Showing 117001 words to 120000 words out of 269010 words
son ki sani ban taba haduwa da macen da hankalina ya kwanta da dabiun ta ba irin ki.
Gashi dan haduwan na dake da madam ta fara min maganan nan maganar sai bibiyata takeyi na rasa sukuni a tare dani.
Sai kuma naga yayi murmushi yace sorry bazan iya ci gaba da fada maki ba amma na gaya maki gaskiyan zuciya na don ba wani lokaci nake son a dauka ba ga zancen.
Nayi shiru ina sauraren shi sai da naji abunda ya fadi a karshe nai saurin dago fuskana sai wanan lokacin muka hada ido dashi.
Take gabana ya fadi don kwarjinin sa da na ga ya fito fili a idona nace da wuri uncle yace dani yes I mean it, idan kina shakkun hakan gara ki daina ko kuma kina iya bani baki ki gani.
Nayi shiru na rasa may zance dashi yadda naga ya zare min a lokaci guda to ni may zance dashi eh ko a a .
Har ga Allah uncle ya samu karbuwa ga zuciyana don ina son shi har cikin zuciyana saboda me ne sulaiman dai namijine wanda duk wata mace ke burin mallakan shi a matsayin mijin aure mutunci addini kamala da natsuwa da gaskiya irin na nuna shi din daban ne da sauran mazan dana sani akwashi.
Amma kuma nauyi da kunya ban taba ganin wanda nake jin nauyin shi da kunya ba irin shi don haka bazan iya nuna mashi kai tsaye na amince da bukatan shi ba.
Bai kara yi min magana ba har muka isa wani shopping mall anan ya tsaya yace mu fita kowa ya dauki abinda yake so.
Kunya bai bari na dauki komai ba sai wani turare dana dauka ganin kuya bai bari na dauki wani abu sai naga ya shiga daukan duk abinda yaga ya dace yana kadawa kwado sai da basket din ya cika sosai har yana zuba ya bari.
Mukaje gurin biya ya biya akai muna packeg din su a ledojin shagon muka fito.
Bai tsaya ba sai wurin wani shagon sai da nama kala kala nan ya shiga shi kadai sai gashi ya fito da ledoji shake a hannun shi yaja mota muka tafi.
Ba magana haka muke tafiyan sai ya koma hira da yaran har muka kawo gida sun fita na bude mota har na saka kafa na daya a waje naji yace dani ina sauraren ki nan da two weeks.
Ban ce dashi komai ba sai da na fito daga motan ne nace mun gode bai bari mun dauki komai ba ya kira security daya ya taya shi shiga da kayan ciki.
Lokacin yamma yayi sosai suna falo zaune muka shigo duk idanuwan su a kan mu anty farin ciki ya kasa boyuwa a fuskanta.
Suko nasan ba komai ya zaunar dasu ba sai gulma basuyi mamaki da irin kayan da muka shigo dashi ba don sanin waye sulaiman din da sukayi.
Bai tsaya ba baya ya aje sai yace da anty zai koma sai dai da safe idan ya shigo karyawa mikewa tayi ta bishi baya suka fita gidan tare.
Sai lokacin Faiza tace yau kan kun sha dadi wallahi naso ace anty ta bari mun bi ku muma mu lakato arziki don ba a barmu mu dawo haka ba.
Wai safiya kodai wani abu na shirin faruwa ne keda uncle nace may ko ke shirin faruwa rabona ne kawai ya koka a wurin shi dariyan ku akaina yazama min sanadin samun alheri yau a gurin sa.
Tace indai yai wari maji amma ai banza baya haka da sauri fati tace balle ma may zai yi wari a nan wanda ke gogayya da mata hamshakai ne zai tsaya a nan.
Nace ako hakan in Allah ya nufa sai ki ga ya faru anan din inda ba komai tai saurin cewa ki iya lafazin bakin ki ramin kura ba wurin wasan yaro bane koda kuwa an rika masa.
Dariya na wuce dakina ina yi ga leda a gaban su babu halin budawa su gani kada anty taci masu mutunci akai dole suka zauna zaman jiran ta ta dawo.
A can waje kuma sun tsaya wuri motan shi ne yayin da ya dafa mota da hannun shi daya suna magana da anty din tace to yaya ina fatan dai kun dan fahinci juna wanan fitan da kukayi tare.
