Showing 33001 words to 36000 words out of 269010 words
Nace may kika gani tace gani nayi dai bata kaunar ki koda yake hajiya ai da kowa zata kwasa indan ya taba mata dan lelenta.
Murmushi nayi mata kawai tace tana masifan son shi cikin yaran ta gashi dai yana aiki kuma yana samu amma bata jin kyashin kashe mai kudi.
Nace aidon su take nema ko tace wallahi yana da hanyan samu sosai amma yan matan shi basu bari ko wanan gidan da mota da ya saya sai da dabara ya saye su.
Na dauka da yai aure zai daina amma da yake dan duniya sai abin da yai gaba ga abinda yake yi.
Nan nake ji wai ai da dawata yake zaune a gidan sai da hajiyan tayi da kyat ta raba su da kamar sun rabu yanzu kuma sun dawo sun dinke wuri guda da ita.
Nan tashiga bani hiran abokiyar shashan shi din da irin rayuwan da sukayi a baya dama wanda suke yi yanzu din har nagama mata kitsa tana min hiran shi ne.
Mun gama ta ciro kudi ta bani ban karba nace ta barshi sai idan ta sake dawowa tace a, a karba wallahi idan kika soma da haka zakita aikin banzane wa mutane nan garin neman kudine ba a wasa da neman kudi.
Naimata godiya taimin alkwarin zata sake dawo idan an kwana biyu na rakata ta tafi sai da ta wuce na duba kudin nayi mamaki don har dubu daya tabani.
Ina ta murna na shiga daki naje hadawa da wanda na boye sai naga ashe dubu uku na bashi na boye bakwai.
Yanzu ga shi taban daya sun tashi takwas taban shawara na sayo kayan yin kitso don akwai wa yanda zata turo min.
Tun ranan da tazo kamar ta buda min hanyane na yin kitson na dinga samun customers mssu zuwa ganin haka ina yi a boye sai na sheda mashi don karya zo ya sani ya hauni da jidali.
Baice komai ba sai ke kika sani kardai ki bata min gidana kan wani kitso naki na banza can.
Don haka idan sun zo muke fita ta waje muyi kitson basai mace ta shigo gidana ba mun bata mai gida.
Wata rana wata mace tazo da diyan ta sai suna neman ruwa sai da aka tafi wani gu aka sayo mata sai take ban shawara na dinga saida abin sanyi mana.
Wanan shawaran yai min dadi sosai tun wanan ranan na fara sayar da ruwa sai nai shawaran ko na dinga zobo sai inayi dashi da wasu yan kakanan drinks ina sayar wa.
Aiko sai abin ya karbe ni matan hausawa harda kumshi nake masu mai zane take sunana ya fara dagawa.
Hankalina ya dan fara kwantawa koba komai dai ina samun abokan hira har ina dariya sai dai in sun tafi na koma dip.
Wata rana na gama kitso na gyara gida na dora girki gap da zan gama na shiga wanka koda nafito abinci yayi na kwashe.
Ina zaune a falo ina cin abinci sai gashi ya shigo ina gaida shi da dawowa ya amsa ciki ciki ya wuce dakin shi.
Ya fito ya zauna kenan wayan shi yai kara ya dauka zaune nake a takure a falon ina gudun in daga yace min munafuka.
Sai na dake na zauna a takure a yadda na fahinci wayan da yake da mace yake magana amma ko yaji darr dan ina zaune a wurin.
Daji lalashinta yake yi don a yadda suke magana hakkuri yake bata ita kuma sai masifa take mai a wayan.
Zuwa can ya mike zai fita sai na sasauta murya na nake cewa kayan miya sun kare a gidan na gobe ya rage kawai da zanyi.
Ya juyo a wullakance ya dube ni yana cewa ina kudin da kike samu a wurin kitson naki ki fitar ki saya mana.
Ya fice ya barni ina mai binshi da kallon mamaki don tunda kayan da nazo gidan na sama ya kare idan nai mashi magana sai ya hauni da fada.
Gashi kuma ance kudi yake samu sosai a wurin aikin shi amma baya nuna yana dashi sai yaga dama yayi.
Nidai na fahinci anyi sallah na mike zuwa yin sallah nabar falon ban fito ba ina shirin kwaciya ne naji dawo wan shi gidan.
