Showing 177001 words to 180000 words out of 269010 words

Chapter 60 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13354

Na dai samu ya sausauta ta hanyar kawo mai ruwa da bashi baki yayi hakkuri ya kurbi ruwan ya dago kai yana fadin kin san ida Allah bai dawo dani yanzu ba iya abinda zasu yi maki.
Zan kira in fada ma mijin ta kada ta kara zo min gida may ye hadina da ita da dan uwanta nake da zumunta ba itaba.
Ya dafe kai da hannu guda tare da lumshe idanuwan shi don takaicin da ke damun shi lokacin ranan haka ya karasa shi babu wani walwala a tare da shi.
Washe gari da muka tashi yana kule dasu a ranshi ya baci da su sosai sai zuwa sha daya saura ya fito falo ya zauna.
Na fito da kayan yake farce a hannuna ina son gyarawa sai naji yace da zaki iya dakin fara gyara min nace Uncle ke nan may zai hana in iya aikin lada.
A hankali na sauko kasa inda na fara da yanke mai na kafafuwan shi gyara nake mai yana waya sai ajiyan zuciya yake sauke wai.
Har na gama gyara mai kafafun shi yana a kan wayan naji yayi sallama da wanda yake wayan daidai zan tashi in koma saman kujera in fara yanke mai na hannuwan shi.
Ya kare wayan daidai na dago hannunwan shi zan fara gyarawa yake ce abokina na Canada yana gaida ke ina sa ran zamu tafi nan da wani dan lokaci.
Da sauri na kallo shi nace uncle dani fa kace ya dan subbanci kuncina yace ke fa madam nace Allah ya nuna muna lokaci lafiya Amin yace.
Ya soma magana kamar mai rada bakinshi a daidai kunne na naga alaman kina farin ciki da tafiyan nan ko ?
Nace ai dole uncle don ban taba fita daga cikin kasan nan zuwa wata kasa ba sai wanan karon.
Ya fiddo da karamar dariya yana matsa hannun dake cikin hannun shi yace tafiya ai yanzu kika fara shi don tare zamu dinga fita duk inda zan tafi sai dai idan kinyi ciki ya tsufa zan dan baki hutu a lokacin.
Da shagwaban murya nace uncle ka bari don Allah ni fa ban shirya haihuwa yanzu ba da sauri ya kalle yace baki da tausayi ne ?
Yanzu duk su Aisha suna da yara wanda ada hakan baya damu sai yazo da nayi aure naji nima ina son na shigo gida in samu mai min daddy oyoyo .
Shiru nayi ina tunane don nima yanzu haihuwa ne tashin hankalina don wanan ne karo na biyu da yake nuna min yana son haihuwa sosai.
Don haka ba abinda zan iya farauta mashi rai da shi a wanan lokaci sai daukan ciki da ya kwallafa rai gare shi.
Na nisa ta yadda yake iya jina yace da sauri naga kamar ke abin bai damay ki ba ko nace ba hakana bane Uncle.
Haihuwar dai naga baizo inda ake neman shi ba sai wurin da ba a maraba dashi ina tuna haihuwa na na baya ne kawai.
Da sauri yace kin taba haihuwa ne a hankali na gyada mashi kai alaman eh naji mamaki da baka san na taba haihuwa ba uncle.
Yace ban samu wanda ya fada min ba cikin masu bani labarin ki a hankali na fara bashi labarin haihuwa nawa fuskan shi kawai zaka kalla kaga alaman tausayawa a cikin ta.
Shafo fuskana naji yayi gami da lumshe idanuwan shi yana sauke ajiyan zuciya yace haka abin yake ya samu yai sakaci da samun shi.
Abin da nake gani ya taba yarinyar don baku amsan treatment a lokacin har yakai abin ya shafi yarinyar a ciki nace uncle sai bayan haihuwar ta nasan cewa ina da cutar a jikina.
Koshi sai da yaya Saadu yaga zan halaka ne yasa a kaini asibiti a dubani shine aka san ina dauke da cutan a lokacin don kowa bai kawo haka ba a ranshi.
Yace ni kin ga tun da na samira ya baiyana na tafi akaimin awo sai aka samu nima na dauka sai dai nata yafi karfi akan nawa ne.
Sun dai cuce mu nace dashi yace sun cuci kan su dan zunubi akan su yake Allah ya gani bata zina muka samay shi ba shine saukin mu ga Allah.