Yai murmushi cikin jin kuya yace mata wanan kaunar taki kunya yai mata yawa taki sakin jiki mu fahinci juna kamar mai tsoron kar na sayar da ita.
Tayi saurin fadin may Safiyan tayi maka kuma yace yace kiyi hakkuri zakiyi mamaki amma wallahi nidai yarinyar tayi min so sai ta tsaya min a rai.
Amma naga kamar ba za iya shawo kanta ba don tana da kunya sosai ga kurciya a tare da ita kuma.
Anty zatayi magana ya hanata yace don Allah madam ki taimaka min ki shawo kanta wallahi son safiya nake yi da zuciya daya ina son ga na taimaka wa rayuwanta .
Auren ta nake soyi na bada dadewa ba sai dai ban san yaya zaku dauki maganan ba yanzu.
Ga baki daya maganan shi ya gama kashe mata jiki da mamaki don bata taba tunanen zai afaka haka da sauri a sona ba shiru kawai tayi ma rasa may zatace dashi.
Ganin tayi shiru yace madam kina mamakina ne ko tace ina jin ka dadi ne ya kashe ni wallahi wai yau kaine kake maganan aure haka a gabana babu kunya sanan wace kake so din gata yar gida ce.
Sulaiman gaskiya ka gama kasheni da jin dadi don haka ka kwatar da hankali ka da yardan Allah kamar ka auri safiya ka gama.
Bari ma ka gani yanzu da na shiga zan tun kare ta da maganan har sai ta bani baki ayi don yarinyar na jin magana na sosai.
Don haka ka barni da ita kawai zan san yadda nayi da ita kar abin ya dauki lokaci mai tsawo iyayyen ta kuma zan san yadda na lurar dasu akan zancen.
Yaji dadi har ya kasa boyewa ya rika fadin na gode madam thanks alot Allah ya bar min ke kin zama babban yayada gaske.
Tace au dama ke nan ta karyace yace ai da madam kike yanzu ko zamu zama sarakai dake tace aban tukwaici na yace ai tukwaicin ki shine daga ke ba wata a gidan nan .
Na biyun bazan fada maki ba sai abin ya yuyu zaki sani sai suka sa dariya a tare a haka ya tafi tana shamatar shi yana cewa yaji.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
🧕🏿4️⃣0️⃣🧕🏿
YA ALLAH MUNA ROKON KA KABA MU IKON BAUTA MAKA BAUTA TSARKAKKEKE KA KUMA KARBA MU NA IBADUN MU, , , , ,
Lumshe idona nayi tun da muka fara tafiya ashe da haka nayi barci sai da mukai nisa sosai ni kadai a baya zaune sannan na falkafirgigi daga barcin ina kallon gaban mota inda driver keta faman sharara gudu.
Sai yamma lis muka iso makwabtan karkaranmu nan na dan fahinci ida muke don da gaba yana tafaduwa don ban fahinci komai ba.
Garin muke shiga lokacin marance yayi sosai don haka mazaje da yawa suna kofan gidan su suna dakon kiran sallah.
Kwantace hanyan gidan mu nake mai har Allah ya kawo mu lafiya na nuna mashi gidan mu ya nufi kofa yai packing a kofar gidan .
Duk hankalin mutane ya dawo kan motar suna son su ga wanda zai fito a wanan mota mai kyau haka ganin ta tsaya a kofan gidan mu ya su yaya sani tasowa da abokan shi.
Da sauri driver ya fito ya bude min mota na sagalo kafa daya dayan na a ciki na tsaya dauko hand bag dina zan fito.
Yaya sani yace ah Safiya ne fa da sauri yazo yana kokarin rike marfin motan da nake fitowa ciki daga ciki suma sauran sannu da zuwa suke man na gaishe su cikin mutunci sai na nufi cikin gida.
Nan suka fara biyo ni da kayan yar wurin mamace zata fito sai gani ta tsaya tana kallo na don bata sanni ba sai da nace da ita maimuna ina zaki sai ta dauki muryana tace Safiya ke ce nace nice maimuna.
Nan ta fara ihu lah ga Safiya ga safiya daidai lokacin da nake kutso kaina cikin gidan kenan duk hankalin su ya koma wurina suna mun kallon kurrullah.
Duk suka rufe ni suna min sannu da zuwa yayin da abokan yaya sani suke ta shigo min da kaya daga ciki ni kaina abin ya bani mamaki ko shiga daki ban yi ba bayan mun gaisa dasu mama sai na wuce dakin baba kai tsaye don in ga halin da yake ciki.
