Showing 93001 words to 96000 words out of 257722 words
Chapter 32 - Halysaah Book 2 By Khaleesat Haydar
kuma har abada babu wata alaƙa da zai sake hada ki da shi don ubansa har duniya ta nade kuwa, ba wai ban ji zafin alakar da kika yi creating da su a America bane a raina, fadin zafin da naji ma is just an understatement wallahi, amma considering the fact that you are my wife yasa nayi letting bygone to be bygone, so let me keep using that to calm my self kar in masu abinda ke raina...." Wani mugun tsanarsa ne ke karuwa a ran Khaleesat jin kalmomin da ke fitowa bakinsa, wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana tausayin kanta da irin monster din da Allah ya bata as miji, kokarin kwace kanta take yi a jikinsa zata sauka daga kan gadon yaki saketa yace "Ohk bokare min za kiyi don ina baki hakuri? But i said i am sorry, and i promise i won't hurt you again, na dena dukan ki...." Ƙin ce masa komai tayi tana kuka a hankali, ya kwantar da ita kirjinsa yana shafa gashinta a hankali yace "Billah ina son ki Khaleesat, duk abinda kika ga ina maki saboda ina son ki ne, but kin ki bani hakkina saboda ke akwai wani plan din a xuciyarki, probably ma su suka koya maki haka" Daga kai Khaleesat tayi ta kallesa tsabar bakin ciki bata san sanda tace "Ai ba kowa ne bashi da aikin yi kamar ka ba" Shiru yayi yana kallonta babu ko kiftawa, ita kanta shirun tayi gabanta na faduwa don bata san sanda kalman ya fito bakinta ba, Instead sai ji tayi yayi kasa da murya kamar me rada yace "Where is the Lubricant?" Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace, yana rungume da ita jikinsa ya bude bedside drawer kamar yasan nan din ta ajiye kuwa, ya laluba ya dauko, shesshekan kuka ta fara yi zuciyarta na bugawa, yayi kasa da murya yace "Kinsan tsinuwar Allah kike tara ma kanki kuwa?" Cikin kuka tace "To ai ba ni bace" Yace "To waye?" Muryarta na rawa tace "Wallahi ban sani ba" Cikin kwantar da murya yace "Promise me today will be different plss Baby" Ta kasa cewa komai hawaye masu zafi na sauka idonta ga faduwan da gabanta yake yi, gently ya fara cire kayan baccin jikinta yana kallon kwayar idonta cikin duhun dakin, a wannan dare Abdul bai yi bacci ba tsabar bacin rai, sai dai bai hantareta ba bai zageta ba, bai kuma doketa ba, haka ya mike ya fice kawai ya bar mata dakinta ya koma nasa, ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwan sanyi duk da mugun sanyin da ake a garin, bayan ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kunna karatun qur'ani a wayarsa ya kwanta amma ko rintsawa bai yi ba har asuba. Tunda Khaleesat ta idar da sallan asuba take zaune kan darduma bayan ta gama azkar dinta, gaba daya jikinta a sanyaye yake, zuwa yanxu kam sosai lamarin nan ya fara bata tsoro, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda abun ya tsaya mata a rai, kawai tayi deciding tayi amfani da abubuwan da Nenne ta kawo mata zuwa anjima, sai da gari ya waye sosai sannan ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin zuwa parlor, sosai gabanta ya fadi ganinsa zaune a parlon da cup din shayi a gabansa, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa ta tafi ta durkusa ɗan nesa da shi a hankali tace "Ina kwana" Maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Meye nake perceiving a cikin kitchen kamar maganin gargajiya?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, shi ma kallonta yake fuskarsa babu yabo babu fallasa, rasa me zata ce masa tayi tana wasa da fingers dinta, a fusace yace "Bakya ji na ne?" Bakinta na rawa da kyar tace "Nenne ce ta kawo min" A takaice yace "Na menene?" Ta sauke idonta tace "Magani ne kawai, dama ta saba bani in dinga amfani da shi a gida" Mikewa yayi yace "Mu je ki bani su" Ta shi tayi kamar munafuka ta nufi kitchen din ya bi bayanta, ita kanta taji kamshin itatuwan da ta shiga kitchen din, ta bude inda ta ajiyesu ta dauko, ya mika hannu, ta karasa ta basa, yace "Ba a min amfani da irin wa ennan abubuwan a gida" Kai kawai ta gyada masa, fuska daure yace "Kin ji me nace maki? Kar ki sake amsa idan ta baki" A hankali tace "Na ji" Juyawa yayi ya fice daga kitchen din ya koma parlor ya zauna, ya ajiyesu nan kasan tiles, tana fitowa daga kitchen yace "Get ready za mu fita, kuma kar ki bata min lokaci" Cikin sanyin murya tace "Toh" Dakinta ta tafi, bayan kusan minti talatin sai ga ta ta fito cikin shiri, dai dai nan shi ma ya fito daga dakinsa rike da wayarsa da car key, yana gaba tana biye da shi suka shigo parlor, ya dau ledan magungunan da Nenne ta kawo mata ya nufi kofar fita daga parlon ita dai tana biye da shi a baya, a booth dinsa ya saka ledan magungunan, sannan ya zaga zuwa driver seat, ita ma ta shiga front seat, bayan ya gama warming motar ya fita daga gidan. A sanyaye Khaleesat ta fito daga Office din Dr Mariya with different thoughts running her mind, ta ɗan juya ta kalli Abdul da ke bayanta shi ma ya fito office din likitan, ƙin kallonta yayi, hakan ya sa ta ci gaba da tafiyarta slowly, sai ga Dr Mariya ita ma ta fito daga Office din zata masu rakiya zuwa parking space, hira suke yi kawai da Abdul suna tafiya a tare, ita dai Khaleesat na can gabansu, har dai suka fita daga reception din hospital din suka karasa parking space, Dr Mariya na kallonta tana murmushi tace "To amarya plss inji labari opposite of this kin ji? There is nothing wrong with you, In kinyi amfani da duk shawararin da na baki komai zai tafi dai dai in sha Allahu, hakuri kawai za ki yi it's always like that dama, Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya, in dai na samu lokaci zan zo har gida mu gaisa" a hankali Khaleesat tace "To Nagode Aunty, Allah ya kawo ki lafiya" Dr Mariya na murmushi tace "Ameen" Sai kuma ta kalli Abdul tace "To Barrister ku gaida gida, ina kuma tabbatar maka in sha Allah matsalar ta zo karshe tunda kaga mun dade ina magana da ita, kuma hopefully ta dau duk abinda nace mata" Yace "Thanks for your time Dr" Zagawa yayi ya shiga driver seat, Khaleesat kuma ta shiga front seat, ya tada motar suka bar hospital din, har suka yi nisa bai ce mata komai ba, ita ma dae shiru tayi tana ta tunane tunane, sae da taga unguwan da suka shigo tayi realizing gidansu ya kawosu, bayan yayi parking ya sauka motar, ita ma ta sauka, booth ya tafi ya bude ya ciro ledan da Nenne ta kawo mata, da mamaki tana kallonsa tace "Ina zaka kai wannan?" A takaice yace "Momy zan kai ma, naga tana dealing da irin abubuwan nan, she can use it if she want, ke dai baza kiyi amfani da su ba a gidana" Khaleesat ta marairaice masa tace "Noo pls, ni dai gwara kayi disposing dinsu don Allah" Fuska daure yace "Bazan yi disposing din su ba" Bata san dama haushinta ne fal zuciyarsa ba bayan Dr Mariya ta dubata ta tabbatar masa lafiyarta qlau babu wani abu da yake hindering passage dinsa, everything is normal, kawai hadin kai taki basa, Khaleesat ta sunkuyar da kai a sanyaye bata sake cewa komai ba, ya nufi entrance din gidan nasu, tana tafiya a hankali ta bi bayansa har suka shiga parlorn gidan, da mamaki Momy ke kallonsu tace "A'a, daga ina ku ke da safen nan, sannun ku da zuwa" Abdul ya zauna ya gaisheta, ta amsa tana kallon Khaleesat da ta zauna kasan carpet tana gaisheta, Momy ta amsa da fara'a sosai fuskarta tana welcoming dinta, Momy na kallon Abdul tace "Amma ba daga gida ku ke ba ko" Yace "Eh, daga asibiti mu ke" Da mamaki Momy tace "Asibiti kuma, waye ba lafiya?" A takaice yace "Bata ji dadi bane, amma da sauki" Momy na kallon Khaleesat tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, sannu Mamana, Allah ya kara lafiya" Sai kuma ta kalli Abdul tace "Ko wajen Dr Mariya ku ka je?" Yace "Eh" Mikewa yayi ya ajiye mata ledan magungunan kusa da ita yace "Kakarta ce ta kawo mata wnn jiya, ni kuma kin san bana son irin abubuwan nan na gargajiya shi ne na kawo ko zaki yi amfani da su ke" Momy tayi kuri