Ciwo kuma kaffara ne ga bayin sa kin ga mun samu riba biyu ga abin koma ukku zance idan ba ta sanadin hakan ba ai wata kila ba zamu hadu ba.
So ki fitar da zancen cewa sun cuta muna don ni tu lokacin na bar ma Allah sanin sa akai kin ga ta ida ya saka min dashi kuma.
Na gama yanke mai akaifar na tatara na zuba a inda muke zubawa kafin mu binne wani akaifa da suma da nake tarawa idan sun cika sai na fita baya can in tona rami in rufe su.
Koda na dawo saman kujera two setter na koma na kwanta nayi rigingine ina lallon fankan dake kadawa a hankali falon.
Shima dai shiru yayi nasan akwai abinda yake tunane a zuciyar shi wanda kila bai wuce zancen haihuwan da yaji na taba yi ne koma may ye ai bai nuna min komai ba a fili.
Sai naji ya jefo min tambaya a bazata dacewa na dauka idan mace ta taba haihuwa ai ana ganewa ne ?
Murmushi nayi na dago tare da cewa uncle may kake son ka gane uncle a kai sai ya murmusa kawai yace forget.
Nace tau ni dai tun haihuwana yarinyar bata ma sha nono ba don haka har ta koma banda ruwa bata sha wani abuba a duniyan nan.
Yace kai labarin akwai ban tausayi wallahi abinda mutane da yawa ke fuskanta ke nan yanzu har bakin ciki ya kashe mutum yanzo idan da za a fadi halin da mutane da yawa ke ciki akan lalurar nan sai ka tausaya masu.
Nisawa nayi daga inda nake kwance nace Allah ya sauwa yace amin wayan da aka bugo ne ya dakatar muna da hiran namu nan dai na mike na shiga kitchen ban fito ba don yau yana gida na tsaya hada mashi abinci da zamuci.
A kitchen din ya samay ya byo bayana lokacin ina motsa miya sai jin hannayen shi na ji saman jikina ya rugumay ni ta baya yana fadin.
Na ga dai baki aminta da aikin John a gidan nan ba yanzu na nisa tare da fadin Uncle da raina da lafiya na zan kwanta kato na yi min girki ina ci.
Juyo dani yayi daidai na gama motsa miyan ya juyo dani muna fuskantar juna yace idan aikin namiji ne baki so sai a canza muna da mace dama dauko shi nayi a maaikatar su .
Don banda mace a gida ne nace a bani na miji yafi yanzu kuma tunda kin zo da magana sai a bamu mace don gaskiya bazan lamunci kina shiga kitchen wanan jikin naki da nake huta gajiya na a cikin sa ba yana daukan zafi.
Kunya maganar ta bani na yi saurin dukar da kaina daga kallon shi yace ai gaskiyana fada nafison ki huta ko yaushe sai idan yara sun zo kuma ki ji da namu lalurar duka.
A hankali na dago nace uncle kana ganin hakan ban cutawa shi john din ba dakai naga sabo ya shiga tsakanin ku kama a gaskiya yana jin dadin aiki dakai din.
Kada nazo na shiga rayuwan shi in nayi mai haka kamar na toshe mai wurin samun shi ne ai murmushi yayi tare da dan buga mi baya na yace .
John zai zauna sai ki sama mai abinyi a gidan kada yayi ta karban kudin banza ko macen kuma za a kawo maki ita goben nan in Allah ya kaimu hakan yayi maki ko.
Nace yayi uncle na gode sai dai macen ta kasance musulma uncle don Allah yace kuma dai za a duba ba matsala da haka har na kare na kwashe na koma nayi wanka na shirya na fito muka zauna cin abinci .
Ban yi fushi da zarah ba ina dan kula ta muna zama muyi hira sai dai bata gane komai a gidan yadda take so.
Ranan yaya Saadu ya shigo da marance bayan na cika mai ciki da abinci nan suka zauna da shi suna fira ganin sun dauko hiran aiki yasa na dan basu wuri na samu zarah a dakin ta kwance.
Tana ganina ta mike zaune nace ai na dauka barci kike yi ne tace a a kwantawa dai nayi naga yau yaya yana gida bai fita bane shiyasa ban fito ba.
