Showing 150001 words to 153000 words out of 269010 words
ni yayi tare da min sannu da zuwa na karba mai fuska sake don mun saba dashi dan haduwar da mukeyi.
Key ya karasa inda suke ajewa ya dauka yana cewa zai fita yayi services din motar yace mai sai ya dawo.
Yana fita ya fuskance ni tare da cewa jinan sai na tattaro hankalina zuwa gare shi yace idan kin je gida yau ina ganin next week magaba tana zasu shigo.
Don a daidaita maganan auren mu ban son abin ya dauki lokaci mai tsawo tunda kin ga an fara samun matsala a ta inda bamu zata ba.
Don haka next Saturday in sha Allahu iyayyena zasu zo sai a saka muna rana dan naga amaryan nawa har yanzu hankalin ki bai kwanta ba.
Murmushi nayi tare da fafin Allah ya kaimu lafiya amma ni ai ban tayar da hankali na ba don nasan komai Allah ke yi .
In bashi ba ina ni ina ja da yar wurin anty uwa wa yan nan yan gaye wa yanda boko ya ratsa su ciki da bai din su ai sune suka dace dakai.
Murmushi yayi yace a naki ganin ke nan ni sam bani rayin irin su nafi son wacce zan iya controling ba tayi controling dina ba ko may kika ce ?
Nace Allah yasa mu dace yace amin mun ma dace din sai dai muyi adduan Allah ya hada hankali baki daya.
Driver ya dawo bai dauki lokaci ba muka kama hanya bayan sun gama ganawa da maigidan nashi ni kuma ya cika min jakkana da kudi wai don bukata acan .
Yace ba lalai bane mu hadu da sauri don zaiyi tafiya cikin wani sati don haka koda zasu zo yana ganin ma bai kasan.
Da haka mukai sallama dashi muka dauki hanya sai garin mu zuciya na cike da damuwa don ban san zan zo gida ba a wanan lokaci.
Mun shigo da dan sauran lokaci don sam bayi tsamanin cewa an gama ginan gidan mu ba har sun tare a ciki.
Sai driver ne naga yaja ya tsaya a kofan gidan mu nan na fara raba ido ina kallon aikin da sulaiman yayi mu agidan muna tsayawa su yaya Sani dake daban su suka taso da saurin don ganin motan da tazo kofan gidan namu.
Ina fitowa suke fadin a safiya ashe ke ne tafe yaya sani da ke kokarin kama marfin kofan ya ce safiya lafiya kuwa ?
Na kalleshi da murmushi nace lafiya yaya mun samay ku lafiya ?
Ya amsa da lafiya aka fitar min da kaya zuwa cikin gida ina biye dasu duk kan gidan ya juye min kamar ba dan kangon gidan mu ba.
Dakin ummi suka nufa da kayan nawa ana cewa Safiya duk suka firfito waje din taro na da murnan su
Sai mamakin tsarin gidan nakeyi ina mai kara bin ko ina da kallo muryan mama naji daga baya na tana fadin kina kallin ikon Allah ko.
Kin ga yadda ubanigji ke nasa ikin haihuwar mace yayi muna rana a gidan nan don gashi ta mayar damu yan birni a lokaci guda har wutan Nepa mun samu bana.
Nayi dariya nace mama mun samay ku lafiya tace aikece abin gayarwa keda kika sha hanya mai nisa.
Takalmana na cire na shiga dakin ummi tana zaune saman kujeran da aka saka masu a falon na rungumo ta sai ta ture ni tana cewa rabani da abin kunya kiji.
Nace kai ummi har yanzu kunyan ne haka takalman da na cire kanne na suka dauka suna kallo gardama ya kaure a tsakanin su wanan yace kwalba wanan yace roba ne da filawa cikin sa.
Dukawa nayi ina gaida ummi ga hasken wutan lantarki da ya haska dakin ya baiyyanar da farin da lafiyan da na kara a lokaci guda.
Daidai inna ta tunkaro dakin a take taji wani irin tsana na ya shiga zuciyar ta lokaci guda cikin yake tace Safiya ne yau gidan namu.
Da sauri nace eh inna mun samay ku lafiya ina saadatu tace ai tana tafe na barta daki ne wai kan ta ke ciwo yau nace ayya ai gani tafe in duba ta.
