Showing 219001 words to 222000 words out of 257722 words
Chapter 74 - Halysaah Book 2 By Khaleesat Haydar
seconds yace "Or is there anything you want to tell me but you are not telling me?" Ajay yace "Kamar me kenan? Why did you say so?" Jay yace "Naga kamar har yanxu kai baka yi na'am da batun nan dari bisa dari ba, You are just being neutral about it" Ajay yayi dariya yace "I don't get you Bruh, idan akwai wani abu ance maka bazan gaya maka bane?" Jay bai sake cewa komai ba ya bude motar ya sauka yace "Bazan dade ba in sha Allah" Ajay yace "Kana wuce minti goma i promise you I am leaving" Jay yace "Ai ba motar ka bace Malam" Bai jira cewarsa ba ya nufi cikin gidan, Ajay ya jinginar da kansa jikin kujeran motar maganganun Mami suna kara dawo masa a kai kamar a lokacin take gaya masa su, rufe ido yayi trying to erase the thought of his mind. Duk da ɓacin ran da Nenne ke ciki mara misaltuwa tana ganin Jay ta watsake lokaci daya ta dinga masa sannu da zuwa cikin fara'a, ta dauko masa rabin ledan pure water ta dire masa a gabansa baki har kunne tace "Ai ni bata ce min kana hanya ba da na bada kudi an amso maka lemon kwalba da ruwan gora nayi maka tuwo da miyar taushe, sai dai kawai matsalar unguwan nan masu kantin barayi ne, komai nasu tsada kamar yan fashi" Shi dai Jay murmushi kawai yake, Umma ta fito suka gaisa da Jay cikin fara'a sannan ta bar parlon, Nenne tace "Amma kuma kace mata zaka zo shi ne ta kama hanya ta tafi Hotoro da kanwar uwar, wai sun je wajen wata wai ita Gaje" Jay na murmushi ya girgiza mata kai yace "A'a ba mu yi waya da ita ba yau, bata san zan zo ba" Nenne tace "To bari in je in sa uwar ta kira mana ita" Jay yace "Zan kirata da kaina Kaka" Nenne tace "To hakan ma ba laifi, sai dai ka zo ina cikin wani bakin ciki wanda rabon da in shiga irinsa har na manta wallahi" Jay yace "Subhanallahi, me ya faru Kaka?" Nenne ta gyara zama rai bace tace "Rimi rimi muka kamo hanya tsakar dare muka dawo gidan nan don bama son kowa yasan inda muka koma saboda tsaro da gudun surutun mutane, amma maganar da nake maka yanxu ɗaiɗai kun 'yan Mariri ne basu zo ganin gidan ba wai sun zo mana Allah ya sanya alkhairi, gaba daya labari ya baza Mariri an san gidan da muka dawo, to duk ba wannan ba, kasan ba mu dawo da matan Malam Ali gidan nan ba, kai dai kaga irinsu kaga yanda suke rayuwa, yanxu fisabililahi ina wajen da za a ajiye su a gidan nan? shi ne uwar Khaleesat ta munafurce ni ta zaga suna ta kulle kullen yanda kishiyoyin nata za su dawo gidan nan mu gwamutsu...." Jay ya ɗan yi murmushi yace "Kiyi hakuri Kaka, baza a biye ta halinsu ba ai" Nenne tace "Ba halinsu nake gudu ba ɗan nan, wallahi rubar da gidan za su yi ya koma dena ba kowa sha'awa, in don ta mugun halinsu ne ni ina ruwana, babban damuwata kar a dena sha'awar gidan nan gaba, sai kaga yanda ake turuwan zuwa ganin gidan nan wallahi, har da yan unguwan, to aka dawo da su Zubaida ai zance ya lalace kuma" Jay na murmushi yace "Ki dai yi hakuri Kaka, gida in ana gyaransa babu abinda zai yi in sha Allah" Nenne tayi shiru bakin ciki kamar ya kar ta, nan Jay ya dinga lallabata yana bata baki akan ta bar su su dawo kawai ko don Baban Khaleesat, bayan kusan minti goma ta sauke wani bala'e'en ajiyar zuciya tace "Shikenan ɗan nan, ai ka wuce ka ban shawara in ki dauka, kuma babban banza ne baya daukan shawara, zan samu Zahra'un ta kira min Malam Alin mu yi magana ta waya" yana murmushi yace "Maa sha Allah Kaka" Tayi shiru a ranta tana cewa "Zubaida me 'ya ya rakacaaa dama sai dai ta zauna tsakar gida, kawai ita ta hakura ta bar masu wannan ginin da take cewa nata ne su karata can, parlor daya da kitchen daya da daki da banɗaki ya ishi ita da 'ya yanta rayuwa, ita kuma Shatu a samu dakin kusa da kitchen a hadata da shi ita ma ta karata da kananun yaranta, su kuma yan matan gidan a basu daki daya su karata su ma, Aunty Farida sai tayi hakuri su zauna tare da