Wuri na samu na zauna kusa da ita ina cewa don yana gida shine baki fita ta dan murmusa tace ban san abinda nayi wa yaya ba baya kallona a yar uwanshi kamar kice yar uwar tawa yanzu don kice kawai may kula ni a gidan.
Nace a a zarah kin fi ni sanin waye uncle fa dan a tare kuka taso wuri daya dashi yakamata ace kin san ko waye uncle yanzu.
Murmushi tayi kawai mai kama da yake tace nima ina ganin dai gida zan koma nace tun yanzu Zarah mai mukayi maki kuma ?
Tace babu komai anty gani dai nayi kamar zaman nawa yana takura maku ne nace ko daya wallahi kece dai kika kasa sakin jikin ki damu.
Nan dai na zauna mukai ta hira da ita sai da uncle ya kirani nabar dakin nata yaya Saadu ne zai tafi shine kiran da yake min din.
Nan yaya din ke fada min zai koma gobe dawowan da zai yi tare da iyalin shi zai dawo garin naji dadi sosai yake ce min yaya waya gida dazun da yana hanya.
Naji dadin haka yace baba ya fada min abin arzikin da maigidan ki yayi masu da sauri na juya na kalli uncle din .
Yace tau bai fada maki bane bana baba da ummi zasu sauke farali a kasa mai tsarki har da Sani don ya kula dasu.
Bansan lokacin da na juya wurin uncle din ba ina murna yaya yace ai na rigaki yin godiya ko ya fice yana yi min dariya.
Ranan ban san ma irin godiyan da zan ma uncle din ba mun dai kwana muna farantawa juna rai kawai don banda abin bashi bayan wanan din.
Kwana biyu dayin haka na samu uncle a daki yana shirin fita nake cewa ina son zuwa gidan Anty Aisha.
Kamar ba zai yi magana ba sai can yace nafa fada maki ban son yawo a rayuwana nafin inganki a gida kullun.
Nace don Allah uncle kayi hakkuri ba dadewa zamuyi ba koshi don munyi waya da itane tace yaran ta biyu ba lafiya.
Yace sai ki shirya in sauke ku in zan fita nima in duba yaran daga can naji dadin hakan don dama tana min korafin bai taba zuwa gidan ta ba.
Mun isa gidan akai muna iso mun samu maigidan ta dakishiryata zasu fita a lokacin nan dai muka gaisa dasu.
Mijin nata yana ta faman kamay kamay da gani baida gaskiya nan suka fice suka barmu da ita munga yaran basu da lafiya har lokacin.
Yake tambaya ko an kaisu asibiti tace baban nasu ya sawo masu magani dai tace baida kudin kaisu asibiti sai naga ya tabe baki kawai.
Yana bin gidan da kallo bai dade ba yace shi zai tafi zai dawo karfe hudu ya dauke mu naji dadi sosai da zai fita ya kira Aishan suka fita tare.
Ta dawo tana murna tana fadin yau maganan hajiya ya tabbata yau yaya ne a gidana Safiya ?
Murmushi nayi nace albarkacin yaran ki ne ya kawo shi tace a a albarkavin ki dai gashi har da zama gidana yau safiya abinda kullun gidan nan ake min gori dashi.
Nan dai ta shiga bani labari don ta tura zarah tai muna girki haka yasa ta samun daman sakewa tana bani labarin halin da take ciki a gidan.
Na fahinci abubuwa da dama a gare ta sai da bance komai ba banda hakkuri da na bata ta fitar da kudi masu yawa tana nuna min wai uncle ne ya bata su takai yara asibiti.
Nace kin ga ko sai ki kai su don asan halin da suke ciki tace ai gobe in sha Allahu zan kai su anan dai muka wuni tana cikin farin ciki damu.
Ya dawo ya kwashe muka tafi tana ta mashi godiya mun dauki hanya ne naji ya nisa tare da fadin mai kika fahinta a zaman Aisha a gidan nan ?
Nace bari mu sauka uncle akwai magana ai sai ya dan kalli zarah dake baya zaune yayi tsaki har muka kai gida ba wanda yayi magana a cikin mu.
Sai da mukai sallah ishai muka dawo falo nan na dauko mai maganan Aisha din yace tun farko sai da na fada masu ba mutumin kirki bane suka ji.
Alokacin yana sakar masu kudi sun dauka mutumin kwarai ne niko tun tasowan mu dashi nasan dan karya ne sosai.