Kanne na suka kwashi kayana zuwa kuryan dakin ummi sai bin ko ina nakeyi da kallon mamaki acan ma da na shiga an gyara shi tsab ga gado har da sphare din kujera dogo.
Na aje jakkana na fito zuwa duba saadatu a dakun su sai muka hade da ita ta taso da kyar muka koma dakin nasu nan naga watau kowa da kalar kayan da aka saka mai a dakin shi.
Munyi yaushe rabo da saadatun inna tana kurya tana jin mu saadatun ke ce min komawa zanyi ne ko zan kwana biyu .
A nace cikin dariya a a saade na dawo kenan sai yadda hali yayi kuma tace kice muna nan ke nan dake kwana biyu nace kwarai da gaske.
Nan dai muka sha hira da ita na tashi ina cewa zan tafi in gaida mama dakin ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGN , , , , , , , , , ,
🧕🏿5️⃣1️⃣🧕🏿
NOVEL DI NA NA KUDI NE NA FADA TUN FARKO KARKI FITAR KARKI KADA KUMA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA, CIN AMANA BIBIYA TAKAI TA INDA BAKIYI TSAMANI BA, , ,
Tun farko na fada maki karki fitar min da novel don karatun ba dole bane ba kowa nake ba amma nasan Allah ya isana dama bai tafiya ga banza.
Bakiji bake kaida bane don akwai wata mai fitar wa bayan ke ke ce kika fara gani saura dayan nata sai yafi naki don ko abin ba zai zo mata da dadi ba ita.
Akan novel akan son kai tajawa kanta masifun duniya sai da na fada maku dan Allah kada ku fitar min don kada in dauki alhakin ku a kaina.
Kullun ina nanata maku kin dauka wasa ne ba abinda zai faru dake har yau kaf makaranta novel dina ba wanda zaice maki yasan makawa ko ya san ida take da idon shi hmmm muje zuwa yanzu aka fara ai ya kama binki ke nan ta hanyar dabaki zata ba yar uwa.
Ganin gidan namu nakeyi kamar bakon wuri a idona don komai ya canza min a idona sai nake jin wani irin dadi a zuciya ta.
Ranan barci dai ne barawo da ya iya dauka na safiyan fari kiran sallah masalacin da Sulaiman ya gina wa mutanen unguwar mu ya karade min kunni na dole mutun ya tashi saboda karan lasifikan da yai yawa.
Duk da bani sallah amma na tashi a lokacin na kewaya na dawo na kwanta ban iya kwaciya ba na mike zan fita don shara ummi na dake falo kwance ta dakatar dani da fadin.
Dama kin koma kin kwanta don ko dan Albarkan nan ya rabawa kowa wurin ta don haka yanzu ma ba komai akeyi a gidan gaba daya ba.
Na koma na kwanta kamar yadda ummi ta umurce sai dai ba barci nayi ba kwantawa kawai nayi zuciya ta fam da tunane.
Misalin sha daya saura na safe na fito saye cikin kayan barci na da ban cire ba a falo na samu ummi da kanne na suna karyawan safe tayi masu faten doyan da nazo masu dashi jiya.
Na fada saman kujeran da babu kowa saman shi don kasa suke zaune dukkan su tare da yin mika nace duk na gaji kamar nayi wani aiki mai yawa.
Ummi ne tace min ai tafiyan mota mai nisa gajiya yake sawa mutum ajiki na gyara kwanciya ina fuskantar su dakya nace ai rabin tafiyan a jirgi nayi ummi daga nan dai zuwa abuja ne ya saukar min da gajiyan.
Tace masu gari yau kece mai tafiya a jirgi yar nan lalai duniya abin da ya baka tausayi wata rana shi zai baka mamaki.
Kwarai da gaske ummi wallahi ni kaina ganin abin nake kamar a mafalki don nakan yi tunanen hakan a raina.
A jiuan zuciya naji ummi tayi tace mhmm ai tun dawowan mu gidan nan yau sati uku ke nan inna ku sai ta baka tausayi don zaman ta a babban gida ta raina kanta sosai a can don basu raga mata ba ko kadan.
Tace yaya wajan anty naki suna dai lafiya ko bansan adduan da zawa wanan matar ba a rayuwana sai dai fatan gamawa da duniya lafiya.
Shiru nayi ina mai ci gaba da tunane sai da naji ummi tace yanzu yaushe zaki koma naga kin kwaso uban kaya kamar baki da niyan komawa can.