da ido tana kallon ledan da mamaki, sai kuma ta dauka ta bude da sauri, lkci daya ta saita kanta tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, ai kam nasan halin ka baka san itatuwa, zan ko yi amfani da su dama nawa sun kare tas" Ita dai Khaleesat kasa dago kanta tayi, Momy was shock har cikin ranta amma tayi karfin hali take wayancewa, can ta kalli Khaleesat tace "Amma baki fara amfani da su ba ko" Khaleesat ta girgiza kai ba tare da ta kalli Momy ba tace "A'a jiya ta kawo min banyi amfani da komai ba" Momy tace "To to, hakan yayi" Ta kalli Abdul tace "In dai an samu wasu a dinga kawo min kawai" Mikewa yayi yace "Za mu koma Momy" Momy tace "Da wuri haka? To wai ka koma aiki ne?" Yace "Ban koma ba tukun" Momy tace "Toh shikenan, Allah ya tsare nima in sha Allahu ina nan shigowa in kawo mata turarrukan wuta da na jiki" Shi dai bai ce komai ba ya nufi kofa, Khaleesat ta mike tana yi ma Momy sallama, Momy duk fa a rude take ta gyada mata kai kamar kadangariya tace "To Mamata, sai na shigo, ku gaida gida, maza bi sa ku tafi" Daga haka Khaleesat ta bi bayan Abdul da har ya fita daga parlon, Momy ta dau wayarta har tana tuntube ta shiga dakin dake downstairs ta fara kiran Dr Mariya don family Dr dinsu ce for long, Dr Mariya na dagawa suka gaisa da Momy cikin fara'a, Momy tace "Yanxu Abdul ya zo min da matarsa yace daga asibiti suke, naga duk ba shi da walwala nasan yana da zurfin ciki bazai gaya min ko menene ba, shi ne na kira inji lafiya dai ko Dr? Ko juna biyu gareta? kinsan dama yace bai son haihuwa da wuri, in dai juna biyu ne da ita gwara in yi dubara in dawo da ita wajena don ni dai ina son ganin jikana, kar yaje ya bata wani abu da zai lalata cikin taje ta sha" Dr Mariya tayi dariya sosai, bata boye ma Momy komai ba tayi mata bayanin dalilin zuwansu Asibiti, Momy ta sauke wani irin ajiyar zuciya ba tare da tasan tayi hakan ba, sai kuma ta bige da cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kinsan yarinya ce fa, duka duka Allah yasa tayi shekara ashirin, har da yarinta abun nata dae" Dr Mariya tace "Wallahi nima haka nace masa don dae in kwantar masa da hankali kar ya dinga jin haushinta, amma shekara ashirin ai ba yarinya bace Hajiya, aka ma er shekara sha biyar aure ta zauna balle er shekara ashirin, ni dai na bata shawarwari Allah ya sa tayi amfani da shi, kar tun yana hakuri da ita hakurinsa ya kare a fara samun matsala gaskiya" Murmushi kawai Momy take tana Allah Allah su gama waya da Mariya ta kira Godiya, daga karshe Momy tace "To Allah ya sa ta dau shawaran naki Dr, kuma zan yi ma yayarsa magana ita ma taje gidan anjima ta kara nutsar da ita in sha Allahu" A haka Momy suka yi sallama da likitan, Momy tayi wani dariya tana girgiza kai sannan ta fara dialing number Godiya, aikin miliyan biyu ai ba wasa bane, sun dade suna waya da Godiya a waya, daga bisanni suka yi sallama, Momy na ta murmushi ita kadai bayan Godiya ta sake jadadda mata Malamin yace lokacin ma da ya dibar masu za ayi sakin baza a kai haka ba, don gab ake da yin sakin cikin kwanan nan kuwa, Meemah da ta shigo dakin ta tarar Momy na waya ta zauna duk tana sauraron conversation dinsu har suka yi sallama tace "To shikenan Momy yanxu haka zai saketa ba mu ci ubanta ba na huce haushin abinda yayi min a kanta?" Momy tace "Ke wa ke ta wani cin ubanta? Ance maki shi ne a gabana sai kace wata yarinya? Ni dai in na samu Abdul ya rabu da ita an gama min komai, kuma hakan kadai ne a gabana yanxu ba shashanci irin naki ba, ke kinsan menene hada iri da talaka kuwa? Ke kiji matsiyaciyar kakarta har ta fara shige shigen malamai tana kawo mata asiri banda Allah yasa Abdul din ya gani, to karyarsu ta sha karya wallahi, cikin kwanan nan zai kora masu ita bayan ya saketa" Mikewa Meemah tayi ta fita daga dakin don kwata kwata ba haka ta so ba ita, so kawai tayi a bar ta tayi ma Khaleesat dukan mutuwa ko zata jin sanyin abinda Abdul yayi mata a kanta.