Na dan tsaya inga da may ya dawo min a cikin mayen ne ko a birkice naji shigowan shi na mike na fito falon inda yake sai naga yana shigowa yana dariya.
A zatona waya yake yi sai naga ashe ba waya bane yana magana ne da wata da suka shigo gidan tare.
Yana dago kai ya ganin ya hade fuska tare da cewa a fusace ke kuma may kikeyi anan baki kwanta ba ?
Yarinyar da suka shigo da ita gidan tana wani taunan chewgun kas kas tana harare hararen ko ina na gidan.
Naji tace wanan ne dama matar taka ashe karamar yarinyace haka no warder kake gudun mutane yanzu
Ta kalle ni sama da kasa sai tace dashi muje don Allah karma ta kwanta mana ita ta sani tai gaba ya juya ya bita a baya.
Suka barni tsaye a wurin imani ya kashe ni may yake nufi kenan karuwa ya dauko min a gidan ko may ?
Jin sun rufo kofan daki ne nadan zabura na dawo cikin hankalina dakyat naja kafana na koma daki.
Tunane nakeyi wanan wani irin bariki ne haka karuwa har cikin gidan tazo ta wuce ni ta shige daki ita da mijina ina tsaye.
Da kyat naga safe don banyi barcin kirkiba a gidan da safe ban fitoba don haka ban dora girki ba a gida ko gyaran gida ban fito nayi ba.
Sai zuwa can ya kwala min kira daga falo saida ya kirani sau uku na amsa mai na fito falon ina saye da hijjab dina har kasa.
Ya kalle ni a wullakance yace dani ina abin karyawan mu banga kin aje min ba nace a sanyaye banyi ba.
What ya fadi da karfi nace banyi na sake fada mai saboda may zaki ce baki dafa min abinda zanci ba.
Cikin dakewa nace ita wanda ta kwana gidan bata dafa maka bane koba mace bace da baza ta dafa ma ba.
Ban san ya iso inda nake tsaye ba sai ji nayi ya buge min baki kub da nashi basan lokacin da na dafe wurin ba.
Ya daga hannu zai kara kai min wani marin sai ga ta ta fito daure da tawul a jikin ta iya cinya tace a, a marta koma ta dafa ba iya ci zanyi ba wanan kazaman yarinyar ba zan iya cin girkin ta ba.
Ta jashi zuwa cikin daki tana wani kariraya tana kwanta mai ajiki suka rufe kofa dakin garam ina wurin a tsaye.
Na sauke ajiyan zuciya a raina nace lalle yau na ga iyakar barikin da nake ji ana fada anayi a lagos na ganshi a wurin wanan bawa shine giya shine taba gashi kuma ya buga ga dauko karuwa kwana a gidan mu na sunna.
Ina jin sun gama watse war su suka fice a gidan da ihuce ihucen su da tafawa a tsakanin su.
Nace shashu banza kawai a haka zaka kare ba aga farar ka a gida ba sai gun matan bazan za suna fita sai ga yaya saadu ya shigo gida.
Natare shi da mutunci muka gaisa dashi yake tambaya na yaya gidan na amsa mai da lafiya kalau.
Sai yake tambaya na yanzu abubuwa sun yi sauki a tsakanin mu ko sai nai murmushi kawai nake cewa dashi babu komai yaya.
Ya ce a, a Safiya kada ki biye min komai ni dan uwanki ne nasan kuma halin mijin ki sarai da rashin mutunci do haka in baki fada min ba wa zaki fadawa.
Sai idanuwa na suka ciko da hawaye a lokaci guda nace yaya komai na nan a yadda ka san shi saima abinda ya karu.
Yau ma da wata mace suka kwana gidan a gaban ta yai min rashin mutunci don naki dafa masu abin karyawa.
Hakkuri ya bani ya dade yana mun na siha ina ta fada mai irin matsalolin da muke samu dashi a gidan.
Yana bani hakkuri tare da fadin sai na hada dayi mashi addua don addua baibar komai ba in kuma yi kokari in kawar da idona ga abin da yake yin don ko na ce zan fada wa iyayyen mu ba yarda zasuyi da ni ba.
Da zai tafi yakawo kudi ya bani yana cewa na rika in dinga sayen abinda zanci basai na tambaye shiba kar yaita duka na a banza.
