Showing 108001 words to 111000 words out of 269010 words
kirani ban dauki lokaci ba na koma ciki tare da ita take ce min mu fara ba mutane abin gift din kamar yadda aka tsara fon uban gaiyyan kan shi yace ya gaji sai da aka nemo muna shi waje ,
Wai da wata yarinya tana fadi batare da ta kalle ni ba take naji gabana ya yanke ya fadi ya kuma ci gaba da bugu uku uku don kada anty ta gane nice muke waje ince mata may .
A tare muka je dakin da kayan suke sai da muka shiga ta fara bayani san nan na sauke ajiyan zuciya tana mun bayani gabana yaci gaba da fadu.
Munyi yadda ya dace haka mutane sukai ta watsewa don komawa gidajen su don dare yayi sai mu yan gida kawai aka bari nan wata doguwar mota ta kwaso mu zuwa gida gaba dayan mu a gidan anty aka sauka.
Sai mazan ne suka sauka gidan sulaima din haka wuri yayi kada dole nida yara muka koma dakin anty sukuma bakin suka sauka a dakin mu.
Ni dai bayan na tube har nayi barcin na falka anty tana gun bakin suna hira ko tashi nawa yan biyu ce ta falka da ni wai zata yi fitsari.
Na dawo kaita sai ga anty ta shigo dakin take cewa bumuyi barci bane idona da sauran barci nake cewa yan husna zatai fisari natashi.
Tace kin ganni sai yanzu muna can muna fira yaushe rabo a kasa na kwanta su suka hau gado sai da ta fito han daki ta ganni kasa take cewa haba dai Safiya ku kwanta mana saman gadon da yara nace kasa ma yai min don na sa bargo.
Tace kedai kin huta wallahi shiya sa nake ma Sulaiman gwadayin ya aure ki ai don rayuwan ki ke simple ne kamar nashi.
Ai yanzu dole in matsa mashi don an fara kawo mai mata wai ya aura ko da kuwa bai so haka za saka shi a gaba sai ya yarda.
Jin abinda ta fada yasani kallon ta da mamaki tace kina ganin wautana ko kan abinda nake kokarin hadawa da hankalina Safiya.
Sulaima mutum ne da ko wacce ke mafalkin auren shi kyakyawa mai kyauwon siffa da hali na gari ga wadatan zuci da Allah ya bashi dana Aljihu mai tattare da illimi addini da na zamani uwa uba dan karen tsoron Allah kamar yana ganin sa.
Abin da na fadi shu ya dakatar da ita da yabon da take fadi nasa don cewa nayi anty ni ina ni ina Sulaiman gashi dan masu arziki niko yar tallakawa.
Dama dai Fati dake mutuwan son shi kikai kokarin hadawa dashi don ita yar uwar kine gashi tana mutuwan sin shi sosai , , , ,
Ke dan Allah rabani da abin haushi koda sulaiman zai iya auren ta ba zan yarda in hada shi da fati ba don bata da tarbiyan da ya dace da mutum kamar sulaiman a tare da ita.
Balle aure ita dashi ya haramta gare su don dai sulaiman shima victim ne irin ki matsalan ku daya dashi.
Da sauri na dago kai na kalleta nace nace a razane HIV anty ?
Tace wallahi Safiya tana hawa gado take cewa matsalan ku daya dashi shima wata ya aura maishi suka munafunce shi basu fada mai ba sai bayan aure ya baiyyana mata koda akaje aka duba akaga shike gare ta har yai nisa da aka auna shi aka samu shima ya samu daga gare ta.
Wallahi safiya daya kiramu yana kuka kamar karamin yaro yake fada muna ranan mun shiga tashin hankali ba karami ba a gidan nan .
Allah yasa daddy yana nan shi ya shiga jirgi yaje can South African ya samay su inda ya samu ya shawo kan shi sai dai kafin yaje har ya saketa ko.
Daga baya daddy yayi yayi dashi ya maida ita amma yace ya gama auren ta karshe ma yace shi ba zai kara aure ba a rayunwan shi.
Daga baya muke jin wai ta gaji da bin shi ta auri wanda yasa mata cutan yanzu shine kika ga sam baya son ai mashi maganan aure kuma ya koma gudun mata.
Dama can ba damuwa yayi da matan ba sai abin yazo mashi da sauki dalili kenan kika ga ina son in hada ku don ko banza halin ku zai zo daya dashi.
