Showing 57001 words to 60000 words out of 269010 words
sosai gani zaune gida banda lafiya.
Banyi magana ba naji yana cewa umurni na baki ba son jin raayin nake so ba ki mata magana a sake ta.
Na nisa nace shike nan kiran yace eh shike nan nake so ki fada mata a sake ta.
Na mike ina ce mai ai da kai kai mata magana zai fi don zata fi jin maganan ka sama da nawa do ni ban san ta inda zan dauko mata zancen ba.
Rashin mutunci tai mata ta dauki mataki ta dauka irina ne da kuke wa son ranku a gidan ku taka ni iya son ranku a zauna lafiya.
Ni banga laifin maman biyu ba da ta dauki mataki ga marasa mutunci irin ku wayan da basu san darajan aure ba.
Ke ya isa ya dakatar dani ta hanyan daga min hannu shi yace umurni fa na baki in kina son kanki da lafiya gidan nan kiyi abinda na umurce ki da shi.
Fuskan shi babu alaman sauki gare shi don haka na juya na tafi kawai ba tare da nai wani magana ba.
Da safe nai sammakon zuwa gidan maman biyu nayi sa a tana gida kasa na zube ina mata godiya ga hawaye na zuba a idona.
Ta ce assha safiya tashi tashi don Allah may ye hakan ai dole a tausaya maki don kinyi karanta da irin wanan rayuwan.
Dudu fa baki kai ashirin ba amma kike fuskantar wanan bahangon mijin naki mai rayuwan kazan ta.
A gaskiya dani wata ce a cikin zurian ku da sai ince a raba wanan auren don baida alaman nadama ko gaba duk kaga namiji yakai haka alamarin akwai ban tsoro cikin sa.
Nace yanzu ma shi ya turo ni akan nazo na baki hakkluri a sake ta wai idan ba haka ba zan gane kurena gare shi.
Tace da sauri kinji ba na fada maki ai baida nadama ko kadan ai dana sani abarshi can shima amma sai na tausayama luluran da yake ciki.
Gaskiya naso yin wani abu akan zaman nan naku amma sai ina ganin kamar ciki ne dake .
Nai saurin dagowa ina duban ta a gidimay nace ciki kuma anty tace tabbas indan ba hasashe nake yi ba kina da shigan ciki.
Gabana yai mugun faduwa tace yaushe ne rabon dakiyi jini a tare dake ?
Nai shiru ina nazari can nace gaskiya wata uku kenan tun da nayi ina gida ba sake yi ba.
Tace shit,
Zargina ya tabbata gaskiya akanki na dade dama ina zargin hakan amma zan sa aimaki test a gani.
Yanzu ki ci abinci zanyi waya a sake ta don ba imani ke ga irin su ba tare suke da yan daba sai dai da yake zamu kafa hujja akan in wani abu ya samay ki nan da shekara biyar itace.
Naga tasa akawo mata abinyin test ta auna fitsari na ya nuna positive alaman ina dauke da cikin wata ukun.
Nai bakin ciki da jin wanan labari kwarai da gaske munyi sallama zan tafi take cewa in kwantar da hankalina killa sanadiyar cikin nan in samu sauki a gurin shi don wasu maza nason yara.
Ta dan bani shawarwari masu mana ta cika ni da abin arziki na bar wurinta zuwa gida zuviya ciki da bakin cikin labarin cikin dake jikina.
Yana zaune ya kura ma tv ido na shigo bako kin dawo sai cewa yayi yaya kin samay ta a gida ?
Nace eh na samu dama zata sa a sake ta saboda kai koda banje ba din tace abin da tayi matane ya bata mata rai ai.
Bai yi magana ba kuma naji ta yadauki waya kowa yake sanar ma zancen sakin nata oho nadai ji ya dade yana waya din.
Nikan abinda ya damay ni ya damay ni zancen cikin dake jiki nakewa bakin da nadama ina tausayawa rayuwan da abin cikin cikin nawa zai taso ya ga ubanshi nayi a duniya.
A haka ma ba tarbiya yaya za a ce aiwa yara tarbiyan rayu kirikiri bani shiga mutane duk da bariki ana cewa ba ruwan wani da wani .
Ina ganin barikin dane bana yanzu ba don wata mace da tazo kitso ya dawo ya shigo murtun compound din tace .