Nace mai akwai kudi wanda na tara do yanzu kitso nake ina samun kudi yace tona kara kawai dasu.
Yai min alkawarin zai saya min fridge don sana,an zobon da nakeyi ya bunkasa sosai naji dadi ina ta zuba mai godiya mukai sallama ya wace.
Da ya tafi na kirga kudin sai naga har sha biyar ne cif din su banyi sanyi a kafa ba na shirya na shiga yar kasuwar uguwar mu na sai kayan amfani na dasu da abinda zan dan rika ci da rana.
Ashe da yabar gidan gidan su ya koma wurin mahaifiyar su ya ke fada mata duk irin abubuwan da dan uwan nashi yake min.
Sai ko ta hau fada da cewa dama tsiyan dan tallaka keman bai iya samun wuri ba ta tsamoni cikin wahala tasani ga rigan mutunci ina bidan in tona masu asiri.
Da nake cewa yana sha, shan ya hana ya kyautata min ne duka kuma in banyi mashi laifi ba ai ba zai duke ni ba , a gidan mu wani irin wahala ne bana sha nazo nan a saka ni cikin rigar mutunci shi zai ma danta sheri.
Yace mummy yarinya ga fa diyan dan uwanki ne halal malan aka dauka aka baki badon taso ba ko uwar ta taso ai kama yayi ki tsawata mashi yadaina shigo mata da maye da matan banza baki goyi bayan shi ba haka.
In tana ahan wuya a gidan su nan ai aurene ya kawo ta kamata yayi ta samu sayin rawa ta huta ba wahala irin haka ba.
Tace to ubana dama ai ka saba min fada sai kayi ita kuma ta zuba ruwa a kasa tasha tunda ta hada ni da diyana fada.
Sadiya dake gefe tana saurare tace mummy ai gaskiya yaya ya fada gaskiya abinda yayan ke wa Safiya baya kyautawa idan mu akaiwa haka bafa zaki ji dadi ba.
Harara ta watsawa Sadiya din tana cewa ai duk kuna da bakuson dan uwan ku da alheri daga yarinya taimai kake kun dauka kun haye ke nan kun yarda da abinda ta fada.
Saadun yace mainene daga ciki kake wanda ba halinsa ba cikin abinda ta fada din ina duk halin da ta fada kin sani yana yin su sarai.
Nan dai yaran suka barta tana ta fada tana fadin ai zata je gidan zamu hadu gobe bazan kara fadawa wani sirin mijina ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,
🧕🏿🧕🏿1️⃣1️⃣
INA MAI BAKU HAKKURIN RASHIN JINA KWANA BIYU WUTAN MU YA LALACE
YAR UWA IDAN KIN FITAR MIN DA NOVEL DON KAN KI KE KI SANI DON KIN SAN DAI HAKKIN WASU NE.
Ina duke ina wanki bansan hawa ban san sauka ba sai jin bugu nayi daga baya na sai da na kife a jikin roban da nake wanki din.
Bai hakkura ba ganin na fadi kasa ya kara kai min duka bazan iya kare kaina ba na fadi kasa gaba daya yana ta duka da zagi.
Sai da ya gaji don kanshi ya barni nayi ligis a kasa yashe ban ko motsi ruwan da nake wanki duk ya zube min a jiki na yana huce yake fadin.
Baki ga komai ba idan kin ce magana zaki dinga dauka kina kaiwa gidan mu shi wanda kika fadawa yazo yai maki maganin abin na gani mana.
Mata yanzu ma na fara shigowa dasu gidan nan gidan ubanki ne ko gidana da zaki kafa min doka akai.
Yar iska jiki matan da nake bi din basu fi min ke ba, ke har mace ce may za a samu a gare ki banda wahala.
Har ya shige ciki ya fito yace ban ga daman kawo abinci ba ki aika wa uban ki mai dakunanen hula ya kawo maki in ya mayar dake wata tsiya.
Yar iska nida gidana har kina sin kafa min doka nakawo mace ki hanani naji dadin da nake so idan kin isa.
Nikan zafin bugu sai wani gumzi nake yi kamar raina zai fita ya shige na dade wurin ko kafana bana iya dagawa a lokacin.