Nisawa nayi na dawo daga tunanen da nakeyi nace ummi ba zan koma gidan anty ba indan ba aure nayi ba in je in gaida ita.
Da sauri ummi tace akwai matsala ke nan a tsakanin ku ganin kanne na dake zaune sun kallo ni lokaci guda yasa ni cewa babu komai haka dai na yanke a raina.
Shiru naga ummi tayi sai can tace a zubo maki faten ne kishashi da zafin sa tun baiyi sanyi ba ki kasa sha barshi ummi ban iya cin abu mai nauyi da safen nan.
Sai kaunana tace ai kin san anty Safiya bata son cin abinci ummi kina dai wahal da kankine sai zuwa rana zakiga tana neman abu mai ruwa ta sha shi ne karin kumallonta ita.
Ummi na mikewa take fadin mukan na kauye ne sai da abu mai dan nauyi muke jin dadin karin Safe don badon doyan nan da kika zo muna dashi ba da shin kafa da wake zan masu da safen nan su karya ko wanan wanan yar sa idon ne nayi aune da ita tana ferewa wai fate zasu sha da safen nan.
Muryan baba danaji ya nufo kofan mu yasani mikewa na isa kofa ina fadin baba har ka fito banje mun gaisa ba.
Yace zan fita Safiya jinki shiru yasa na dauka ko barci kikeyi yaya hanya yaya wajen su hajiyar taki nace suna lafiya sun mace agaida kai.
Yace ina karbawa yaya wajen gwagon naki kina lekasu kuwa na dukar da kai sai yace aiko baki kyauta ba Safiya ai ba a yanke zumunci tunda ita ta yanke da sai ke ki raya shi lada zaki samu a wurin Allah.
Nace baba ai zan tafi amma gaskiya ba yanzu ba yanzu ba nafi son sai ina da aure inje da mijina yafi sauki.
Yace kuma fa kinyi tunane maikyau kuma Allah yasa mu dace yaya shi Alhaji sulaiman din suna dai lafiya ko na amsa kasa kasa da lafiya yake shima yana gaida kai baba.
Ya juya yana magana da ummi da take kofan daki hakan yasani mikewa na shige uwar dakin namu ban zauna ba wanka na shiga don makewayin da ke akwai a dakin kuma da ruwa a ciki.
Na fito ina shafa mai ummi ta shigo kuryan dakin tana ce min may ke faruwa tsakanin ki da uwar dakin naki naga ganin kannen ki yasa baki fada min ba.
Nace ummi ba wani matsala sai dai akwai matsala kadan nan dai na fara bata labarin abinda naji da kunne na anty din tana fadi.
Ta nisa tare da fadin ikon Allah ai tayi kokari ko wanan da datayi Allah ya saka mata da Alheri ai an gode.
Shi son kai sone ba wanda yaki nasa ya samu bata so ki ba taki dangin mijin ta don ko sune nata don da su take zama.
Nace aini ummi banga laifin anty ba don sanin ko waye anty uwa danayi don ba karamar macen duniya bane sosai anty uwa.
Tace Allah yai muna mafi alherin sa nace amin tace yanzu shi may yace a nasa bangaren nace yace wani sati magabatan shi zasu zo sai a saka ranan aure dayani.
Tace to Allah ya kyauta muna magana kiran wayan shi ya shigo nan ta fice dakin ta barni ina karba wayan nayi sallama ya karba yace.
Watau kin ga ummi kin manta da kowa ko nace ba hakana bane yanzu na tashi ina batun kiran ka sai gashi ka kirani yanzu.
Yace yaya gajin hanya don nasan akwai gajiya nace Alhamdullahi yaya na barku can?
Ya amsa da kalau sai nace yallabai naga ka mayar muna da gida kamar bila ubangiji Allah ya saka da alheri ya dada daukaka da yalwatan arziki murmushi naji yayi yace anty ki ta kiraki kuwa ?
Ya kawar da maganan nan take nima murmushin nayi mashi nace baka son godiyan nawa ke na ko ?
Yace tambayan ki nake yi antyn ki ta kiraki da kika zo arewa?
Nace har yanzu bata kirani ba yace na san za a rina ai, kyale ta, jiya ta kirani yau ma da safen nan munyi magana da ita.
