bisani firar tasu ta ƙare anan,
Tuntsirewa da dariya Aunty babba tayi tana tafa hannu tashiga cewa"ban ta6a ganin ƴar wahala ba irin Amani,duk irin abunda nakeyi mata amma ita burinta ta taimakamun wurin ganin na cimma burina,gaskiya na tausaya mata,abun tausayi,
girgiza kai kawai hafsat tayi tare da wucewa ciki tabar mommyn nata tana ta faman sambatu,
A can 6angaren kuwa fashewa da dariya Amani tayi tare da cewa"Aunty laila kenan!ke atunaninki kinyi mun wayau bakisan cewa Amanin da kika sani ada ba ita bace ayanzu ba,ashirye nake dana kwance dukkan wasu notikan kanki,zan mayar dake kamar wata zararra,ita kuma hayaam zanyi amfani da wannan damar wurin ganin na canza mata halittar jikinta,kamar yarda kuka canzawa Amal kamanni ta tsotse ta rame ta ƙanjame haka itama nakeson ta koma,dama ance ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,that's my plan!

Tana faɗin hakan ta juya tare da komawa wurin Amal ta zauna,kallonta Amal tayi tare da cewa"Aunty amani,dan Allah kiyi haƙuri da abunda zan faɗa maki,bansan ko zai 6ata maki rai ba,nasan cewa su mammy sun cutar damu sosai,amma kada kice zaki ɗauki fansa,mubarsu da Allah kawai shi zai saka mana,sannan in zamu iya mu taimaki mahaifinmu don yana cikin mawuyacin hali"
Shuru kawai amani tayi batace mata komai ba,amma fa har yanzu tana akan bakanta,maganar mahaifinsu kuwa tasan matukar mammy na numfashi bazata barshi ya sarara ba,don ba karamar shedaniyar mata bace,ita kanta yanzu tana shakkun in don Allah aka hadata da Abbas.