Khaleesah kawai tunda haka Allah ya kaddaro masu, ta sauke wani ajiyar zuciya a fili tace "Toh ya iyayen naka?" Jay yace "Duk suna lafiya Alhamdulillah" Ta mike tace "Bari in duba ko da sauran shinkafar in zubo maka, dama Khaleesah ce ta dafa" Bata jira cewarsa ba ta wuce kitchen da sauri. Tunda Khaleesat da Aunty Farida suka sauka daga cikin adaidaita sahu take kallon motar da aka yi parking kofar gidan with the front seat slightly open kuma an kwantar da seat din motar, lokaci daya kawai tasan Ajay ne a motar for some reasons, ta kalli Aunty Farida tace "Kamar Ya Junaid" Aunty Farida tace "Haba" Khaleesat ta karasa har front seat din ta leka cikin motar tana kallonsa, taga idonsa a lumshe, a hankali ta kai hannu zata dau wayar sa dake ajiye lokaci daya ya bude ido, Mikewa zaune yayi da sauri yana komawa baya ta kyalkyale da dariya ta daga nikab din fuskarta don da alama Nikab din ne ya firgitasa cause he was sleeping, sosai ya bata dariya ba kadan ba ganin da gaske ya ji tsoro, shi ko ya hade rai yana kallonta, tace "To guduwa zaka yi da?" Aunty Farida ta karaso gun motar, ya gyara zama suka gaisa tace "To me yasa baka shigo ciki ba Junaid" Ya ɗan shafa kansa yace "Ina ɗan waya ne, amma Jawwad yana ciki" Khaleesat ta ɗan bude ido jin abinda yace, sau uku tana kiran Housemate din nata yau yaki picking call dinta, wanda hakan yasa tun daxu bata da wani walwala sai yanxu ne ma tayi dariya tunda gari ya waye, Aunty Farida tace "To mu shiga tun da ka gama wayar" Ya sauke idonsa bai ce komai ba, Aunty Farida ta nufi cikin gidan, Khaleesat na tsaye har ya sauko daga cikin motar, ya kara hade rai yace "Wai ke mayya ce ne, Kiyi tafiyarki mana" Ta ɗan yi murmushi kawai tace "Ai ko mayyar ce i will finish you first before anybody" Tana fadin haka ta nufi gate kafin ma ya bata amsa, kulle motar yayi ya ɗan tsaya for some seconds before walking toward the gate too. Khaleesat na shiga parlor Jay dake zaune ya daga kai ya kalleta, suna hada ido ta hade rai ta dauke idonta ta karaso cikin parlon ta zauna kasan carpet, Nenne na kallonta tace "Kun samu Gajen ta ku?" Khaleesat tace "Eh" Nenne ta kalli Jay tace "To bari in shiga wajen Zahra'u in yi yanda kace ayi, ai tunda kace inyi hakuri an gama magana kawai" Ya ɗan yi murmushi yace "To Nagode Kaka" Mikewa tayi ta bar parlon, Sai a sannan Khaleesat ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba tana wasa da Hijab din jikinta, shi dai kallonta kawai yake babu ko kiftawa, can ya ɗan yi murmushi don yasan fushin me take, sai kuma yayi kasa da murya yace "Should I take my leave?" Sai a sannan ta daga idanuwanta ta kallesa, kamar zata yi kuka tace "Mene yasa baka son yi ma mutum uzuri?" Kamar bazai ce komai ba, sai kuma yace "Uzurin me za a maki Halysaah?" Tace "Da ka kirani jiya ban daga ba ai wayar baya wajena ne Aunty Farida ce tayi waya da shi" Yana kallonta yace "Why didn't u explain to me on Whatsapp yesterday? Instead you only asked weda I didn't see ur call and that's all" Shiru tayi bata ce komai ba, yayi murmushi yayi kasa da murya yace "You know one thing about you Halysaah?" Ta daga idanuwanta tana kallon sa, still smiling yace "Idan kika yi wani action that needs explanation, ignoring explanation din kike kiyi acting as though nothing happened, I called you 4 times yesterday and ur line was busy, da kika min magana ta WhatsApp sai ki bada uxurin ki amma sai kika yi ignoring din hakan" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "To kayi hakuri" Shi dai murmushi kawai yake yana kallonta yace "In ban yi hakuri ba ai bazan zo yau ba Halysaah" Ta langwabe kai tana kallonsa, yace "Kun ga Ajay a waje ne?" Ta ɗan bude ido sai kuma ta mike tace "Ina zuwa" Da ido ya bi ta har ta fita daga parlon, a compound din gidan taga Ajay zaune ta tafi har inda yake, ita har ta manta ma da shi, tana kallonsa tace "Baza ka shigo ba ne" juyawa yayi, yayi backing dinta yana