Showing 42001 words to 45000 words out of 269010 words
da ya tankasu ba.
Can waje ya samu yan uwanshi su yaya Nura yana basu labarin rashin mutuncinn da ya samu mijin nawakeyi don haka ya hade kan su akan suyi wa baba tawaye ga zancen.
Don gulma baba har ya fita kasuwa sai inna ta tura yaro ya kirashi a kasuwan don tasan bazasu ji komai a wurin yaya Sani din ba.
Tun shiga na dakin ummi kuka nake yi ban iya magana ba har da ruwa da kunun da ta aje mun ban iya shan ko daya ba a ciki.
Kanina ta tura ya kira mata gwagonta da sauri a gidan su don tasan ba lafiya ba wanan zuwan nawa kan.
Ta fita ta kira su mama da inna kafin gwago din ta zo nan suka sakani gaba da tambaya amma basu samu amsa komai ba ban da aukin kuka da nakeyi.
Gwago ta taso hankali a tashe tazo gidan namu cikin tashin hankali da son ganina kamar karta shigo na kara sautin kuka na ina fadin ban komawa wallahi gwago kasheni zai yi kinga duka,
Na shiga bude jikina ina nuna mashu ga tabo nan ko ina a jikin nawa ba iya ka take ummina ta fashe da kuka inna ne kawai batai kuka a wurin .
Sai ga baba da yaron da ya tafi kiranshi sun dawo tun a kofan yake fadin ina Safiyan take ne lafiya ko tare suke da mijin nata
Nan take gidan yai tsi kowa na sauraren abinda zai fito bakin na amma sai kara sautin kuka na da nakeyi kawai.
Tsawa ya dakamin tare da tambaya na dacewa ke ki ba mutane amsa kin tsaya sai kuka kike zubawa mutane, kukan ne zai fishe ki.
Daga kofa suka tsinkayo muryan yaya Nura da yaya sani suna cewa baba mijin nan ta dan iska ne wallahi da ce anan arewa yake zaune ba abinda zai hana mu casa shi wallahi.
Baba ya daka may tsawa da kai rufe muna baki don Allah yanzun dai may ya kawo nan a wani dalili tazo .
Yaya Sani ya karbe zance cikin dakewa yace a dalili na tazo don ni naje har lagos na dauko ta na zo da ita gida kar ya kashe ta ga banza kar mara galihu da gata .
Wani kallo baba yake mashi ya ci gaba da cewa diba baba ka gani yadda duka ya mayar da yariyan ga duk ta koma kamar wata ta baba wallahi.
Baba ya daka mai tsawa da kai dakata kaina ubanta ko kaine uwar ta ya girgiza kai alaman a a baba yace to kada hurumin dauko ta ka dawo gida ita .
Baba ta yaya zanje na samu yana dukanta da zagi akan taki dafa masu abinci shida karuwan shi ya doke ta yana zagi na fitan arziki.
Ina ruwan ka baba ya firfito da indo waje ya sake cewa nace ina na ruwan ka wa ya aike ka zuwa dauko ta idan ya ga dama ya kashe ta mana ai mijinta ne kuma dan uwantw.
Gwagon Ummi tace a a malam wanan ba hujja bane gaskiya kace fa ya kashe idan yaga dama da yar uwar shi ce aiba zai mata wanan tsinanen duka haka ba.
Baba yace cikin daure fuskan karki saka bakinki ga zancen nan don ba maganan ki bace diya dai diyatace kuma dan yar uwana na bawa ita.
Don haka ko yanka ta yake yi gunduwa gunduwa sai ta koma gidan nan shidin da yaje ya dauko ta shi zai mai da ita dakin ta ta zauna ai kowa hakkuri yake a dakin shi.
Mama tace bako da duka ba har da su tarmashe da sauran su sai dai wani abin kadai tsaya ai bincike kada a dauki yarinya a mayar wani abu yaje ya samay ta ta halaka fa.
Baba ya amshe zancen nata da cewa idan ta halaka aure ya halaka ta nace aure ya halakata sai ummi na ta fashe da kukan bakin ciki yace sai kiyi amma komawa sai ta koma wanan gidan ba fashi .
