Showing 111001 words to 114000 words out of 269010 words
Da yamma aka fitar da tsaraban da yazo dashi wanda tufafi ne sai kayan ciye ciye irin na kasa shen ketara yazo dasu wannan kan an zube su ne kowa ya ci ya sha iya shan shi da ci.
Daki na koma ina kallon tsaraban ina mamaki dan zuwa na gidan su na karu da abubuwa da dama na rayuwa.
Na tuna da iyayyena da yan uwana dake zaman ukuba saboda talauci kullun ana ganin laifin juna a tsakanin zama tausayin halin da gidan mu ke ciki ya kamani.
Na wani fitina nan har da talauci ke kawo shi ma in kowa na dashi ai ba mai kallon halin da dan uwa ke ciki kowa tashi ta isheshi ma.
Daddy ne ya tsure anty a daki yana tambayan ta game da hadin daya samu labari tana batun hadawa a tsakani na da sulaiman.
Kin fi kowa sanin halin da yaron nan yake ciki amma shine zaki dauki yar mutane ki hadata dashi don kwadayi komai yaushe kika fara wanan halin na marasa imani ban sani ba.
Idan yarinyar ta gane an cuce ta kina ganin ba zatayi kuka dake ba kai har ma da mu duk abin zai iya shafa nan gaba.
Haba dai daddy may zai sa da hankalina nayi irin haka ga yar mutane may tai min yarinyar nan ai in babu godiya to kuma babu fallasa.
Ta sauke ajiyan zuciya tana cewa dashi matsalar su daya da sulaiman domin ita ma Safiya postive ce da sauri yace may ne ?
Tace wallahi kamar yadda shima ya samu ta sanidan aure haka itama ta samu gun mijin da aka aura mata dan uwanta nan dai ta shiga bashi labarina yana fadin subbahanallah.
Yanzu wanan yarinyar mai hankali haka aka dauka akabawa mashayi ya cutawa rayuwanta subbahanallahi wallahi dai ana cuta a duniyan nan.
Yana kada kai yana fadin wallahi ta ban tausayi gaske nake ganin ta shiru shiru ashe da abinda ke damunta a rayuwan ta.
Ya kara nisa yace yanzu na fahunce ki idan kinyi hankan kin taimaka masu sosai don sulaiman idan a biye masa baiki ya zauna a haka ba ba aure.
Tace ai shi na gani don haka kamar yadda kowa bai san da halin da suke ciki ba sai muyi rufa rufa a daura kawai ta tare an wuce wurin Allah kadai yasan gawan fari tsakanin mu da su.
Nan dai suka kara tatauna yadda zasu fitowa zance don kada a samu matsala a wani bangaren a taru a rufawa juna asiri.
Mako shi kusan uku tun a abuja daya bar mu ya tafi bai zo gidan ba wai ashe tafiya ta kamashi ya ketara waje sai yanzu ya samu kan shi ya dawo nigeria din.
Ranan jumma daidai an sauko daga sallah sai gashi gidan ya shigo babu kowa a falon gidan sai nauran kallo da yake aiki shi kadai a falon.
Goran ruwa yaje da kansa ya dauko a fridge ya dawo ya zauna yana sha sai ga funke ta fito ta ganshi a zaune da sauri ta gaida shi don tana son zuwan shi don dan abinda yake bayarwa a bamu bayan tafiyan shi.
Ta juya bayan ta gaida shi zuwa kiran Anty a sama dakin ta sai gata da saurin ta tana fadin oyoyo da karamin mai gida.
Yace ai nayi fushi tun yaushe nake nan zaune sai ni da kaina na dauko ruwan da zansha gaskiya gidan nan yana bukatan kari don gidan yai maki girma ke kadai dole yaya ya kara wata.
Tai wani dafe kirji tana cewa waini dakaina kawa Allah ka huce ina ni ina amarya yanzu a gidan nan.
Nan fa nabar su Faiza ashe duk sun shige subar falin ba kowa a wurin wane ni in kyale ka haka koda yake zuwa bazata kai ma kai muna ai yaudin.
Yace kuma hakane fa to na dai huce tunda anfini gaskiya ya nisa yana gyara zama dakyau yace wallahi nima dai haka tafiyan ya kama ni gashi tun a abuja bamu hadu ba sai naga ban kyauta ba ko ban gajiya ban samu yi maki ba .