An zaunar dashi wai yai sallah amma saida ummina ta tsaya daga bayan shi na shigo dakin ina cewa sannu baba yaya jikin ?
Yadago kai zabban tausayi yace safiya kece tafe nace eh sannu baba yana fadin wai may yasa su ka fada min baida lafiya banji may yake fadi ba sai da na tambayi mama dake gefen shi take fada min.
Na juya wurin mama ina tambaya anko tafi asibitin birnin yau sai tace man wai kudin da aka samu arro baya isa don tun a daukan mota da za a tafi rabin kudin ya kara nace haba haba mama nace a kaishi ko nawa ne , gani nan tafe ai zan biya.
Na dan tsaya tsaye shiru ina kallon yadda baba yake wahala da bautar Allah sai na fita dafa daki na samu kanne na sun shiga min da kayana dakin mu .
Sai dai suna waje suna gardaman wai kwali goma ne inji yar wurin inna sai dan wurin ummi kanina yace hummumm sha biyu ne na gardama ya kaura a tsakanin su.
Inna ta kwala ma yar ta kira wai ina ruwanta ko kwali dari ne na shigo dashi tasan sanan da nake yi na samu kwalayen da na shigo dasu iyayyayena suna murna.
Kai kawai na girgiza na ce a ban buta nayi alwala daga dakin ummina ban tsaya sauraren ta ba bayan munyi sallah ne na fito na samu yaya sani nake cemai yaka mata mu tafi asibiti da baba sai yace ai maganan kudi ne da mota nace motar da na zo da ita zamu tafi.
Yace sai a bari sai da safe ina shiga dakin nace dashi yau dai zamu tafi yanzu ma zamu kama hanya dawa zamuyi tafiyan ?
Nake tambaya yaya Sani din ina dafa baba ina kai sannu yaya jiki ya gyada min kai alaman da sauki jikina ya kara yin sanyi don dai ni a yi sani na dashi ban taba ganin yayi ciwo irin haka ba.
Mama tace bari taje ta shirya don da ita za a tafi inna da ummi su zauna gida amma da inna ta samu labari sai ta tada fitina wai ita zata .
Yaya sani yace ai ba kasuwa zamu ba da kowa zaice zai tafi da mama kawai zamu sai ni da Nura yace mata.
Na fita naiwa driver magana kamar yadda Sulaiman yace in sanar dashi duk abinda nake so nasa ankai mai ruwa da maltina da abinci yana ci ne sai gani na fitinan nake fada mai tafiyan mu birni.
Sha daya na dare muka isa asibitin basu so su karbe mu ba a lokacin sai da na nuna masu kudi sannan suka fara nan nan da mu, har likita suka tayar cikin daren nan yazo ya duba baba maganin da ya rubuta.
A cikin daren nan su yaya Sani da driven nan suka fita neman magani anyi saa an samu a wani shago sai dai shi yaya sani yana ganin yawan kudin don dubu ashiri da wani abu suka kaso .
Ya dawo yana fada min nace mun yi arziki ai tunda an samu tun cikin dare akaiwa baba aluran da bashi maganin sai gashi ya samu barci sosai ranan.
Washegari nacewa driver ya wuce sai yake cewa ai sunyi waya da maigida yake cewa ya dan tsaya don zirga zirgan mu ya taimaka muna naji wani iri a raina sai dai a fili cewa driver nayi anya ayi haka bazamu takura maka ba ?
Haba madam aini a kan aiki na nake daganan har ki gama banda damuwa ko kadan Allah dai yaba baba lafiya.
Nai mashi godiya sosai yace babu damuwa hajiya ai mu aikin mu ne naga kuma oga ya damu sosai da ciwon na baba murmushi nayi kawai.
Sai na tuna ban kirashi ba tun jiya kamar yadda yace in kirshi din don ya anshi wayana yasa min nombashi da zamu wuto.
Gefe na koma saida na tattara natsuwa na wuri daya sanan nai dialing din nomban na shi ringi na uku ya daga wayan yana cewa.
Safiya yaya ai na zaci bazaki kirani ba kin ga mutanen gida kin manta da kowa.
Murmushi nayi nace wallahi ba hakana bane ya dan kwaikwayeni yace to yayane nace kawai dai jikin babane ya tsoratani jiya da na samay shi jikin ba dadi wallahi.
