Showing 243001 words to 246000 words out of 269010 words

Chapter 82 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13328

a fuskana tare da fadin sannu da zuwa uncle hannuwan shi ya bude da sauri na shige ciki .
Yana rike dani muka shiga gidan bai nufi dakin shi ba sai da ya tafi yaga Abba dake barci na wuce na bude mai daki tare da kunna naurorin dakin na hada mai ruwan wanka.
Kayan shi ake shigowa dasu gidan daya dawo dasu sun gama na rufe gida tare da yi masu sai da safe.
Ya dauko yaron ya nufi dakin shi dashi a kafadan shi nan na gama komai nabi bayan su nima tari naji yana yi sai muryan shi daya dan shake bai fita sosai.
Uncle baka jin dadi ne dan murmushi yayi yana kara gyara ma yaron shi kwanciya da kyau ya juyo gareni yana fadin .
Mura ne ya kamani kin san yanayin sanyi da ake yi yanzu acan ya fara kokarin cire kayan jikin shi na juya na fita zuwa kitchen inda na hada mashi shayi da cita da kanunfari na kowo mai dakin har lokacin bai fito daga wanka ba.
Bakin gado na zauna ina jiran shi koda ya fito yana goge ruwan dake jikin shi tari ya kama yi a lokacin tashi nayi na fara tsiyaya mashi ruwan tea din dana hada mashi a kofi.
Ya gama yasa kaya a jikin shi ya nufo inda nake jiran shi da cup din tea din da nake dan motsawa a hankali cup din na miko mai bayan naga ya zauna a saman gadon.
Karba yayi yana tari sosai hankali na ya daga sosai ya dan kurba kusan sau biyu yace na kwana biyu ina tarin nan tun acan.
Sannu nayi mai nace yi kokari ka shanye tea din zai taimaka maka ka samu barci da sauki don wanan tarin dake damun ka.
Ido ya dan lumshe kadan yace yaya kibaro mutanen gida nace duk suna lafiya suna gaida ku sun ce kuma ai masu godiya sosai.
Da akai may yana miko min kofin daya shanye tea din na aje a saman dan drower dake gefe na hawayayi saman godon ya dan dukule a wuri daya kamar mai jin sanyi.
Hankali ya tashi ga yanayi da naga yake ciki sai dai yana kokarin kwantar min da hakali da fadin ai murna ne kawai ke damun shi a lokacin.
Ki kwanta yace dani haka na kwanta a sanyayye tare da tausayin kan mu ga halin da muke ciki na rashin lafiya a jikin mu .
Ni yanzu in uncle ya mutu ya barni yaya zanyi da rayuwana jamma, a da sauri na kawar da wanan tunanen a raina tare da kai hannu na na dan shafa Abba dake barci a gefe na.
Ina sauke ajiyan zuciya hannu na guda nakai a saman goshin uncle wanda idon shi ke a lumshe a lokacin.
A haka barci ya dauke mu dama karfe uku na dare yayi ko haka yasa mu makara da safe ba laifi ya samu barci kamar yadda nace mashi din zai samu.
Washe gari ban fito daga dakin uncle da wuri ba don makaran da mukayi yan matana har sun fito sun zauna falo kin san dan kauye bai barcin safe shi.
Sai raba ido suke suga inda zan fito a gidan har Nura ta shigo ta fara aikin ta sacen na fito ganin inda na fito ina sabale da Abba daya tashi daga barci nayi mai wanka acan.
Da sauri suka taso suna gaida ni da kwana na amsa masu cikin dadin rai ina fada masu baban Abba ya dawo jiya da dare .
Sun nuna farin cikin su a hakan daki na shiga tare da kiran su muje dakin nawa a lokacin a saman gado na aje Abba na juya dauko mashi kaya in saka mashi.
Hindatu ta dauke shi tana mashi wasa maimu tace anty na zata kin fita ne da ban ganki ba nace aini maimu ban faye fita unguwa ba sai idan ya kama.
Mun gama muka fito falo bayan na shirya suna zaune suna jirana a dakin sai da nagama tsab muka fito lokacin had Nura ta hada abinci a table na dan duba nake fada mata dawowan uncle tea din jiya na kara hada mai tare da bude fridge na dauko hadin tsoho na zuba a cup na nufi dakin shi.
Na samu ya tashi yana zaune yana duban wasu takardu a hannun shi nace uncle ina kwana yaya jiki da gajiyan hanya.