Da kyat naja kafa na shiga dakina ko ina sai ciwo yake min don zafi da cowo kuka nake ina tunanen rashin imani irin na yaya Ahmed.
Bai kara bi ta kaina ba sai shaye shayen shi yake a cikin falo ina jin shi warin giya da taba har dakin da nake ciki.
Sai dare naji yana rufe gida ya fita da kyat na ja kafana zuwa falo nan na samu yai baja baja da kayan da yai shaye shayen wurin.
Kitchen na nufa na dan hada ruwan liptop na don a lokacin shi kadai nake iya saqa cikina ga wani irin zazzabi ya na neman rufe ni.
Ranan tunane kala kala nayi gadai kudi a jiki ina son gudu in koma gida don dai na san motan zuwa arewa bai gagara na zuwa.
Amma kuma nasihan Ummi yana min yawo a raina da tace dani yar nan komai wuya komai dadi ki natsa kafan ki a dakin ki wuya baya kashin bawa.
To amma kuma a haka ake son na zauna cikin wanan irin ukuban babu dadin rai ko yaushe sai fitina kamar ankawo mai jaka.
Nidai tun zuwa na gida ba zan ce ga rana daya wanda naji dadin zama da shi ba daga ni har shi zamane na dole muke yi da junan mu.
Washe gari abin yafi na gare ne duk fuskana ya kumbure ga hannu da kafa ban iya daga wa ko kadan don ciwo.
Ina cikin wanan halin amma ya saka kida yana tashi ina jin sautin na shiga min har cikin rai na ba halin in magan ta.
Ganin da yayi kayan wankin da na jika ya kwana ya wuni yasa shi shigowa dakina a fusace yana cewa ke don ubanki kayan nan da kika jika suna wa mutane wari baki kwashe su wurin nan ne.
Sai ya samay ni cikin wani hali banko san ya shigo dakin ba lokacin tsayawa yayi a kaina yana kare min kallo sai kuma ya juya ya fita.
Ko ina nawa ya hakke ya kumbura dan bugu da ciwa gashi ba mataimaki yan kitso na sai zuwa suke suna tafiya.
Wata boyar Allah da nake kira mama biyu don tana da tagwaye tana kawo su kitso wuri na tai karfin halin fadowa har cikin daki na.
Sai da ta dan yi ihu don ganin halin da nake ciki tace dani amarya waya maki haka ko hatsari kika yine wai.
Na bude idona da kyat ina kallonta dishi dishi nace buguna yayi tace amma mijin nan naki baida imani ita na samu ta taimaka min har na da wanka .
Ta dan sayo min abinda zanci da dan magani na sha tai ta jamashi Allah ya isa yafi a kirga ta shirin tafiya ne sai ga yaya saadu ya shigo gidan yace yazo ya sallamay ni nao zai tafi.
Hankali yace bai kwanta ba ga yadda ya barni ranan sai kuma yazo ya tarar da abinda ya faru dani.
Matar take kara yi mashi bayanin halin da ta samay ciki aikuwa bai tsaya ba ya juya zuwa gidan su kai tsaye wurin mahaifiyar su.
Ya je ya sameta yake fada mata irin taasan da yayan nashi yai min maimakon tai fada sai cewa tayi fada kota tausaya mashi sai ta fara fada dani tana cewa.
Ai maganin ta kenan yarinya bata da kunya sam ga sa ido ga abin da bai shafe ta, gunma da yai mata dukan tsiya goma bata karawa ai.
Ya ce mummy na fada maki yarinyan nan tana cekin wani halin a yanzu idan ba zaki dauki mataki ba ni zan dauka don wallahi zanyi karashin gurin yan sanda akan zai kashe yarinyar mutane.
Da sauri tace dashi dan uwan naka zakai kara har kana fadi da bakin ka akan wata Safiyan ce ?
Yace ita din ba yar uwar mu bace mummy da zaki ce hakan wa take dashi a garin nan bayan mu ka wata sani in bamu ba.
Waya ta jawo ta kira wayan Ahmed din ya amsa mata a kadarance da cewa mummy aiki nake yi fa banson kira yanzu.
Tace kazo ga Saadu nan ya zo ya tayar min da hankali akan makiran yarinyar nan safiya wai ka mata duka har ta kwanta kuma baka kaita asibiti ba.
A cikin fada ya na daga sautin muryan shi yace