Nace uncle yanzu tunda har akwai haihuwa har uku a tsakanin su baza a bi ta wanan ba taimaka mata ko masu su duka ya kamata kayi.
Ta hanyar sama masu sanaa da zasu dogara dashi da yaran su don na fahinci tana cikin wani hali a gida don baka ga part din kishiyar taba tsan wallahi amma ita ga nata kamar na wata tsohuwa can.
Tsaki yayi yace ko an bata wanan mugun mijin ai ba zai bar mata ba nace uncle adai tamaka mata din yafi don gorin da suke mata a kan ka.
Yace gori fa ?
Shi har yana da bakin da zai min gori akai wanda kulun yana office dina da bukatar shi nace kagani shike morar ka itako bata kosan anyi ba.
Yace zai kira Aishan idan yaranta suji sauki ansan abinda za ayi mata din nace uncle mun gode wallahi.
Kallo na yayi yace wai ke a ina kika koyo wanan godiyar taki ce haka tun bakiga may zanyi ba kina zabga min godiya haka.
Nace koma may zakayi indai ka gyara mata wurin zamanta ka bata abinda kudi zai dinga shigo mata ai ka gama mata komai.
Yace ai ido nasaka masu daga su har hajiyan don naga gidun su nace uncle kayi kuskure wallahi idan basu dadi a wurin ka ba duniya wurin wa zasu ji.
Nan dai nayi ta kawo mashi musalai iri iri yana saurare na bai yi magana nasan dai ya gamsu da bayani na ne da nakeyi.
Yace wai ke indan da kin yi karatu mai zurfi zan iya dake kuwa Safiya ?
Nace uncle don may ba zaka iya dani ba ai fahinta daban fannin aure daban don haka karkaji komai a kaina .


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/18/20, 10:16 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,


🧕🏿5️⃣9️⃣🧕🏿


NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN KIN FITAR UBANGIJI YABI MIN HAKKINA A KAN KI/KA DON BAN YAFE BA, , , ,


Kamar yadda yaya Saadu ya fada haka ne ya faru don yayo kaura daga kalaba zuwa abuja da iyalin shi inda suka zo da yar uwan Samira da mijinta ya rasu zata dan kwana biyu a wurin su.
Sai bayan kwana biyu suka zo gidan mu don bamu da wani nisa sosai dasu dasu ban san da zuwan su ranan ba sai ganin su nayi kawai a gidan.
Sun shigo ina daki Zarah ce tazo tana fada min zuwan su cewa tayi nayi baki suna falo azatona ko anty uwace suka sake dawowa gidan.
Amma kuma sai nayi tunanen mai zai kawo su kuma in ba rashin zuciya ba yadda aka kwasa dasu din nan ya nuna shi sam bai san su ba.
Wanda kuma nasan yayi hakane don ya kakabe su daga gidan namu gaba daya da zuwa don zuwan nasu babu alheri a cikin sa.
Fitowa nayi sai mukayi arba da sister kamar yadda suke kiran safiya karama dashi.
Nace Lah bakin kalaba ne a gidan namu baku tsaya munzo taron ku ba har kun tula min nauyi na aka ?
Samira tace a, a mun huttar dake aikin san ke amarya ce ba a matsamaki yanzu na samu wuri na zauna ina mikawa sister hannu tazo wuri na sai yarinyar ta make hannun ta bata zuwa.
Gaisawa mukayi ina tambayan su mutanen gida da sauran yan uwanta tare da fadin ai na dauka zaku zo min da mummy ne wallahi.
Tace mun so mu zo da ita kodan azumi dake tafe takine sai da gabaya zata biyo mu in dan ta shirya.
Nace kai mummy ho har wanu shiri zata yi kuma makin ta biyo ku kawai kuzo tare samira ne tace wai Safiya kin ko ga yadda kika canza gaba daya.
Nace kai samira dashi kuma zaki tare ni tace wallahi safiya kin canza gaba daya komai naki ya canza kamar ba Safiyan yaya saadu ba.
Dariya muka ka kwashe dashi gaba dayan mu falon nace aikin Uncle tace aina gani wallahi gaskiya aure ya karbe ki sosai wallahi.
Nayi murmushi dadi har cikin rai na nace bakomai bane Samira sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login