kallon different direction yaki tanka ta, dariya ma ya bata, ta taɓe baki ta juya ta koma cikin gidan kawai, ta zauna tana kallon Jay tace "He is sitting outside, kilan bazai shigo ba" Jay yace "Ohk, i think I will take my leave now, dama Abuja za mu tafi gobe so we decided to spend the night in Kano Today" a hankali Khaleesat tace "Ohk, to ko inyi girki sai anjima ka zo ka amsa? May be after magrib" Jay yace "A'a kar ki ba kanki wahala Halysaah, we will get food at a restaurant" Khaleesat ta kalli wayarta dake vibrate alamar shigowar kira sai kuma tayi silencing call din don bata da number dake kiran nata, Jay yace "Wa yake kiran ki"
*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* ur evidence 07087865788
HALYSAAH 90
Khaleesat ta kallesa ta langwabar da kai tace "I don't have the number, ban san waye ba...." Jay yace "Let me see it" Daukar wayar tayi ta mika masa ya amsa yana kallon screen din, after some seconds ya mayar mata da wayar ta karba tace "Kilan 'yan can unguwan mu Mariri ne, daxu ma wata ta kirani za su zo nan wai Aunty Sha'awa ta bata number na" Jay yace "Ohk, but ya kamata a samu Gate Man for security" Khaleesat tayi murmushi kamar zata ce masa ai Nenne ce ke ajiye kujera ta zauna baƙin gate din tun sassafe amma kawai ta fasa, Jay ya shafa kansa yace "I will take my leave now Halysaah, ki ce ma su Kaka na tafi...." Khaleesat tace "Za ku yi celebrating birthday din Ya Junaid ne? Ko ba ya celebrating?" Jay ya ɗan kalleta yace "Ai ban san ko yace maki yana Celebrating ba" Khaleesat tayi dariya tace "A'a ni ban ma yi wishing dinsa Happy Birthday din ba ai, ko nayi bazai kulani ba ma nasani, kai yaushe ne naka Birthday din?" calmly yace "Rana daya da na Halysaah" Tayi murmushi tace "Uhmm... ai shikenan tunda baza ka gaya min ba" Shi ma murmushin yayi yace "Lokaci na wucewa bari in tafi" Tayi kasa da murya tace "Kasan me?" Yana kallonta yace "A'a sai kin fada" Tace "Promise me you will listen to me" Shiru yayi yana kallonta, can yace "To me zai hana Halysaah?" Tace "A'a ni dai kayi alkawarin zaka zauna kaji duk abinda zan ce har karshe" Cikin few seconds ya fara nazarin meye zata fada masa haka amma ya kasa ganowa, Yana kallonta with much interest yace "Ina jin ki Halysaah, meye kike tunanin zaki gaya min da bazan tsaya in saurare ki ba?" Sauke idonta tayi a hankali tace "I just want to solemnly appreciate you for everything you've done to me and my parent so far, I know words will never be enough to express all my gratitude... Words will definitely fail me but I believe you are a God sent angel to I and my family and I appreciate the very day I met you in my life...." Tun da ta fara yake wani kallonta, cikin sanyin murya tace "And I also want to appreciate Ya Junaid too, duk da nasan he won't give me a listening ear, Amma Nagode da duk abubuwan da yayi min shi ma, Allah ya saka masa da alkhairi..." Mikewa Jay yayi, Khaleesat ta kallesa ta hade rai tace "You promise to listen till the end fa" Ya ɗan yi murmushi yace "You are wasting my time Halysaah, ta shi ki rakani, keep ur words for another day" Ta ɓata fuska ta mike tana kallonsa, A hankali yace "To yi hakuri, za mu ci gaba ta waya" Ita dai tayi shiru bata ce komai, ya fara tafiya yace "Ko in tafi baza ki rakani ba" Tana tafiya a hankali ta bi bayansa, suna isowa gate ta zaro ido tace "Nayi mantuwa, i am coming plss" Daga haka ta juya da sauri ta koma cikin gidan, shi dai ya fita daga gate din ya karasa gun motarsu ya samu Ajay zaune yana jiransa a gaban motar, front seat din ya bude Ajay ya hade rai yace "Thanks for wasting my time" Jay ya ciro wayarsa a aljihu jin ana kiransa, yana dubawa yaga Mami ce, daxu ma ta kirasa bai samu ya daga ba, komawa bayan motar yayi ya jingina jiki yayi picking call dinta ya kai wayar kunne, Khaleesat ta fito daga gate din gidan ta nufi gun motar ganin Ajay kadai zaune a front seat ta fara dube duben inda zata