Na aje kayan kafin ya amsa na juyo na dan kai mai kiss a saman goshin shi yace da sauki madam yaya gida yaya bakin ki kuma ?
Suna lafiya na bashi amsa ina zama kusa dashi nace yaya jikin naka don yanzu na kulla a raina duk fushin shi ko shirun shi zanyi kokari inaga na kara kawo kusanci a tsakanin mu.
Ko zan samu in rage mai yawan saurin fushi a rayuwan shi wanda ni kadai ne a yanzu zan iya kawar mashi da hakan.
Na fada masu ka dawo suna can suna murna na barsu suna karyawa a falo yanzun haka.
Yace akwai kaya cikin kayan da na dawo dashi ki duba ban samu wani lokacin tsaya yi maku tsaraba sosai ba don yanayin jiki na.
Uncle aimu kullun cikin tsara ba muke ina kai hannu na saman cup din maganin tsoho daya bamu musha.
Dauka nayi na kurba na kara kurbawa sosai sai na mika mashi don kawar da zargin wani abu a ranshi duban cup din yayi yace wanan kuma may nene haka ?
Magani ne kasha uncle yana da kyau sosai wallahi tsoho ne danaje ya sama muna don yanayin jkkin mu sai dai ban fada mai ko may ye ba don kada yaji kazantar sha.
Amsa yayi ya kurbe duk ya aje cup din tea din na mika mai yasha nace irin na jiya ne na hada ma naga ka samu saukin tarin jiya da dare.
Kwana kikayi ke nan gadina ashe naji ya fada nace ba dole ba baban mu ya dawo gida ba lafiya ina naga kwanciyan hakalina.
Murshi yayi ya karba ya fara dan spping din tea din a hankali yana lumshe ido har ya shanye ya dan yi gyaran murya nasan cittan ne ke aikin shi a lokacin.
Tashi muje in gaisa da bakin nawa yace min bayan tea din ya dan fada mai wurin na dan gyara kafin mu fito na kwaso kayan da na kai mashi tea din zuwa kitchen.
Suna zaune sai wasa suke ma abba yana dariya suka ji muryan shi a bayan su yana cewa wasu kauyawa ne haka a gidan namu ?
Juyowa sukayi suna gaishe shi ban fito kitchen din ba sai dana dauraye kayan dana shiga dasu din don rage ma Nura aiki.
Na fito na samu yana hira dasu cikin natsuwa yana tambayan su aji nawa kuke yanzu aji uku maimu ta fadi yace kaji ba kauya ba haka zaki ce ba .
Sai hindatu tace primary three yace a a ashe hundatun dai ta waye tafi maimuna jin turan ci ke nan nace ko go and come back ba wanda ya sani cikin su.
Anty munaji fa ana koya muna maimu tace nace makarantan da sai an kora ku kuke zuwa yaushe kuka tafi har ku iya wani abu.
Shigowan yaya saadu ne ya katse muna hiran ya shigo yanayi mai sannu da zuwa sun dan gaisa yace da cashiar suke haka yasa uncle fita.
Don bai yarda a shigo mashi gida kamar yadda sauran maza suke amincewa da kowa ya shiga masu gida kai tsaye.
Haka a kidojin shi suke kamar mutumin da shi yawan tsare iyali da sa ido akan mace ga komai da takeyi fitan su falon mukaci gaba da hiran makaranta da yan kanne na .
Yaya Saadune ya dawo yana fadin ashe maigida baijin dadin jikin shi ne ko da ya dawo yanzun naji yace likitan shi yazo ya duba shi.
Nace yace sanyi ke damun shi mura ya kamashi yace yadai boye maki amma ai ke ma kinga ya ramay sosai ciwo yayi sosai acan fa.
Wani iri naji a raina sosai a lokacin nace nima nayi zargin haka yaya yadda naga ya ramay sosai wallahi.
Yace kafin in gama tunane yace ki bani takardu a saman gado daya aje tashi nayi zuwa kwaso mashi takardun a dakin shi.
Bayan na dauko na kai mashi na koma dakin don hada sauran takarcen daya dawo dasu daga tafiyan nan naga takardan asibiti a ciki na dauka na duba abinda na dan fahinta ciwon nashi ne ya tashi mai acan har ya kwanta asibiti.