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500*
We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c.....
All at affordable prices
Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested....
Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM
HALYSAAH 50
Bayan Khaleesat sun koma gida tayi wanka sannan ta canza kaya tayi sallan azahar ta fito ta dora lunch a kitchen, tana ta zaune parlor bayan ta gama hada komai na girkin tayi tagumi tayi nisa tunanin da take bata san sanda ya fito daga dakinsa ba, ya karaso parlon yana kallonta yace "Burden din mutane nawa ne a kanki da kike tagumi haka" Juyawa tayi ta kallesa tana gyara zamanta amma bata ce masa komai ba, tunda suka dawo gidan sai yanxu yake mata magana bayan ya gama cika da batsewan sa kenan, Yace "I am asking you" Shiru tayi still bata ce komai ba, ya zauna kan kujeran dake facing dinta yace "Mutane nawa kike ciyarwa da kike tunanin yanda za ki yi?" Bata san sanda tayi murmushi ba tana wasa da fingers dinta, kamar bazata ce komai ba, sai dai a hankali tace "Ba ina son zan yi magana da frnd dita Sophie ba kace bazan yi ba" Yana kallonta yace "Kiyi magana da ita ki ce mata me?" A hankali tace "Babu komai, i am just missing her kawai" Wayarsa dake hannunsa ya cire ma lock sannan ya mika mata yace "Speak to her in my front" Amsan wayar tayi ta shiga contact dinsa ta duba number Safiyyah sannan tayi dialing, yana kallonta yace "Sa a handsfree" Ba musu Khaleesat ta saka kiran a Handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga, a hankali Khaleesat tace "Sophie" Safiyyah tace "Omg Khaleesat? Wallahi I've been expecting your call for so long kawata amma shiruu, Ya Allah, number Abdul din ne wannan?" Khaleesat ta ɗan kalli Abdul da ya kafeta da ido tace "Um, nasa ne" Lkci daya har Safiyyah ta gane wayar a handsfree yake sanin wanene Abdul, a hankali tace "Ohk then, ki gaida min shi sosai pls, but can i come over in gan ki if he will permit that pls?" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I will speak to him about it" Safiyyah tace "Alright dear, take care of ur self, i will be waiting for ur feedback" Khaleesat tace "In sha Allah" a haka suka yi sallama, safiyyah ta kalli wata aunt dinta dake kusa da ita cike da bakin ciki tace "Wallahi nasan yana gefenta shi yasa ban tofa nawa ba, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Her marriage and Abdul is the worst thing that have happened to me last year, yanxu shikenan ta zama matarsa duk guje mata hakan da na dinga yi, ba irin addu'an da ban sa ta akan Allah ya rabata da Abdul ba, nayi ta mata sha'awan Housemate dinta amma Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta, dubi yanda take min magana kina jin muryarta kinsan tana cikin damuwa da matsin rayuwa, gashi karshen watan nan za mu koma school ban kuma ga alamar zai bar ta taci gaba ba" Safiyyah ta fara matsar kwallan bakin ciki, ita dai tana jin babu wanda ya kai ta bakin ciki da auren Khaleesat da Abdul, Abdul ya amshi wayarsa da Khaleesat ke mika masa bayan tayi sallama da Sophie, a hankali tace "Thank you" ajiye wayar yayi yace "Sai hankalin ki ya kwanta yanxu tunda kin yi magana da kanwar Baabarki ko" Cikin sanyin murya tace "Plss ina neman favour din ka barta ta zo wajena don Allah, i am missing her so much" A takaice yace "Baza ta zo ba, in barta ta zo ta ji dadin zuga ki kamar yanda ta saba? you think i don't know saboda tasan wayar a Handsfree yake shi yasa tayi composing words dinta without saying anything silly yanxu, duk ba ita bace ta fara ruining tunanin ki, very stupid girl" Khaleesat dai kallonsa kawai take hawaye cike idon ta, kawai tayi deciding tayi masa maganar abinda ya tsaya mata a rai all this while, hoping Allah zai sa yayi considering din request din nata, cike da karfin hali tace "Amma don Allah Yaya Abdul kar kace bazan koma makaranta ba, we are resuming end of this month kuma kasan wannan shekaran kadai ya rage min plss kar ka bari inyi asaran shekarun da nayi a baya, kayi considering expenses din karatun plss, in kuma zai yiwu kawai a