Tace kai haba dai ai nasan yadda harkan naku yake bawani lokacin kanku kuke dashi ba sosai mu dai tunda kana lafiya ai shike nan.
Ya sake mika hannu yana daukan ruwa gami da bude roban ruwan yace wallahi lafiya nake sai dai abinda ba a rasa ba dai.
Tace bari a kawo maka abinci shima captain tunda suka tafi masallaci bai dawo ba shida twins yace ashe suna can yau ya dauki rigima .
Tace wallahi rankai dade abincin fa your fovourite akayi yau fa a gidan don nasan kaima kaman dan uwanka ne kana son cin tuwo shi Safiya ta girka mashi.
Dam gaba shi yai mugun bugawa jin ta ambaci suna na take yawan mafalkin da yake akaina ya fado mashi a rai don bai ko son ya ganni don bai son zuciyar shi yana fada mashi karya a kaina.
Ban san da shi ba a wurin don anty ta kirani na fito da dan kwalina a hannu ina kokarin daurawa akaina sai ganin su nayi tare zaune suna kwasan dariya.
Gaba yai mugun faduwa dan ban san da zuwan shiba gidan kuma ban tsamani anty ta sani ba don baji tana magana ba.
Ban yar da mun hada ido ba sai gasheshi nayi da cewa sannu da zuwa uncle, ya amsa da yauwa mun samay ku lafiya.
Tuni har anty ta lura da yadda na daburce ko sai tace safiya ga bako mun samu yau girkin ki ko saura bai ragewa don maciya biyu sun hade a gidan jeki zubo mai abincin kafin daddy ya dawo.
Sai yace ai da a bari ya dawo muci tare don tunda ya fita da su yan biyu bai nisa da gida yanzu tunda an sauko tun dazun.
Na kalli anty tace barshi kin ji bai jin yunwane sai dan uwanshi ya dawo kin san haka suke kamar tasbaha wajen zumunci.
Ya kalleta yai murmushi yace in dai an matsa muna sai mu kawo wa mutum kishi ya yanzu don na gane tako yanzu baki son zancen kishiyan nan.
Dariya suka kwashe dashi tace mu ai yanzu ba batun mu akeyi ba kai dai ne gwaro zamuwa aure don zaman nan naka haka yana bata min rai wallahi.
Ya kwar da maganan da cewa kin ga ke ne mai sin cin naman Turkey yana mota na sayo maki ki tura a kwaso maki da sauran tsaraban ki har na fara tafiya zuwa dakina don jin topic din da suka dauko.
Sai naji tana cewa kai safiya don Allah dawo kin ji ki dauko min a saka a fridge tun bai lalace ba kace gobe akwai harka a gidan nan ke nan komai bazan ci ba sai shi gobe in Allah ya kaimu .
Juyowa nayi na dawo inda suke na dan tsaya dan nisa kadan dasu tace taya ni murna maigidana ya sayo muna naman Turkey wai yana a motan shi waje.
Dan murmushi nayi kadan yasa hannu a aljihu yana ciro key din motar shi yace anya kuwa zata iya kwaso kayan ita daya ?
Tace ai shine kuma fa kodai ba ka son ta wahala ne tun yanzu yace kai madam baki da dama wallahi aidai yanzu nasan takonki in kin yi wasa sai kiji ayyururi a gidan.
Tace gaba dai ba nan ba ai anyi tun 1900 dariya yayi yana miko min key din tace nifa da gaske nakeyi wallahi ba wasa ga magana na tace kira funke ta taya ki kwaso kayan don waya nan mashiriritan nan san sun kwanta ne.
Funke na kira muka fita tare a daidai lokacin da motan daddy yake shigowa ge din gidan tun mota bai tsaya ba su yan biyu suke kwala min kira.
Sun fito suka nufo mu suna cewa daddy ya kaisu shopping da zasu dawo mosque nace kaga yan gata daddy kenan daddy ya fito muna mashi sanu da zuwa ya amsa tare da cewa motar waye anan ?
Funke ne da sauri tace uncle ne yazo aisai yaran suka kwasa da gudu ciki suna fadin uncle oyoyyo nan suka barmu muna dariya shima daddy ya bisu ba tare da ya kara fadin komai ba.
Nace a raina ko yaro yasan mai kyautata mashi ke nan muka bude buth din da kyar don dagani har ita ba wanda ya iya saida security din kofan ya taimaka muna budewa.
Mun shigo da kayan da kyat muka koma kwasowa mun samay su na ta murnan ganin juna shi da daddy sun zauna kamar abokai sun rungumay junan su.