Na dis yeye man you marry , .
Dis man too dey follow women .
Murmushi nayi mata kawai ban bata amsa ba sai wata da take zaune ne tayi mata magana da cewa hakana fa ba kyau.
Sai tayi shiru damuwa ya isheni da fargaban halin da zan shiga nan gaba a garin mutane .
Sai wuraren sha dayan rana aka sako lilliya daga hannun sojoji bayan tasha dan banzan wahala.
Haka ya daure ya fara fita tun wanan ranan baya zama gida yana wurinta acan kafar ta karasa warkewa a hanya.
********* ********* *********
Yau na tashi jikin ba dadi ga damuwa dana sawa raina ga kuma halin maigidan ba sauki akan komai.
Kwace nake a falo saman dogon kujera nayi da daya da kafana ko zan ji dadi jikina misalin karfe biyar na yamma.
Can na fara barci naji dawowan shi gidan yana gauran kofan shigowa gidan gabana ne ya fadi don ganin shi a murtuke da fuska.
Innalillah wa,inna ilaihi rajiun Allahuma Ajirni min musibati waakhimi min kharir minha na anbato a raina.
Ya shigo yana ta faman kalle kalle har ya kai zaune saman kujera tsoro ya kamani don ban an damay ya shigo ba.
Na dago cike da natsuwa da girmamawa na furta sannu da dawowa bai amsa min ba sai taba da ya ciro cikin aljihun shi yana kokarin kunawa warin taban ya gauraye falon lokaci guda.
Na mike da sauri zan bar falon sai lokacin yai magana yace ke mayye haka kuma ?
Ina kokarin tare aman da yazo min a baki nace zan zan zan sai na mike da gudu na fada dakina direct makewayi na shiga nai ta shega amai aciki.
Bina yayi da kallon mamaki bai yarda dani ba, ya mike ya bini yana tsaye nake ta aman sai da nagama na mike zan fito naganshi a tsaye ya rike kugun shi.
Gabana ya sake faduwa yana min wani irin kallo na tuhuma mai kama da bai yarda dani ba yace ke mai ke samun ki ke amai haka.
Na amsa dakyat da cewa ban da lafiyane .
May ke damun ki koma may nene ke kika sani don ni banda lokacin ki ya juya har ya fara tafiya ya juyo yana ce mun ki sani ban son kazanta a gidana.
Na yamutsa fuska nace kona bata ma aini ke gyarawa ba wani ba ya juyo yace may kika ce ne ?
Nace bada kai nake ba ai yace shgiya naga randa bakin nan naki zai mutu da bakar magana dibi yadda kika murje kikai wani bulbul dake duk abincina kike cinyewa ga banza.
Yafice na sauke ajiyan zuciya na zauna nadan huta na fito kai tsaye kitchen na fada don girka abinci don nasan a gida zai kai dare tunda ya dawo da wuri.
Na gama aiki da kyat na shiga na watsa ruwa don lokacin sallah ya gabato ina zaune ina lazimi naji ya kwala min kira.
Na taso dagani sai yar doguwar rigan da anty ta bani ranan da naje gurin ta tace ta gani ne dataje sayayya ta sayo min shi.
Na fito abincin da na aje mai yana bude na sauke idanuwana akan abincin dake gaban shi din.
Ya watso min harara yana cewa wani irin abinci kika dafa haka nace shi kadai ya saura muna a gidan shiyasa na dafa taliya ne nai jelop din shi.
A fusace yace what, what are you saying ?
Kina nufin har abincin da na sayo yakare komay ?
Na girgiza kai nace yaushe rabon da ka sayo abinci a gidan nan wanda ka sayo din ai shi na dafa lokacin da bakada lafiya masu jiyan ka suka cinye.
Ya dakatar dani da hannu yana fadin ya isa haka maganan ya isheni sai ki zauna ki cinye dama haka kike so ai.
Ya dauke makulin motar shi dake saman tabur yabar gidan yana faman huci.
Sai da muka share kwana uku cur ban da lafiya kuma ba a girka komai a gidan.
Ina kwance daki ina fama da kai na nidai kamar kar maman biyu ta ambaci cikin nan wahala ya soma zuwa min.