Ya juya ya fice gidan da banbami shiko yaya sani fadi yake yi ba inda zan tafi wallahi abar shi yaje ya kashe ta din ba shike nan ba ai yar shi ne yace.
Wanan kalamai na yaya sani suka tayar min da hankali ina ihu ina fadin yaya Sani kataimake ni bana komawa gidan nan kashe ni zaiyi wallahi.
********* ********* *********
A can lagos din bayan tafiya na bai tafi gidan su ba har tsawon kwana biyar yana hadiyan bacin rai shi kadai.
Da farko ya dauka wasa ne yana cewa in tafi mana ya huta da wahala da yar kauye maganganu dai na batacin yake fada gamay da ni din.
Sai yazo ina dan ya dawo zaiga gidan yai mashi girma ga wani irin duhu ba gyara shi kuma bashi da time din zama yai gyaran.
Don haka ya bugo waya gidan su kannen shi suje su gyara mai gida basu so zuwa ba suka tafi dole.
Sun dawo suna kwarara amai da zubar da miyau na kazantan da suka gani a gidan amai ne ragowan giya ne kai komai sun gani a gidan.
Suna fadawa uwar su kan cewa basu kara zuwa gyara mai gida sai ta hausu da fada inda take shiga ba nan take fita ba.
Idan ya rasa kudi babu mai bashi yadda yake samu ya amshe dan kudin da nake samu ga maman biyu ko wurin kitso.
Yanzu babu inda yake samu sai dai ya arro ko kuma asai mai giyan kyata don mashaya akwai su da wanan kara.
Sai ya kara sanin ashe ba karamin karya nake mashi a gidan ba gaskiya ne da aka ce mutum dan adam yana da rana.
Ga yariyar da ya raina yaga ranan ta tun ba, aje ko ina ba gashi yasan muhinmacina a gidan yasan ina hakkuri dashi to amma kuma shidin ya kasa kyautata min ne bai san dalili ba.
Ina da matukar mahinmaci sai yanzu da ban gidan ya gane hakan duk da bakwa yake dani ba sai ya ga dama amma sai tafiya ya zamay mashi yashin hankali da rashin kwaciyan hankali , ya rasa may ke kawo mai jin yawan tsana na a rashi.
Kodon yawan zagina da mahaifiyan shi keyi ne a gaban take fadin kwadayin mahaifina ya jawo min haka yana gani ita sakarai ne don kawai ya bata diya sai ta bude mashi bakin aljihun ta na kashe mai kudin ta, ba dai a kan wanan diyar tashi ba dai.
Wani yammaci sai gashi yazo gidan su dayamma nan mahaifiyar ta tare shi da zance na tana zagi tana aibanta ni tare da zagin iyayye na kamar yadda ta saba yi idan yazo.
Yai shiru yana sauraren ta sai can da abin ya isheshi yace mummy zuwa zakiyi fa, ki dawo da ita don ba zan sake taba .
Uwar dago cikin mamaki tace haka zaka ce ni ina ganin bata dace da kai ba sam,
Yace mummy idan ba ita ba da iyayyen ta wata mace ne zatai hakkuri damu gaba daya duk abinda muke mata tana zaune tana hakkuri sai zuwan dan uwata ya gudu da ita.
Ke kanki kin san cewa indan yar ki akewa hakan bazaki taba lamunta haka ba .
Don haka ki kama hanya zuwa arewa ki dauko ta kidawo da ita nan shine saukin mu bai kamata ace don ki aka dauki yarinya nan aka bani ita.
Don kwai ina danki ace baki kaunan ta ai gaskiya saadu ne da yake fadi da taimakon ki muke wani abin.
Duk ke ke kara lalatamu muke abin da muka ga dama abin da bai dace ba idan munyi sai baki iya hana mu , sai muga cewa shine daidai don bamu da masu yi muna fada a rayuwan mu.
Shi wanan tsohon ya na shagamu can yake sha a nin shi bai damu ba da halin da muke ciki a garin na babu ci babu shan shi.
Nan dai ya takewa uwa gidan wuta akan sai taje ta dawo mashi da matar shi ya zube mata kudin mota anan ya fice yabarta tana tunane akai.
Yaushe yaran nan ya fara son Safiya hakan nan ban sani ba kodai shima sun magance shine yadda suka magance yaya a gidan shi.