Mun gama kwasowa muka zube su nan a inda suke zaune anty sai cewa take a a a Sulaiman duk may ka kwaso muna haka ?
Yace well yanzu dai ai ki buda ki gani don ni yarana na yowa sayayya bake ba tace aina sanj indai sin kaine akwai ku dashi ba a magana.
Nace daddy a kawo abinci ne yanzu ?
Na fada tare da dan kallon shi yace haka ya kamata yar albarka ke kan ai mijin ki ya huta wallahi.
Jeki ki bamu yunwa nake ji sosai ganin wanan ya hana in nema tun da na shigo haka dai kuke so mutum kada ya huta ko yaushe sai aiki.
Mikewa sukayu zuwa table din suna kara tattaunawa akan kasuwan cin Sulaiman din wanda ya fara yanzu a logos da Abuja wanda yake kuma son karawa a wasu jahohin kasan nan.
Cewan da nayi wanan ya isa daddy ko a kara ne nace da daddy din sai suka maida kallon su ga abincin dana zuba masu daidai anty na kawowa wurin.
Dakyau safiya inji anty ai gwauna da kika tula masu abinci yau muga iyakar son cin tuwon su suma dariya suka sake a lokaci daya.
Daddy ne yace Safiya sannu da aiki kinji Allah dai ya saka maki da alheri anty tace ya nuna muna auren ta da oga koda yake ma na fasa bada kawar tawa ai don sai mu ja maka rai muma.
Daddy ya jawo plate din shi gaban shi yana cewa a a haka kuma zaki muna kinyi niyar yin abin arziki kuma zaki zuga yarinya Safiya karki dauki maganan ta ina bayan ki kinji .
Fuska na daure ba annuri na azuba masu ruwa na juya na wuce lokacin ya jawo plate ya fara cin abincin kamar bai son ci zuciyar shi ba dadi a lokacin.
Sai mamakin su yake yi kawai sunyi nisa da cin abincin shiru yai yawa daddy ne ya kawar da shirun da cewa wanan maganan yai min dadi danaji.
Don shawara ne may kyau madam ta kawo sai a lokacin yai magana yace tare da dakatar da cin abincin da yakeyi amma sai nake ganin wanan abin kun san bamai yuyuwa bane.
Daddy ya tare shi da cewa kana ganin zamu hada abinda bai dace bane a kan ka ko zamu cuce ka ko yarinyar ?.
Gaba daya ture plate din dake gaban shi yayi daddy yace kaci abincin kamana naga abincin yayi dadi ai .
Baiki ba yasa hannu ya mayar ga abincin daddy yaci gaba da magana yace ka kwantar da hankalin ka ka saurare ni.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGO, , , , , , ,
🧕🏿3️⃣9️⃣🧕🏿
INA MAKU FATAN ALHERI ACIKIN WANNAN TAKIN DA MUKA SHIGA UBANGIJI ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMISA AMIN YA ALLAH YAR UWA, , , , , , ,
Har ya juya ya tafi motar shi ta fita get din gidan tana tsaye tana daga mashi hannu tana murmushi a fuskan ta ta sauke ajiyan zuciya ta juya zuwa cikin gida.
Still su Faiza na falon ta shiga tana fadin aaah lafiya baku ga lokacin sallah yayi bane kuna zaune kuna kallo .
Nan suka bata rai sai anty tace may nene haka wai ina kuma safiyan ta shiga kuma bata zuwa ta dauke kayan nan a nan tashiga da su .
Faiza ce tai karfin halin fadin baza a bude muga abinda aka sayo ba shi muke jira mu watse dama wani kallon banza anty tai mata har ya sata natsuwa .
Tace don Allah baku jin kunyan hakan da kuke yarinyar nan bata saka maku ido amma ku kokarin ganin kwakwaf dinta kike yi ko yaushe.
Dan malama taya ni kwashe kayan nan mukai mata ciki kafin mu watse haka nan cikin bacin rai suka taya ta daukan kayan zuwa daki na sun shiga ga dakin tas sai kamshi ke tashi na gyara gado kamar wadda keda mijin aure a dakin.
Ina bandaki koda suka shigo sai maganan anty naji tana cewa ga kayan ki nan mun shigo maki dashi kafin fito ta face daga dakin don haka na tsaya nayi alwala nai sallah.