Yanzu haka yan uwa basu san halin da yake ciki ba don ba afitar da zancen waje wani yaji ba.
Shine ita mahaukaciyar kika ga tana wanan haukan haka shi yasa ma kika ga bai son zuwa kasan nan don matsin da iyayyen shi ke mai akan ya kara aure.
Kafin taga bani labarin fuskana har yacika da hawaye fam taji ina kuka tace ke ko saurin karaya gare ki ai hakkuri za a yi haka wani rayuwa yakan zo wa ba ya zama BAHAGGON RAYUWA .
Amma in ai yi hakkuri aka rungumi kaddara sai Allah ya duba ma mutum Allah mai tausayin bayin sa ne akoda yaushe yana ma mutum mafita ta hanyar da bai zata ba.
Nasan labarin nan da kika ji ya sa kin tuna da naki matsalan ya dawo maki da shi sabo sai hakkuri abin ba dadi gaskiya.
Ta haye gado ta kanta tare da kashe wutan dakin ya koma duhu ta barni cike da tausayin kan mu da ma sairan uan uwa musulmai da suka tsinci kansu a wanan halin irin namu.
Tabbas Sulaiman idan ya zama mijina zan yi kokari inga na bashi kwanciyan hankalin da ya dace dashi naji zuciya na ya sami karbuwa dashi dari bisa dari bawai don kudin shi ba don ni basu gaba na yanzu don ina ganin kwana nawa ma yarage min a duniyan.
Saboda na sha zama inyi ta nacin rokon Allah da yai min mafita ga matsala ta in samu miji wanda zan masa biyayya kuma yasan ina yi.
In har abin ya tabbata zan fi ko wata mace sa a a rayuwana amma kuma ban taba tunanen samun haka ba.
Sai gashi kwatsam Allah na baiyyana min ansan addua na yana batun bani uncle Sulaiman a matsayin miji a gare ni.
Nasan anty da naci kan abinda take so wanan abinda take shirin hada min da wani irin godiya zan saka mata dashi don tsabar girman shi da daraja a a gare ni.
Sai dai kuma kash nace a raina anys kuwa shi uncle sulaiman din zai soni kuwa ga yadda yake baya kallon ko wata mace.
Kuma ma yasan cewa na taba aure har da haihuwa indan bai taba sani ba anya zai so bazawara kamata kuma yar talakalis.
Wanan sune tambayoyin dana rika yiwa kaina kawai sai jin hawaye masu dumi nayi sun soma bin kuncina a karo na farko da na furta Allah ya isa ga Ahmed kenan.
Don shi ya jefa rayuwa na a wanan hali dan ma taimakon Allah ya kawo min sanadin sanin anty a rayuwa na har take kokarin mantar dani halin da nake ciki yanzu.
Na sake fadi Allah ya isa aure na da Ahmed cikin sanyin jiki na gyara kwanciya na ina ci gaba da tuna ne wanda ban san iya wanda nayi ba a lokacin.
Washe gari mun tashi da baki a gidan don haka tunda nai sallah muka fada kitchen dani da funke don hada masu abin karyawa.
Koda anty ta tashi har mun gyara gida mun gama hada breakfast din na shiga wanka ina jin tana fadin yau na shiga uku wani irin barci ne nayi haka mai nauyi.
Na fito ina mata ina kwana tace safiya ai yau kan ban san irinbarcin da nayi ba ga baki gida ban shirya masu abin karyawa ba har wanan lokaci.
Nace anty fita falo kiga abinda muka shirya masu ko yayi na dai hada ban san ko zaki soshi na tace kai Safiya ubangiji Allah yai maki albarka yasa mu raka da junan mu.
Har kin hada abinci ina daki kwance ban sani ba shiyasa nake son kada ki kubcewa Sulaiman don shi kadai ya dace dake.
Shima kene kika dace dashi sai ku taru ku rufawa junan ku asiri a zauna lafiya.
Murmushi nayi nace kai anty dai kina dai son musa kafan wando guda da fati a gidan nan don ta mutu akan so uncle din sosai wallahi.