Yanzi ni idan naje da wani ido zan kalli mahaifin yarinya nan dashi nace na rike mai ya amana ko mai.
********* ********* *********
Acan gida bayan baba ya kare fadan shi ya kare da cewa zai hada kudin mota da zaran sun cika bani kara kwana mashi gidan shi.
Bayan fitan shi ne gwagon ummi ta rarashe ni da mama na samu na danci abinci da aka aje mun sai dai ban iya cin komai ba ruwan kunu kawai na iya sha.
Dana dan gyagije namike naje nai wanka na fito har lokacin gwago tana nan zaune na sa kaya a jikina,
Sai lokacin na fara ciro masu tsaraban da nazo dashi da wanda na sara ina gwadawa mahaifiya ta nan dai muka cire ma kowa tsaraban shi.
Na fitar wa aka fitar ana tallata min ne diban ma maman Amina kawata aka kai mata take tambayan nazo ne yaron ke fada mata cewa nazo tun jiya ina nan gidan mu.
Nan da nan aka saye kayan don na sake su da sauki sai gulma ya fara tashi a gidan mu daga dakin inna suke fadin ai gwai dama sun san cewa yaran gwago ba su da kamun kai.
Sundai yi shiru ne naje na dan dano ai maganin mu kenan uwa cikin ukuba diya ma haka ai kadan muka gani.
Na dan samu sukuni don har na fara maida jikina da haske naje na gaida maman Amina kawata mun dade muna hira da ita na dawo gida kada baba ya dawo bai samay ni a gida ba don satan hanya nayi nazo gidan su.
Wai duk da halin da nadawo gidan mu ciki Inna sai da tai bakin ciki da gani na haka na kodan dan kayan da na saro ne ake saida min ban sani ba.
Wani lokaci taimin gori akan rashin dace miji wana sain kuma ai min habaici wai ina wa mutane takama natafi birni na waye.
Don dan kayan da nake sai daiwa yasa mutane na ribibin zuwa sayan unders na yara da yan dogon riga na mata nashan iska da sauran tarkace.
Shine dalilin da inna ta rasa sukuni a cikin zuciyar ta tace wai ai gara na koma akarasa ni can ko yaushe cikin ba babana mugun shawara take a gida.
Ina da sati uku da zuwa gida ne safiyan wata asabar sai ga gwago ta sauka a garin direct gidan mu ta yo sun tare ta kamar yadda suka saba mata idan tazo har da ummi na bata nuna mata komai ba a zuciyar ta.
Hakan yasa gwagon dan sake jiki bayan sun gama gaisawa da mama sai gwago tace dada wanan yaron haka yaje yai muna, ya dauko kaunan shi ya zoda ita gida bada sanin mu ba.
Sai mama din tai murmushi tace muma haka dai muka gansu kwatsan a gari sai dai a gaskiya abin baiyi dadi yadda suka zo muna da labari .
Anyi abu don dadin rai kuma sai abu nason ya koma tsiya haka don ma malam daya tare maganan ya hana kowa ya fadi yace yana tara kudin mota ne , ta koma dakin ta.
Gwago taji sanyi a ranta sai dai taji mama tace a gaskiya dake har wanan yaron baku rike amana ba sam abin baiyi dadi ba wallahi don ma dai anyi kawaici andubi baya .
Gwago tace to ai dada yanzu dai kuyi hakkuri kamai aka ce munyi mun dauka sai dai muba da hakkuri kawai.
Mama ta sake cewa ki sani diyar malam diyar ki ce ba sai an fada ba don in anyi laakari da irin diyaucin da ya nuna tun daga kan auren har kawo yanzu amma sai ga labari mara dadin ji ya samay mu kuma mun ga alama don ga shedan bugu nan da tazo muna.
Yadda duk akeyi mama tayi don ta fadi gaskiya yadda ya dace har da zancen kudin da suka bar ma gwago ta ja min jari sukayi tace wai mijina ya karbi kudin
Amma zatai mai magana ya dawo min da kudina na dinga juyawa da kaina zaifi tana ta ban hakkuri can dai ta tashi zuwa dakin mama ne tayo mata rakiya wurin ummina.
Nan ma hakkuri ta bayar suna cikin dakin ne baba ya shigo gidan wanda inna ta aika a kira shi yazo wai ga gwago tazo.