Sai da na idar da sallah duk suna falo sun fito na dauko kayan zuwa wurin anty da su buda tashiga yi tana yabawa da kyan abubuwan tace wanan irin kyauta haka Safiya ?
Na dan marairaici nace wallahi anty ni har abin yaban tsoro don haka yau ta diban kayan duk abinda yai mashi dadi a rai.
Wani irin dariya ta kwashe dashi tace ina ruwan sabon shiga dake dashi yanzu duk kun zama kamar yan koyo Faiza ce ta dakatar da duban wani ruba da ta dauka tana dubawa don bata san ko may ye a ciki ba.
Tai saurin aje roban a hannun ta tana kallon anty gami da cewa ko dai da walaki ne wanan sayayyan haka nikan nayi mamaki haka kawai zikau mutum zai yi hidama haka.
Ashe zamu sha buki kenan ta fada a cikin gatse wa mu biyun duka sai anty tace inda rai da lafiya mun kusa cassawa.
Tsukin da Fati taje ne ya katse hiranda faiza da anty keyi kan kaya tamike but ta shige tana ambatan munafunci shi kadai na iya ji cikin maganan ta.
Bayan shigewan tane anty tace wawiya kawai mara hankali don rashin wayyo wai ke ke gwada ma namiji kina son shi baza ki jira ya furta maki ba da bakin shi.
Sai faiza tace wanan shi ne son maso wani anty ta karasa da koshin wahala ba tana daki tana hauka shi hankalin shi na inda yake so.
Ashe bata karasa shiga ba tana jin duk abinda suke fadi sai dai bata ga bakin su sai ni da banyi magana ba taji haushi na.
Wai dama mu yan kyauye mun iya shige da fice wurin kwantan maza an raba kayan bayan anty ta fitar min da masu amfani naci din ne kawai tace a raba.
Bayan na koma daki wayana dake cikin jakkata yai kara da sauri najawo jakar ina daukan wayan wani irin firgita nayi don ganin kudi a jakar nawa.
Har wayan ya katse ban samu dauka ba don kudin ya firgitani kara waya ya kara yi sai na dauka a firgice ina sauke ajiyan zuciya.
Ummi na ce muka gaisa da ita na tambayi mutanen gida take cewa kowa lafiya sai dai mahaifin ki ne baiji dadi ba kwanan nan.
A firgice nake tambayan abinda ya samay shi take cewa dai je asibiti an bashi magani amma bin sai gaba yake yi kuma.
Na dauki salati nace ummi zan zo ko gobe ko zuwa jibi in Allah ya yarda mukai sallama hankali na bai kwanta ba ga zancen kudi ga maganan baba da ya tsaya min a rai.
Don haka na kasa bari sai da safe na saka hijjab a firgice tare da daukan kudin da wasu kaya daga cikin na dazun na hari dakin anty din.
Nayi sa a tana dakin bata nufi dakin daddy ba lokacin tana gani na ta mayar da hankalinta gare ni tare da fadin Safiya lafiya kuwa.
Karasawa nayi bakin gadon ta na zube kasa sai ta mayar da hankalinta gare ni na fitar da kudin ina mika mata nace anty yanzu nagan su a cikin jakkata ba san da su ba kuma.
Murmushi tayi ta karbi kudin a hannuna tana dan juya kudin tare da yi murmushi tace wa zai saka maki in ba Sulaiman ba don yasan in ya baki ba karba zakiyi ba don ya fada min kin ki ki saki jiki ku fahinci juna .
Dukar da kai nayi kasa ina tunanen yaushe ya zuba min su ban sani ba to wai ma ni ina zan kai wanan kudin haka masu uban yawa.
Ita ce ta katse ni da cewa indan kina tambaba ne bari yanzu in kirshi muji sai ta shi ga lalavan wayan ta dake bayan ta, alokacin nake fada mata cewa mun yi waya da ummi yanzu take fada min jikin baba ba dadi .
Sun je asibiti wai amma abin bai ja baya ba na karasa fadin ina son inje gida anty don in ga halin da yake ciki.
Ashe har ya dauki wayan ban sani ba yaji may nake fadi yake cewa tare kuke da mutumiyar ke nan tace eh wallahi gata nan tazo min a firgice wai taga kudi a cikin jakkanta.
Murmushi yayi yace rabon ta ne ya shiga jakkan ta kila tace ai dama nasan aikin kane amma dai ka ruda min kauna ka sani.
Dariya yayi yace ina son ta saba