Wai ba zaki rabani da wata Fati can ba ana maganan mutanen kwarai kina kawo min fati ciki wanan kazama may ta iya banda rashin kunya ita kuma Faiza ragguwa ce ta karshe bata iya aiwata komai banda kallo da kwanciya ai dai za a yita ta kare ga yan uwan haihuwan shi ai sunzo
Sai da mukai wanka muka fito falon a lokacin har bakin suma sun fito ko take cewa kun gani sai yanzu na tashi ba sukace suma basu dade da tashi daga barci ba ai.
Dayan tace gashi har an hada abin karyawa ko tace aikin sarakuwan ku ne wallahi sai duk suka kalleta matar take cewa sarakuwan mu ta ina tace Sulaiman mana.
Nan suka shi murna da sa albarka ga abin nidai kunya duk ya rufe ni dago kan da zanyi sai ga fuskan fati tana tsaye kamar ruwa yaci ta.
Uncle ne sukai sallama da sauran mazan da suka kwana gidansa suka shigo da murnan su sai ya samu suna zuba abinci yace a a madam baku gaji ba har kun iya tashi kunyi wanan aiki haka.
Bata kai ga bashi amsa ba sai wata tace kaidai ai kayi dace wallahi ga yarinya da kirki ga kunya Allah dai yasa ayi damu.
Kallon mamaki yake aikwa anty sai tace Safiya na fada masu nufinka akan ta shine suke ta murna da abin.
Ajiyan zuciya yayi ya gyada kai yana cewa kai madam baki da dama wallahi sai matar tace wallahi mukan munyi murna don wallahi zaben yayu kun dace kwarai .
Gashi muna barci an hada muna abin karyawa irin haka may ake nema gun mace dama tasan darajan yan uwaka an kuma samu tunda anty ta yaba da hankali ta may za a jira banda musha buki.
Ni dai duk na kasa sukuni a wurin don haka na mike da sauri na shige daki cikin kunya duk suka bini da dariya banda shi da yake jin wani iri a zuciyar shi.
Don may anty take son ta yaudari yar mutane gata karama zata cuta ma rayuwan ta bayan tasan halin da yake ciki.
Idan wani ma bai sani ba yasa take fadin haka ai shi da ita sun san matsalar shi ta rasa wanda zata cuta sai wanan yarinyar dake kokari da ita haka a gidan.
Shi har naka bashi tausayi idan yazo bai taba samun Faiza ko fati na kau da kara a gidan ba komai ni zai samu ina yi ko yara ke son abu sai dai yaji sunce anty Safiya.
Har suka gama karya da yan uwa yana cikin wanan tunanen yace su tashi yakai su su zaga gari don washe gari zasu koma gida don haka yake son ya fita dasu.
Har sun fita ya juyo yace madam idan na gama dasu kila zan dawo don akwai maganan da nake son yi dake idan mun samu time.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,
🧕🏿3️⃣7️⃣🧕🏿
INA ROKON ALLAH DA YA SADA MU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN WATA MAI ALBARKA YAN UWA, YASA MUNA CIKIN YANTATTUN BAYIN SHI, , ,
Bayan komawa yan bauchine gida sai muka fara shirin tafi muma don sam ba mu san zamuyi wanan kwanakin haka ba a abujan.
Har lokacin Fati bata sake min fuska ba cikin ma bataji kan maganan sosai ba don dukkan su basu kusa dan haka basu ji maganan da akayi da kyau ba rana.
Mun fara shirin komawa lagos sai dai har lokacin bamuga Sulaiman din a cewan anty tafiya ya kama shi ya tafi gida.
Shiri sosai mukeyi dole a mota mukai tafiyan don kayan da muka loda na amfanin gida a Abujan dama wasu tarkace can.
Mun dawo da kwana biyu mun warwale gajiya a jikin mu yau anty ta fita aiki Fati tafita zuwa makaranta sai Ni da Faiza kawai a gida.
Na gaji da kwaciya dan haka na fito falo muyi hira da Funke sai na samu Faiza ta rigani fitowa tana gani na take cewa kema kin fito shiru yai yawa a gidan.
Nan na zauna muna hira har funke din sai dai matasalan Faiza shine son ayi da wani a bayan shi wanda ni kuma ban lamunci haka ba sam.
Take fadi wai dama tana son mu samu lokaci ne ta fada min Fati fa ta fara zargina akan ina shishiwa don in fi kowa gun anty dama haka muke da bin bokaye ai duk inda bakauye yake ya san inda bokan kwarai yake ko malam.