_💋Boss Bature💋_

______________________tunda yadawo daga masallaci yake jin jikinshi wani irin yanayi mara daɗi,bedroom dinshi ya shiga tare da nufan saman gadonshi ya haye yana faman sauke ajiyar zuciya,pillow ya jawo tare da aza kanshi a saman shi yana faman lumshe ido,yana cikin wannan yanayin yaji fitar wani abu daga hancinshi mai ruwa ruwa,cikin sauri junaid ya tashi daga zaune yana kallon pillown nashi,zuba ido yayi yana kallon jinin daya ɗigo daga hancinsa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,kafin yayi wani yunƙuri sai ga wani ɗigon jinin ya sake fitowa daga ƙopan hancinshi,abu kamar wasa jinin ya dinga ɗiɗɗigowa saman bedsheet ɗinshi,
  Hankali tashe junaid ya sauko daga saman gadon da saurin gaske ya faɗa cikin toilet ɗinsa,kai tsaye ya nufi wash basin,dafa shi yayi yana kallon fuskarshi acikin mirror ɗin,hancin shi yabi da kallo ganin yarda hancinshi ke cigaba da bleeding,sam bai damu ba saboda yasan cewa yana yawan yin nose bleeding,don haka tunaninshi ha6o ne kawai,
  Hannu yakai tare da kunna tap ɗin,ruwa ya soma shararowa da gudun gaske,tarba hannunshi yayi tare da ɗebo ruwan ya watsa a fuskarshi yana wanke blood ɗin,murzar wurin ya shiga yi don jinin ya tsaya amma yaƙi daina zuba,ya kusan 15mins a haka sannan jinin ya dakata da ɗigowa,ajiyar zuciya ya saki tare da kai hannu ya kashe tap din,
  Sannan ya fito daga cikin toilet ɗin,yana ƙoƙarin ɗaga ƙafarshi ya nufi gadonshi,wani irin jiri ya kwashe shi,hannu ya aza asaman kanshi tare da ambaton sunan Allah,yayin da idanunshi ke ganin mashi biji biji,
  Yana cikin wannan yanayin Sehrish ta faɗo cikin ɗakin ambaton sunanshi ta shiga yi "junaid, junaid.....,"
  ganin shi atsaye abakin ƙopar toilet ya sata tsayawa tana kallonshi tare da cewa"baby junaid meya faru ne naganka haka?baka jin daɗine,"
   Jin muryarta yadinga yi acikin kanshi tamkar ana buga ganga,hakan yasa ya yanke jiki zai faɗi gadan gadan,
  A wani irin slow sehrish ta ƙarasa wurin da sauri ta ruƙo shi suka faɗi ƙasa atare,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin yarda yake kokowar fitar da numfashinsa,hankali a matuƙar tashe take faɗin"Innalillahi_!junaid!meke faruwa dakaine!me yake damunka ne?ka faɗamun dan Allah,
   Ko iya ɗaga la66ansa ba yayi bare ya iya furta mata wata kalma,hannunshi dake kerma yasa tare da ƙara ƙanƙameta sosai ya kwantar da kanshi asaman ƙirjinta yana cigaba da ƙoƙarin fitar da numfashinsa,hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,tuni ta soma fitar da ƴan matan hawaye,yanke shawarar zuwa ta sanar ma wani tayi don a hanzarta zuwa aga halin da yake ciki,ƙoƙarin janye jikinta tayi daga nashi,tamkar zata rabashi da ranshi haka yaji,ƙanƙameta ya kuma yi sosai da sosai sai lokacin ya iya furta"rishi kada ki tafi ki barni a yanayin da nake ji zan iya mutuwa,"
Cikin shessheƙar kuka take cewa"junaid ka bari inje in sanar dasu,idan wani abu ya same ka fa"?
   "A'a nidai kada ki tafi kibarni,"ya ambaci hakan da wata irin kasalalliyar murya,tsananin tausayinshi ne ya kamata,mayar da hannunta tayi abayanshi tare da ƙara rungumo shi ajikinta tana tofa masa addu'a,lamo yayi ajikinta yana faman sauke ajiyar zuciya,lokaci guda kuma numfashin ya daidaita kamar yarda yake ada,komai nashi yadawo normal,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,idonshi na arufe yake shaƙar ƙamshin turaren rishi ɗinsa,gaba ɗaya ya shiga yanayin da bai ta6a shigar irinsa ba,
Muryarta ce ta katse shi da cewa"junaid kana lafiya kuwa?naji ka tsit"?
   shiru yayi mata,saboda bayason tasan cewa ya dawo cikin hayyacinsa,baison ta raba jikinta da nashi,ɗumin jikinta ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,yaushe rabon da yaji ɗumin mace haka akusa dashi tun yana da kananun shekaru,tunda mommynshi tabarshi,Aunty azmee ta ɗaura da shayar dashi,shima ɗin da zarar ta kammala bashi nono ƴan uwanshi ke ɗauke shi daga wurinta,don basu son rabuwa dashi kona minti ɗaya,ya saba da jikin abban shi,dana ƴan uwanshi yayi missing wannan feeling ɗin,
   Jin yarda junaid ya lafe mata ajikinta kamar jinjiri,yasa tayi tunanin cewa kodai ya cika ne,cikin sauri takai hannu tare da ɗago da kanshi tana kallon fuskarshi,waro ido waje tayi ganin yarda yake ta faman sakin murmushin nan nashi,ranta ne ya bata cewa Dama duk plan ne ya tsara mata don ya tsoratar da ita,ɗaure fuska tayi tare da cewa"janaid wannan duk shirinka ne ko? don ka tsoratar dani,"
Buɗe idanunshi yayi a hankali yana kallon fuskarta data zuba mashi ido,tana mashi kallon Tuhuma,
  Murmushi ya kuma saki tare da cewa"dan Allah rishi ki mayar dani a jikinki na kwanta,ba kiji wani irin daɗi dana ji ba,daɗi kamar nayi bacci,"ya ƙarasa maganar yana lumshe mata ido,tsuke fuska sehrish tayi tare da cewa"amma ka rainamin wayau junaid!wai meyasa ka fiye shiririta ne,kalli fa, ka gani hada hawaye na soma zubarma saboda halin da na sameka aciki,ashe duk plan ne ko"?
   girgiza mata kai yayi tare da cewa"ba haka bane reesh,kona faɗa maki gaskiya ba zaki yarda ba,"
  A hankali ta kwantar mashi da kanshi ƙasa,sannan ta matsa tare da saita fuskarta akan tashi tana kallon shi,shima binta yayi da kallo yarda ta duƙo da fuskarta asaman tashi sumar kanta kuma tayi masu rumfa,tunda ta faɗo bedroom ɗin nashi tashigo da gudu don ta tarbe shi mayafinta ya sulale ƙasa daga jikinta,
   "Junaid waye uncle Abusufyan?naji abbanku na cewa zaizo nigeria,kodai shima ɗin yayanku ne"?
  girgiza mata kai yayi alamar a'a yace"uncle ɗinmu ne,ƙanin mahaifinmu dake zaune a ƙasar turkey"
   jinjina kanta ta ɗanyi kafin ta kuma cewa"bayan shi kuma naji Abbanku yana cewa,Mommynku zata zo itama,tare da wata goggonku ta katsina da kuma Ammi da Aunty azeema,duk zasu zo,"
   Sai da ya bari takai ƙarshen maganarta sannan ya ɗan harareta tare da cewa"Ashe dama jin gulma ne ya kawoki ɗakin"?
   Murmushi tayi tace"no ba haka bane junaid,inason nasansu ne saboda na koyi zama da kowannansu,bana so na samu matsala da kowa acikin family ɗinku,"
   "Zan faɗa maki halin kowannansu amma bisa sharaɗi ɗaya'?ya jefa mata tambaya,
  Tace"ina sauraronka wane sharaɗine wannan"?_
  murmushi ya saki tare da kai hannunshi ya nuna mata red lips ɗinsa yace"kiss on lips,if u agree then saina faɗa maki,"
   hannu tasa tare da ɗan buge bakinshi tace"pls junaid banason wasa fa,in zaka faɗamun ka faɗamun kawai,in ba haka ba zan tashi inyi tafiyata,"
  tayi maganar tare da yunƙurawa zata miƙe cikin sauri ya ruƙo hannunta tare da cewa"rishi mommyn mu bata da sauƙi,nima haka naji ana faɗa,amma in har zaki iya zama da babban yayanmu to wannan bazai maki wuya ba,bambancin ita mace ce kinsan ku mata da tsiwa kuke,
  Dariya tayi tana sauraronshi
"Uncle ɗinmu kuma Abusufyan,wayayyen mutun ne,idan yazo zakiji daɗin zama dashi,bafa wani babba bane autansu daddynmu ne,yana da sauƙin kai sosai amma idan mutun bai kwanta mashi araiba hmmmmm bazasu ta6a jituwa ba,Aunty azeema kuma kamar abbanmu take wurin faran faran da mutane ga son ƴa'ƴa,zakisha mamaki idan tazo ta ganki sosai zata jaki ajikinta,goggon katsina kuwa......"bai ƙarasa ba ya kama dariya,
  Murmushi ta saki tare da cewa"me tayi ita?ko batasan mutane"?
   Girgiza kai yayi tare da cewa"a'a tanason mutane sosai,matsalarta ɗaya tana da mental illness.......'
  Tunda junaid ya ambaci mental illness taji gabanta ya ɗan faɗi kaɗan kamar maison tuna wani abu acikin brain ɗinta,
  "tana da ban dariya sosai,tana fa iya ganinki tace ke ɗiyar wani ce acikin family ɗinmu kuma dole ki yarda da hakan in ba haka ba ta sanya rigima hada kuka ma,'
  Sai faman zuba junaid yake yi yana korama sehrish jawabi,ita kuwa tuni tayi nisa cikin tunaninta,kalmar da ya faɗi na cutar ta6in hankali ta tsaya mata arai,so take ta tuna waye ta ta6a sani da irin wannan lallurar amma sam tagaza tuna hakan,
  Ganin ta tafi duniyar tunani yasa junaid kai hannu ya janyo sumar kanta yana cewa"wai menene haka reeeshi,kin barni ina ta zuba kamar rediyon da bata da saiti,"
  Firgita ta ɗanyi tare da kallon shi har lokacin yana daga kwance tace"junaid thanks for the information,zan koma bedroom ɗina naji ana kiran sallar isha,kaima ka tashi kaje kayi sallar,'
   Ba musu ya amsa mata da cewa"bari nayi alwala sai mu fita atare,"
  Amsa mashi tayi da toh sannan ta miƙe tare da juyawa ta ɗauko mayafinta daya faɗi kasa ta rufe kanta dashi,toilet junaid ya shiga shaf shaf yayi alwala,bayan ya fito atare da ita suka saukko downstairs,
   Anan ya haɗu dasu Irfan zasu masallacin suma yabi bayansu suka tafi,
   Komawa bedroom ɗinta tayi kai tsaye ta fada toilet ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ƙarasa wurin wardrobe dinta tare da ɗaukar hijabinta da sallaya ta shimfiɗa tare da kabbara salla,anatse ta kammala sallar,fitowa tayi daga dakin nata sannan ta wuce kitchen don ta shirya ma kanta abincin da zata ci saboda yunwar data taso mata,