ga Jay, can ta hangosa tsaye yana waya, kallon Ajay tayi taga far end of the street yake kallo kamar ma bai san tana tsaye wajen ba, abinda ke hannunta ta ajiye masa a gefensa tace "I got you this for ur Birthday, Allah ya karo shekaru masu albarka" Ya kalli package din da ta ajiye masa, sai ga Nenne ta fito daga cikin gida da sauri tana gyara yafin gyalenta, karasowa gun motar tayi cikin hanzari tana cewa "Na fito parlor naga wayam ba kowa, nace kaddai tafiya kayi yarinyar nan bata sanar mana ba, ga Parida can ta ɗora maka koren shinkafar nan da ake yi da hanta da karas, don Allah ka tsaya ka ci abinci tukun ko kuma a juye maka a Cooler ka tafi da shi" Tana ganin Ajay ta saki baki tana kallonsa, sauke kansa yayi ya sauko daga motar ya gaisheta kansa a kasa, a hankali tace "Lafiya lau ɗan nan, ashe dama tare ku ke, me ya hanaka shigowa, ko da yake naga baka da sakewa kai kamar sa, kowa da irin halittarsa dama, Malam Ali ma haka yake bai sakewa in bai saba da mutane ba" Shi dai sai murmushi yake wanda iyakarsa lips, sai ga Jay ya zagayo don saboda muryar Nenne ne ma yasa yayi ma Mami sallama har ta fara tambayarsa muryar wace tsohuwa ce take ji haka, Nenne tace "Wallahi bata ce mana zaka tafi ba Ahamad, ga kuma girki can ana maku kai da ɗan uwanka" Khaleesat ta hade rai tana kallon Nenne, can ta daga ma Jay hannu shi dai ya bi ta da ido har ta wuce cikin gidan, duk tunaninsa da ta ce masa tana zuwa kiran Nennen taje yi, sai da Nenne ta ɓata masu kusan minti goma tsaye a wajen tana zuba sannan daga karshe suka samu suka bar unguwan tana daga masu hannu... Lokaci Lokaci Ajay ke kallon abinda Khaleesat ta ajiye masa har suka isa gida, Jay ko kula da package din bai yi ba, sai bayan da yayi parking ya kashe motar yayi ido hudu da package din ya dauka yana kallo yace "Where did you get this Ajay?" Ajay dai kallonsa yake, kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Oho yanda ka gansa nima haka na gansa a wajen" Jay ya wani kallesa ganin raina masa hankali zai yi, bude package din that is wrapped neatly and beautifully ya fara yi, har sai da ya bude gaba daya, Ajay dai sai kallon Box din hannun Jay yake, Jay ya bude box din ya ci karo da designer perfumes biyu wanda kudinsu zai yi 200k each ko ya kusa, making almost 400k kenan, ya kalli Ajay da shima kallon turarurrukan yake, Jay ya ciro wrist watch shi ma me shegen tsada dake cikin box din, iya abinda ke cikin package din kenan sai Birthday card from a friend, ya kalli Ajay yace "Tell me how you got this? Ko dai Paul ne ya ajiye a motar daxu kafin mu fita?" Ajay ya bude hannu alamar shi ma bai sani ba, Paul worker din gidansu ne na nan kano, shi ke kula da gidan ko akwai mutane ko babu, sosai suke jin dadin mu'amala da Paul, shi ma kuma haka yake ji da su saboda kyautatawar da suke masa, ya kuma rike amana sosai ba kadan ba, Jay let out a grin yana jujjuya Birthday card din hannunsa yace "But you are his boss not his friend...." Sai kuma yayi murmushi yace "This is soo thoughtful of Paul, few months back ba ka basa kudi masu yawa ba, yana da hankali sosai ai" Gently Jay ya bude turarurrukan duk ya fesa daya bayan daya to perceive the scent, ya lumshe ido don kamshin sun tafi da shi, yace "This is waow" Lokaci daya kamshi ya cika motar gaba daya, Shi dai Ajay bai ce komai ba ya bude motar ya sauka, Jay ya maida duk gifts din cikin box sannan ya fito daga motar yana rike da su ya kulle motar, suka nufi cikin gidan.... Karfe tara saura Ajay ya dau laptop dinsa da waya zai wuce daki yana kallon Jay da Cousin Bro dinsu Mukhtar yace "Good night" Sannan ya wuce dakinsa, kulle dakin yayi da makulli ya ajiye laptop dinsa ya zauna gefen gado yayi dialing number Khaleesat, Khaleesat na zaune tare da Nenne a dakin da Nenne ta zabar ma kanta a gidan, Islam ta shigo da wayar Khaleesat a hannunta ta mika mata tace "Aunty ana kiran ki" Amsan wayar tayi tana duba me kiranta