Sai kawai gashi ya shigo min daki misalin goma na dare don rashin imani irin nashi sai ji nayi ya afka min .
Na soma kuka ya gama ya daga yana cewa may ye haka tsiyan azo wurin ki kenan walahi ki damu mutum da munafukin kukan ki.
Na dago ina cewa azo min haka kamar wata karya ni kadai nasan abinda nake ji a jiki na yanzu haka ji nake kamar baya na zai tsage san nan ban ci komai ba tun safe ga yunwa na damuna.
Yakai kofa ya juyo yana cewa ai sai ki samu abinda kikaci ko kije asibiti adubaki nace da nawa zan tafi asibitin yace ke kika sani.
Washe gari ma da ciwon na tashi don da dare banyi barci ba ciwon mara ya hanani shakat a rayuwa na.
Ban fito ba har ya gama shirin shi zai fita komay ya gani sai ya leka dakin nawa.
Ina kwance ina faman murde murde a saman gado ni kadai a dakin ya leko yadan dade tsaye akaina sai ya karaso bakin gadon yana cewa.
Wai ke may ke damuwan ki ne haka kike faman murde mude a gado ke kadai a dakin ?
Da kyat na bude bakina nace cikina ke ciwo sai kaina dake sarawa kamar zai balle min nake ji.
Ya fita da zai dawo sai gashi da magani da maltina da peak milk mai sanyi a leda da kayan abinci ya sayo.
Ya samay ni a falo na yi laga laga dani ya miko min maganin da maltina yana cewa ga magani ki sha.
Nai mamaki ganin magani harda maltina ya sayo min babu kunya babu alamanta ya zauna yana cemin tashi ki sha.
Da taimakon shi na hadiye maganin sannan ya hada min maltina da madara yace in shanye kafin ya fito.
Bayan kaman minti shirin sai gashi ya fito ya dubeni yace yanzu ya fada maki ko yana nan ?
Nayi ajiyan zuciya nace ya fada min nace na gode yace na taimaka maki ne don nima kin taimaka min da banda lafiya don haka arama ma kura aniyan ta.
Na ciza baki na yunkura ina cewa aiko kura ta gode in don Allah akai mata.
Ya harare ni yace gunma ki wartsake don ba zan dauki nadewa a gado ba tunda kun hanani hurda da yan mata na yanzu.
Na saurin kallon shi ina cewa wa ya isa ya hanaka da abinka muka ganka mu mun isa wanan sai Allah daya hallice ka ai.
Sai kawai naji ya kyalkyale da dariya sai nai saurin dago kai na kalle shi cike da mamaki yau shike dariya haka kamar ba shi ba.
Yace ashe kun san da haka da baki wahalan hada baki da matar sojs tashigo abin da bai shafe ta ba.
Ya fice ban sake jin duriyan shi ba sai dare sai gashi ya dawo min a cikin maye yana ta tsuki burutsun shi a gidan.
Ina daki ya samay ni a haka na dan dago ina kallon shi naga ya nufo ni gadan gadan sai na fashe mai da kuka don na san halin fitinar shi sarai ba imani ne dashi ba.
Yace a cikin maye ke ke may nene haka ?
Na yun kura na tashi da kyat ina cewa don Allah yaya kayi hakkuri wallahi ban iyawa banda lafiya ne.
Na gaya maki zan maki wani abune kawai kawai yana inda inda ya kasa fadin abinda zai fada din ya juya yana suruntun abinda banji ba ya fice dakin.
Na lumshe idanuwa na a hankali ina sauke ajiyan zuciya ganin ya fita natashi na rufe kofan dakin nawa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
🧕🏿1️⃣9️⃣🧕🏿
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE.
Kwanaki goma sha uku da aukuwan wanan lamari yana zaune a falo ya harde kafa yana shan ruwan kwalba da sigari yana sha yana yamutsan fuska kamar an sashi dole ya sha.
Na fito daga daki rike da cup a hannu na ban san yana zaune wurin ba sai ganin shi nayi yana korawa.
Da sauri na wulkita zan juya dakin da nafito ganin haka yasa shi mike a ida yake zaune din ya nuna ni da hannu.
Ke ban san sau nawa zan fada maki cewa idan ina zaune kika gani ki daina gudu kamar wata mara gaskiya dake.