_💋Boss Bature💋_

A hankali Motarsu tashiga babban gate din gidan Abusufyan,major ne ke driving dinshi yayin da Omar ke hakimce a seat ɗin baya,sai faman zullumin haɗuwarshi da hossana yake saboda yasan cewa ba ƙaramin fushi take dashi ba,saboda ƙin zuwan da yayi,
Parking ɗin motar major yayi sannan ya fito tare da buɗe mashi motar,a hankali Omar yasa ƙafa tare da fitowa daga ciki,sannan cikin sauri batare da 6ata lokaci ba ya wuce cikin gidan,
Tunkan yasa ƙafarshi cikin parlourn nasu yajiyo shessheƙar kukan hossana,tsayawa ya ɗanyi yana sauraron abunda suke cewa,
   "Hossana wai ba zaki daina kukannan ba?salon ki 6ata kwalliyarki ko"?
  "Jahad ba zaki gane bane,bakisan yarda nake ji bane,saboda ya omar nayi kwalliyar nan,amma ta tashi a banza,yau ma bazaizo wurin mu ba...'cikin shessheƙar kuka ta ƙarasa maganar,
ƙayataccen murmushi Omar ya saki a fuskarshi,kafin yasa kai tare da shiga cikin palourn,samunsu yayi zaune asaman 3 seater,hossana ta kwantar da kanta asaman hannun sofa ɗin,yayin da jahad ke gefenta tana rarrashinta,gaba daya duk sunyi wanka sun canza kayan jikinsu,riga da skirt ne ajikin jahad,hossana kuma gown ce mai kyan gaske,
   jin alamar motsin mutum yasa jahad ɗagowa tana kallon shi,cike da mamaki ta buɗe baki zatayi mashi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login