Yana shigowa yai dakin mama aka ce suna dakin ummi sai ya kama fada yin may ina ruwan ta da ita aiba ita taba ki dayin ba.
Nan dai yake ta sababi irin na maza da iyalin su basu da tacewa sai su kaida ke kafa dokan su a gidan yadda ransu yaso.
Bai tsaya sauren ta ba yace binta kinzo dama ina son zuwa wani sati in mayar maki da yarinyanan .
Sai hakkuri yake bata abin ya bani mamaki naidai tuna yadda take zama ta kare mashi zagi da yankar kauna .
Amma shi yana nufanta da alheri ya kuma bata go ahead akaina yace tana da iko akaina ta tsawa ta min ba sai nazo gida ba.
Hannu na sa akai ina ihu baba yace indan ban rufe masu baki ba yanzu zai debe min albarka dole mama tasani yin shiru mama tana fadin adai tsaya abin abin a sannu ba a hakana,
Tsawa ya daka ma mama tare da cewa indan bata kama mashi baki ba yanzu zai da ita dani mu bar mashi gidan shi.
Duk yadda akeyi mama tayi amma ita inna cewa tayi indan ma na zauna gidan may zan yi ai kawai gara na koma daki na, na zauna shiyafi.
Baba ka taimake ni karka mayar dani idan ka mayar dani kashe ni zasuyi wallahi wayyo baba ka taimake ni yace idan ban isa gare ki ba sai dai kibi duniya.
Ummi na saboda kawai ci kala bata ce dashi ba amma zuciyar ta kamar zai tsage take jin shi ansa rana, ranan labara zamu tafi.
Don gwago zatai dan sayayya da zata tafi dashi na sana an ta can sai wani nan nan dani takeyi don ganin idon mahaifana.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
🧕🏿1️⃣3️⃣🧕🏿
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON WANAN NOVEL DIN KUDI NE.
Ummina dake barci ta falka cikin matsanacin firgici daga barcin da takeyi wanda kwana uku kenan a jare ta mafalki dani.
Kuma mafalki mara dadin takeyi a gamay dani din wani lokaci sai taga na gwauce zan fada rami ko tagan ni a ruwa mai zurfi ina iyo.
Ina gudu ana bina zaa kashe ni da wani guduma a hannun mai shi ire iren wanan mafalkin takeyi koda yaushe hakan ya tayar mata da hankali.
Ta shiga cikin damuwa sosai ta dan saka abin a ranta don haka yau ta kudiri aniyar fadawa baba na idan ya dawo dakin ta.
Haka akayi sai da yagama sauren ta kaf yaji abinda take fada bai bari takai aya ga zancen ta ba ya ko hauta da sababi har yana daga murya sauran mutanen gidan suna jin shi.
Mama ce da taji fadan yayi yawa hakana ta tako zuwa kofan dakin tana cewa haba malam ayi hakkuri koma may nene tunda ka taba fada ai ya isa ko.
Yace a hasale bari matar nan da abin haushi auren yariyar take son kashe wa don rashin sanin ciwon kai.
Yariya na gidan mijin ta zaune lafiya hankali kwance zaki tsiro da wani tsurku wai kila ba lafiya take ba ke kina yawan mafalkin ta ke kila wani abu zai samu yar ki.
To Wallahi ahir din ki da zancen Safiya a gidan nan idan ba haka ba rayuka zasu baci sosai akan haka don sam ba zan lamunta ba.
Har yayi ya kare bata ce dashi uffan ba da safiya kuma ya tusa jidali inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Sai inna ce ta sa mashi baki tana fadin ai kasan dan tallaka bai iya samun wuri ba in bashi ba abin farin ciki yar ki na can lagas tana aure amma ke bakin ciki ya hanaki ki gane haka ki kwantar da kai kici arziki.
Mutum mai bakin ciki da hassada ai har kanshi yake yi saboda mugun hassada daya huda jiki na sheri, har taci ta sude ummi bata tankasu ba sai share su da tayi tana aikin ta a cikin gida.
Kwana biyu hakana suke da baba sama sama sai da taga ya dan fara mantawa da zance ta roki fita unguwa gidan gwagon ta.