Amma yanzu ya samu lafiya sosai don maganin da aka rubuta mai da allurai tunda ya sha su ya samu barci jiya sosai.
Yace masha Allah haka akeso to yaya mutanen gida nace suna lafiya sai nai shiru kusan tare mukai magana ina cewa kuma har da wani dawai niya haka mai yawa.
Yace bake nai wa ba iyayyena da kanne na naiwa tsaraba ki basu godiya na fara mai yace haba na fada maki bana son haka nifa iyayyena ne yanzu koba hakana bane ?
Murmushi na danyi yake cewa yanzu dai hankalin ki ya dan kwanta ko baba ya samu lafiya sai na sauke ajiyan zuciya nace hakane amma da hankalina a tashe yake so sai.
Don mu din tallakwa ne na karshe indan baba ya kwanta wa zai dube mu shi kaga hankali na ya tashi sosai.
Yace karki manta da cewa Allah ne mai yi ba wani ba yanzu bagashi ya samu sauki cikin yardan ubangiji ba nace haka ne kuma.
Yace idan ya tashi ki gaida min shi zan shiga meeting yanzu dama don baki kirani ba ne yasa ban kiraki ba yanzu kuma naji dadi alama ya nuna na dan samu karbuwa ke nan.
Kai nace haba uncle kabar wanan magana tukun yace na bari as you wish ganin zai kashe wayan yasa nace sai kuma driver yace kace ya tsaya damu.
Yace eh haka na umurce shi don idan ya wuce ina zaku samu abin yin zirga zirga shine nace ya dan dakata har muga yadda hali yayi.
An gode na kara fadi zan shiga godiya naji ya kashe wayan shi kit na dubi wayan ina murmushu na shiga dakin da aka aje baba din har lokacin yana barci naja kujera na zauna tare da kafa mai ido.
Mama tana zaune a kasa saman tabarma tana karyawa da abincin da na sa yaya Sani ya sayo muna don bamu da kowa a garin.
Na dan dade a zaune sai ya motsa da sauri na dago ina cewa sannu baba yaya jikin ina dan gyara mashi kwaciya yace Safiya ke ce yaushe kika dawo ?
Nace a sanyayye jiya na dawo baba yaya jikin yaya jikin baba ?
Yace jiki da sauki Safiya na gyara mashi kwaciya yace baiyi sallah ba da tai makin mu nida mama muka kamashi ya kewa yayi alwala.
Bayan ya idar da sallah ne yake cewa nan ina ne mama ne ke fada mashi ai asibitin birni aka zo dashi jiya da dare da safiya ta iso.
Yace Allah sarki sannu Safiya nagode nagode ubangiji yai maki albarka yasa ki gama da duniya lafiya nace amin baba mama tace yau ga ranan diya mata mun gani a gidan.
Don badon Allah ya taimaka ba da bamu san yadda wanan alamarin zai kaya muna ba kana zaune a gida ciwo zai halaka ka babu yadda muka iya .
Gashi daga zuwan mu jiya jiya har mun ga haske gashi yau ubagiji ya nufa ka bude ido nace baba don Allah ka rage yawan tunane don likita yace tunane yai maka yawa har zuciyar ka ya kumbura.
Murmushin karfin hali yayi yace yaro yaro ne tune ne ai dole mai rai yayi shi balle ni da gidana yake batun fin karfina inda rai na kuma don may bazanyi tunane ba safiya ?
Nace baba hakkuri za a yi abar ma Allah komai ubangiji yana sane da komai da bawa ya gani yanzu dai may zaka iya ci a sawo ma ?
Yace ban jin cin komai sai barcin da nake bukatan komawa don idon nan nawa kamar asa min abu mai nauyi nake jin shi.
Nace baba ka daure kasha tea mai dan zafi ko hajin ka zai warware ka kara samun karfin jikin ka.
Yace dadai kune ne kila zan dan iya sha da sauri nida mama muke cewa ga kunu nan an sawo bari a baka yaya sani ne suka shigo shida driven nan suka shiga gaida shi.
Bai sha wani abin kirki ba ya koma barcin muka sauke ajiyan zuciya muna kallon yadda yake sauke numshi a wahale wai ma cikin yaji sauki ke nan.
Sama sama muke hira da mama ina fada mata irin zaman arzikin da muke yi da anty da yan uwanta