Shine kuma uncle zai boye min hakan idan wani abu ya faru dashi fa fiye da funanen shi sai banji dadin yin hakan da yayi min ba ai ba a boye ciwo ga masoyi nace wa kaina.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/21/20, 9:58 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , , , ,


🧕🏿8️⃣2️⃣🧕


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

NOVEL DINA NA KUDI NE IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA NA BARKI DA ALLAH KE/KAI MAI FITAR WA HAKIN AMANA YA HAUKAN KU DON BAN YAFE BA.

Wasa wasa sai da uncle ya share sati daya a gida yana jinyan jikin shi wanda yawan jigilan da yake yi ya jawo mashi hakan.
Dani da yan kanne na dana dauko daga gida muke jiyan shi ida ya hana mu fadawa ko wani dan uwa nawa da shi.
Muna cikin sulilin rashin lafiyan uncle duk da yaji sauki zuwa yanzu ya dan samu sauki sosai sai dai bai fita har yanzu.
Labarin sakin anty ya zo muna inda ake fada mashi faruwa abin yau kwana biyu ke nan waya yakeyi ina sauraren shi hankalina yayi matukar tashi dajin abinda ya furta din a waya.
Take na fara maimaita innalillahi wa inna alaihim rajjiun a fili har ya gama wayan ya dago kai nace da sauri uncle anty na daddy ya saka.
A hankali ya sauke ajiyan zuciya yana fadin innalillahi shi ma cikin tashin hankali yake maganan nace may yayi zafi haka uncle ?
Tace wai kudine ya hadasu fada ya shigo da kudin aikin su gidan washe gari zai fita dasu sai ta taba yayi yayi ta fito mai dasu taki shine ya kawo masu sabani.
Nakai zaune don tsaye nake dama akan shi na dauko mai waya a daki sai na tsaya bayan kujera daga bayan shi.
Nace haba anty wai may takeyi da kudine haka don Allah kudi dai tana samun su mijin ta kuma tana samu a gare shi.
May zai sa ta daukan ma daddy kudin shi kuma har abin yakai ga jawo masu sabani haka ina magana ina girgiza kaina a hankali cikin damuwa.
Nisawa uncle yayi tare da fadin nima tunanen da nakeyi yanzu kenan a raina don son kudin maimuna yayi yawa wallahi.
Wanan labarin mutuwar auren anty ne ya kashe min jiki yinin ranan haka na wuni a lalace ina son kiranta ban san amsan da zan samu a gare ra ba.
Washe gari mummy ta dawo daga wurin yaran ta da taje gani mun yi murnan dawowan ta sosai a ranan gidan ya koma muna happy house don kowa na nan.
Nan su maimu suka koma hira da mummy dawuya su fito falo wurin mu suna wurin ta koda yaushe.
Har uncle ya fara fita aiki bai kara magana kan su anty ba kuma gashi ina son in tamabaye shi halin da ake ciki da zancen na su.
Ranan na kira hajiya baaba ina gaida ita bayan mun gaisa mun dan taba hira da ita take cewa dani sai kuka ji labari ba dadi rabuwan maimuna da mijin ta.
Nace wallahi hajiya tace manya sun zauna akan zancen ya nuna masu sam ba zai sake zama da ita ba kuma yanzun haka aure zai yi.
Don su uwa sun hada shi da wata nan abujan har anje tsayar da magana akai mutumiyar adamawa ce wacce ya samu din.
Inna lillahi nake iya maimaitawa a bakina nace hajiya yanzu shike nan su rabu da anty din tana ina yanzu hajiya ki bashi hakkuri mana da kan ki tunda daddy yana jin maganan ki sosai.
Murmushi naji tayi tace kaiyya safiya ai labarin ba dadin jine wallahi tun da abin har da zargi a ciki sosai.
Munyi sallama ina tunanen maganan hajiya din da mukayi data ce har da zargi ni dai iya sanina shine anty tana da yawan ibada kuma banga wani alama na wanan halin a gare ta ba tunda muna fita tare wani lokaci.
Da dare da uncle ya dawo nake fada mai munyi waya da baaba har nake fada mai yadda mukayi akan maganan anty din da ita.
Yace koma may ye ai zalaman ta zai iya sawa suyi mata hakan tunda ita ta yarda dasu a marairaice nace uncle kasa baki ga maganan nan don Allah.