Murmushi nayi nace aiko ba boka da malam idan ka gyara alakarka da mutane sai a soka ita tasan wanan don haka take zargin kowa da wanan halin.
Duk hiran da ta dauko sai in kawar dashi don mafi munin sabo shine giba amma ita shine sana,anta yi da wani idan baya kusa.
Munyi gyaran gidan nida Funke kamar ba tafiya muka yi ba munn maida gidan tsab gwanin ban shaawa na koma daki na kwanta ban falka ba sai da maigidan ta dawo ta turo yaran su kirani.
Ckin barci naji suna tadani wai mummy su na kira na, mika kawai nayii na sauko muka fice dakin zuwa falo tana tsaye a tsakar falon da waya a hannun ta.
Wuri na samu naja na tsaya ina jiran ta gama sai na zo na fahinci sa mijinta take waya sai da ta gama ne ta kashe wayan ta maida hankali gare ni..
Anty sannu da dawo wa nai mata ta amsa tare daga mun hannu tace yawa safiya zozozo nan kin ji tana mika hannu wai in zo kusa da ita haka take yi idan abu ya dan ruda ta ko ya bata mata rai.
Banyi nawa wurin karasawa inda take ba ta riko hannu bibiyu tana cewa Safiya kiji min daddy da rigima wai bai fada min zai fito ruwa ba mu shirya mai sai yazu da suka fito wai yake sanar dani sun fito.
Jimun daddy da neman rigima fa safiya ni kaina ma ya kulle ban san may nake ciki ba wallahi yanzu in an gama masu clearing za a kawo shi gida.
Nace anty ba daddy yafi son tuwo ba tace shi ne ai safiya nace akwai komai hade tuwon kawai zan tuka bani minti ashirin yanzu sai inyi warming din biya don dama jiya na hada su.
Tace kai Safiya sai ta rungumoni zuwa jikin ta tana cewa yarinyar nan basan godiyan da zan maki ba amma dai bari komai nake dabban zan fitar maki in daddy ya dawo.
Haka take dason abin ban dariya sai dai kuma indan ta tashi daure fuska ba mai gane kanta kuma sai taga daman saukowa dan kanta da kanta.
Kafin daddy ya iso gida mun hada mai table lafiyayyen abincin irin wanda yake so namu na gargaji na shirya mai tuwon semo sai miyar kubewa danya sai stwee din cow tail dashi zai hada ya ci simple.
Sai abin sha suma na jera su yadda ya kamata da kunun samiya da yake son sha sai kamshi kayan yaji yake yi.
Wanka na shige ina ciki naji jiniyan su ta aiki ta shigo gidan haka yasani sanin ya dawo take gida ya rude da murna don shima daddy kamar matar shi yake bai da matsala ko kadan da kowa a gidan.
Matsala daya ne ba a ganin shi sosai kullon yana ruwa kasancewa shi na sojan ruwa indan ma yana tudu aikin gaban shi ya shamai kai.
Ban fito ba sai da na shirya mai kawai na shafa na zura rigana na fito tari yan shi na samu kowa a falo security din shi na ta shige da fice nace aifa bissimillahi a raina yanzu zamu fara ganin kattan sojoji a gidan ba da dare ba rana.
Can na hango shi yana ta yanka loman tuwo yana kaiwa baki na karasa da sauri ina fadin daddy sannu da zuwa ya dago yana kokarin hade loman tuwon da ya cusa a baki yace.
Yace yanzu nake tambayan ki naga kowa ban ganki ba na dauka kin koma gida ne sai anty dake gefen shi tace ai yau da ta wuce da bakaci wanan tuwon ba aiki ta tsaya yi sai ta shiga wanka kafin ka iso.
Nan dai na gaida shi nai mashi sannu da zuwa da yaya aiki da hanya ya amsa a takaice yana mai ci gaba da cin tuwon dake gaban shi alama ya nuna yana jun dadin kasancewan shi a gida.
Tunda suka shige bai kara fitowa ba daga shi har matar nasa su yan biyun su suna tare dani ranan a wurina suka kwana basu koma dakin su ba.
Duk da daddy ya dawo bai hana anty fita aiki ba da safe sai da daddy ya tashi yai breakfast shi kadai nace a raina mijin ma,aikaciya kenan.
Bai fita ko ina ba muke ta fama da dauwainiyar shi a gida har zuwa lokacin da ta dawo don bata dade a wurin aikin ba ranan.