Nikan ban masan yana yi ba don na dafe bakina da hannu daya kar amai danake ji ya fito mun a falon.
Ganin yanayin da nake ya dakatar dashi ga fadan da yakeyi din ya kafa min idanu yana kallona a cikin zargi.
Yace Safiya ciki gare ki ne ko may ban sani ba don tun ga kwanaki naga kina wanan aman na tsiya.
Nikan ban ma san yanayi ba ina tsugune na dafe kaina sai kakarin amai da nakeyi a ban dakin .
Hakkali a tashe ya sake magana da cewa kefa nake tambaya na dago da kyat ina cewa cikin yanayin ciwo warin taban nan ne ke wahal dani.
Ya ja tsuki ya juya yabar wurin dakin shi ya shige da bacin rai bai fito ba haka nima ban fito ba na kara dunkulewa cikin dakina.
Kwana biyu baya gidan ban san ina ya shiga ba ga komai ya kare min don haka na shirya zuwa gidan maman biyu.
Yanayi na kawai ta kalla tasan ban jin dadin jikina yace wai ko kunje asibiti kaina girgizamata kawai alaman a a.
Safiya kamata yayi ki fito ki sanar dashi zancen cikin nan amma ba wai ki boye ba don ba zai yuyu kibar ciwo a jikin ki ba don ciki ciwone.
Nace to Anti shidin ne almarin shi har yanzu ba canji kin ga tun kwanaki ya gane bana jin dadin jikina amma don rashi imani yau kwana biyu kenan baya gidan kuma ban san ida ya shiga ba.
Idan ma yana nan ba wai kyaleni zai ba don banda lafiya haka zai afka min kamar dabba don rashi imani irin nasa.
Tace ke Safiya kar in sake jin kalman dabban nan a bakin ki, karki manta shifa mijin ki ne na sunna.
Nace anty ai ba fadina bane, Annabi nefa ya siffanta duk mai irin wanan dabian da daba, sannan sai kinga irin wahalan da yake bani abin har da mugun ta yake hadawa.
Wai in mun hana shi bin mata banza waje ni zanji a jikina tunda nace ina iyawa.
Sai na soma mata kuka tai saurin cewa may ye haka kuma safiya ko so kike ki tada min hankali ?
Ina kuka nace wallahi anty ba haka bane wallahi ni kadai nasan abinda nake ji ajikina yanzu haka idan indan ina tafiya jire nake gani marana kuma kamar zai tsage min biyu nake jinsa sanan na kasa sa komai a baki na komai naci sai ya dawo min.
Tace ya zama dole ki dada masa idan bai dauki wani mataki ba ki zo kifada min kina jina ko don ba a zama a duhu haka kina jina ko.
Nace naji zandan kwanta kozan samu barci yanzu haka jiri nake gani tace inshiga daga ciki don kar a dameni nan falo na kasa barci.
Na samu nayi barci sosai sai wajen uku na rana na farka daga barcin naji dadin jikina matuka don naji kaina yabar sarawa.
Nai sallah naci abinci sannan na fara shirin komawa gida ta harhado min komai da zan bukata zakace ko uwatace ko wata yar uwana ta jini abinda take min.
Kusan karfe hudu da rabi na dawo gidan na danji saukin jikina ko banza nadan samu warwarewan zuciya na dana dan samu idan da na tsiyaye.
Har na dawo na dan gyara gida tunda na samu karfin jikina bayan nai sallah ishai ina kwace saman carpet ina kallo ya dawo gidan.
Kai tsaye dakin shi ya wuce bai fito ba yan yai wanka ya fito saye da guntun wando da singlet sai taba a hannun shi.
Bai same ni a falo ba yayi zaton ina dakin girki ne sai da ya saurara sannan yajiyo kakarin amai daga daki na ina cikin ban daki.
Ya mike da sauri zai bini sai gani na fito ina tafiya kamar wacce tayi makwanni cikin ciwo ya dinga sata kallona har na dawo inda na tashi saman carpet na kara kwantawa.
Na daure na dago kai a hankali nace dazun ka dawo ina gaisheka baka amsa min ba ido kawai ya tsura min baiyi magana ba.
Sai cewa yayi tashi muje chemist a duba min ke ban yarda wanan uban amai da kike min haka ba cikin