Yaran nan nake tausayi wallahi yace yanzu ke duk abinda sukayi maki baki tsane ta ba saboda su fa ta gujeki har abada take fushi dake.
Nace uncle ba a duban wanan domin tayi min a rayuna yadda ba zan taba mantawa da ita ba a rayuwana.
Yace yanzu yaya kike son in yi ke nan nace uncle baki ya kamata kasa a zancen anty uwa yar sherin matace sosai wallahi komai suna iya yi din su kuntatawa mutum don ba tsoraan Allah garesu ba.
Shiru yayi na dan wani lokaci tare da ci gaba da cin abincin dake gaban shi har ya gama idona yana kan shi don son jin may zaice akan maganan.
Bayan kwana uku da mukai waya da hajiya ne sai ga anty taje gidan nata duk cikin son a shawo kan daddy din take fada mata ai munyi waya nima abinda na fada mata ke nan.
Tace zatayi wani abu akan zance zata kira daddy din su zauna dashi koda tafita tunane takeyi ashe safiya har yanzu bata fita zance na ba har zata iya bada hakkuri akan magana na.
Haka yasa ta shirya washe gari sai gata ta iso abuja a lokacin mu kadai ke gida uncle yana wurin aikin shi.
Ina daki hindatu ta shigo tana ce min anty wai kinyi bakuwa tana falo nace wacece tazo tace nima ban santa ba anty na dan gyara na fito taba da baya don haka ban gane ta ba.
Nace daga bayanta sannu da zuwa ta nata bin gidan da kallo ko ina a lokacin ta juyo da sauri tana amsa wa ganin itace da sauri na karasa wurin ta ina fadin lah anty sannu da zuwa.
Yanzu kike tafe ashe duk na rude da ganin ta nayi kamar zan zauna sai kuma na nufi kitchen na hado mata abin sha.
Bayan na aje na zauna ina gaishe ta ta amsa min cikin sanyin rai ba kamar yadda take amsawa mutum da izza ba.
Nan dai nace anty kisha ruwan mana tace bari Safiya ashe kin ji abinda ya faru tsakani na da baban su yan biyu da yan uwan shi.
A sanyaye nace da ita naji anty abin baiyi dadi ba wallahi hankalina a tashe yake akan maganan tun ranan dana samu labarin.
Amma anty uwa basu kyauta maki ba anty duk irin yadda kike dasu kike kyautata masu haka zasuyi maki sakaiya dashi kuma.
Safiya bari wanan zance yanzun ai duniya ta koya min darasi sosai wallahi wai har uwa ke cewa daddy maza nake bi idan bai jan shi kuma ya yarda.
Could you believe that safiya wai uwa ke fadan haka kuma aka yarda ita ba a ce mata haka ba sai itace zata fadi haka a kaina a yarda.
Nace anty kiyi hakkuri don Allah tace ina sulaiman yana gari ko na kirashi bai dauki waya ba har sau biyu da abin ya faru.
Wayana na dauka na kirashi ina fada mashi zuwan ta yace tana ina nace gata zaune a gida wuri na yace yana zuwa ta kura min ido tana kallon yadda nake wayan cikin ladabi kamar yana gabana a lokacin.
Na sauke ajiyan zuciya nace anty wai yana zuwa ki sha wani abu don Allah ki rage wanan tunanen haka bakyau komai zai zo da sauki da yardan Allah tace safiya kina ganin hakan zai yuyu yadda daddy ya hau din nan ?
Nace anty babu abin da ya gagari ubagiji ai idan ke ce da gaskiya Allah bai basu ikon samun galaba akan ki dayardan ubangiji.
Tayi ajiyan zuciya ta dan tsiyaya ruwan ta kurba tasha mukaci gaba da maganan ya dan dauki lokaci sai gashi ya shigo gidan .
Yace madam ashe kina tafe tace ba dole ba na yanke shawars inzo wirin ku ne ku taimaka min ga abinda daddy ke shirin yi min.
Yace saki nawa ke tsakanin ku ina jin haka sai na mike uncle yace ina zaki kuma ana magana kin kuma tashi.
A marairaice nace dashi zan baku wuri ne da yace ai wanan maganan ta shafe ki tunda ta shefi anty ki ki dawo ki zauna ya fadi cikin daure fuskan shi.
Da sauri na dawo na zauna tace saki biyu ne don da cen da dadewa ya taba sakina sai kuma yanzun da ya kara daya.
Nan dai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login