Sai naji bakina yana tambayan shi may tace ma ?
Sai yace min ina ruwan ki da maganar mu da ita.
Haba uncle dina don Allah yaya kukayi da ita yace maganan dai ne na in rabu dake in auri diyar hajiya uwa don tafi asali.
To kai may kace mata yace cewa nayi haka shine daidai don dama ke baki waye ba.
Nace to Allah ya hada kowa da rabon sa yace amin ai ya hada tunda ya hadani dake kin sace min zuciya yanzu bani jin maganan madam dina kuma.
Murmushi nayi wanda ya baiyanar mashi da jin dadi na a fili tare da sauke ajiyan zuciya tare dacewa nagode uncle dariya yayi yace aini zan gode maki da baki yarda sun hadani da ke ba.
Murmushi nayi nace ai ba zasu iya ba don hadin Allah ne bana mutum ba da zasu iya da sun raba ko tunda duk wanda aka fadawa irin kazafin da sukai min dole ya dauka gaskiya ne.
Ya katse ni da cewa ai baki san wani abu ba nace ina jinka.
Yace ai tunda ta gabatar min dake da farko hankali na ya kwanta da zancen ki don haka ma daddy su twins shima ya yaba da hankalin ki.
Banga abinda zaisa yanzu daga baya ba kuma ta kawo min zancen wata na dai ce da ita haka ne daidai sai idan lokaci yayi zata sani.
Mun dauki lokaci muna waya dashi kamar ba kudi yake kashewa ba sai da ya gaji don kanshi yai min sallama na tashi na karasa shiri na dakin mama na fara shiga muka gaisa muka dan taba hira sai na wuce dakin inna inda na samu saadatu ita kadai a dakin wai inna tafita unguwa.
Nan na sake jikina muka dauki lokaci muna hira da ita nake tabayan ta fanin Isah dayai mata ciki take fada min bata da labarin shi.
Nace baya kawo maki komai ne tace tun wanan lokacin bai kara kulata ba kuma ba wanda yai masa magana akai ana batun ginan gidan mu.
Da yaya sani ya shigo na tuntube shi da zancen sai cewa yayi min ai shi ba abinda ke gaban shi ke nan ba nace haba yaya sani idan baku tsaya muna tsaye ga alamarin mu ba wa zai tsaya muna akai yace zai duba yagani yadda za a yi.
Anan muka bar zancen ban jima da fita dakin nasu ba inna ta dawo gidan tana shigowa sai ta fara budan hancin ta tana shakan kamshina dana bari dakin tace.
Safiya ta shigo dakin nan halan sai Saade tace eh tace karuwan banza ina shigowa naji kamshin turaren ta.
Haba inna Safiyar ce kuma karuwa Saa ta fada mata haka na tace idan ba karuwa bane may nena ita uban wa take nema a birni.
Abinda kikeyi gaskiya inna baida kyau shiyasa kullun bamu ganin karuwa ga alamarin mu don bakin hassada irin naki.
Aiko tayi cikin Saade din da fitina ita kuma kamar mai jiran uwa nan suka shiga yaba ma juna bakar magana har ya jawo hankalin mutanen gida aka tsaya sauraren ta yaya Nura da yaya Sani ne suka shigo gida suke tambayan ba asin maganan.
Inna ta kama inda inda sai Saaden ne ta fada masu abinda ya hada fadan da sukeyi daidai ina fitowa daga daki kenan maganan ya daki kunne na.
Cak na tsaya raina ya baci sai yaya nura ne yace in ma karuwanci Safiya ke yi a birni ai anci albarkacin karuwancin ta a gidan nan.
Yaya Sani ya karbe da fadin wallahi fa ke yar taki mai take zaman suna takeyi maki a daki da tsohon ciki komay ba gara safiya ba kowa ya san alherin ta ne ya kaita ga haka.
Wallahi inna idan kice bazaki bar halin nan ba watarana sai kinji kunya ba kadan ba zuwan Safiya dakin ki alheri ya kawo ta ba tsiya ba.
Don zuwa tayi ai magana da Isah asan halin da Saadatu ke ciki don bai waiwaye ta ba har yau mama tace kai kedai Rakiya halin ki baiyi ba wallahi.
Safiya tayi maki kama da wacce take karuwan ci koda ba a ganin zuciyar mutum ai abin duniya baya boyuwa da muji tun