Showing 237001 words to 240000 words out of 269010 words

Chapter 80 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13326

da basu da nauyin kowa a ransu abinda suka ga dama sukeyi sai wanda ke da tsoron Allah a zuciyar shine Allah ke tsarewa.
Amma nan arewa a cikin tako suke alamarin na yadda kafin a gane halin na miji sai ta dade yana cutar da mutane wani kuma ba yadda za a gane halin sa sai Allah.
Da ire iren wanan tunanen barci ya dauke ni bamu falka ba sai asuba don abba tunda ya tashi kafin mu kwanta na bashi madara yasha ya koma barci bai kara falkawa da dare sai dana tashi zan yi alwala don yanzu ya fara wayau ya tashi yana ta kuka.
Saida khadija ta kamashi ta goya ta hada mai madara yasha ya koma barci ina zaune take cewa yanzu fa ya fara gane ki anty.
Don daga tadhin ki yasa kuka wai don may kika tashi nace bari zaiyi ai idan mun koma don dan tafiyan da mukayi bauchine gashi kuma bamu zauna ba mun taho nan.
Hmmm aini idan na tuna badakal ku da uncle a bauchi abin dariya yake bani nace in dai uncle ne ai kadan ma kika gani don ban biye mashi ne kawai.
Yanzu baki ga dana nuna mashi ban damu ba dayace ban zuwa gida ban san abinda ya gani ba kuma yazo ya barni inzo da yaso ne fa da na zo mu koma tare dashi.
Tace hakan yana yuyuwa kuwa anty dz fa duk wanan ziyarar bakiyi shi kai koma a garin ba inda zaki ai.
Uncle ai halin shi sai shi wallahi wanda bai san halin shi ba sai yayi ta wahala da daki nakan shiga inta kuka daban gane haka yake ba.
Amma anty maganan da kika fada ma anty Amina daren jiya naga jikin ta yayi sanyi nace tayi sake ne tun farko ta saba mashi da hakan da tun farko ta koya mashi zama gida ba zai yi hajan ba koda zaiyi ba hakan da yawa ba dai.
Mazan mu na hausawa na da saukin kai idan mace ta san yadda zata bi dasu sai dai abinda basu so mace ta nuna masu kamar tana commading din su sai suce ka raina su.
Tun da mukayi sallah muke hira duniya dani da khadija anan na samu daman yi mata magana akan ta rabu da Sanusi dan uwar inna.
Na nuna mata illar abinda take shirin yi din dayin hakan nasan dai magana na batai wani tasiri a zuciyar ta ba sai dai a sanu zata gane abinda muke nufi gare ta.
Nayi mamakin ganin sai da rana ta take Amina ta tashi ida na fahinci ba wani dogon addini suke yi ba da ita da mijin nata don ta fito tana fadin wai sun makara ne.
Nace Amina ya kamata fa yanzu ki daina wasu abubuwa domin ke din uwace a yanzu kina kwaciya barci har asuba ta wuce bakuyi sallah ba ta yaya kike ganin zaki koya ma diyan ki ibada da hakan.
Shifa yaro anbinda kake yi yake koyi dashi mai kyau ko mara kyau don shi gani yake komai daidai kake yi.
Tace wai ni Safiya wanan mijin naki halan ustzune naga duk halaiyar ki sun kara canzawa yanzu ba a yanda na sanki ba duk da dama can babu ruwan ki baki kaimu rawan kai ba.
Dariya nayi kawai mun karya ban wani jin dadin zama a gidan ba don haka kamar yadda muka bar gida sha biyu haka muka baro gidan Amina zuwa gida bayan na masu alheri muka dawo gida.
Saboda gaba daya naga Aminan ta canza tabar halaiyan ta dana san ta dashi a baya sai wani nuna waye taki wanda bai dace da diyan musulmai ba da matan hausawa.
Abinda nake son mata su gane shine bawai sai mun nuna wayewa a fili za a san mun waye ba dabiun ki na diyar bahaushe musulma a ko ina ya rinjayi zuciyar ki.
Ako ina kika samu kan ki kada kiga kina zaman bariki ki watsar da tarbiyan da kika samu ki manta da rayuwan ki a yanzu yafi muhinmanci ga Allah.
Ki dinga fita yadda kika ga dama batare da kin rufe jikin ki ba wai ke zaman bariki kina daukan hakan a wayewa gare ki.
Kamata yayi yar musulma bahausa ta nuna a ko ina ta mai cikaken tarbiyane a duk inda ta riski rayuwan ta wanan rayuwan duniyan ba komai bane a gare mu.
Wataran kana gani anayi ba dakai ba lokacin ka makara ga gyaran dabi,un ka don yara sun taso sun dauki rayuwan da suka samu kanayi suna kanana.
Badon kan mu zamu daina wasu abubuwan ba sai don tunanen makomar yayan mu na yanzu da wanan tunanen na canzawan Amina a raina har muka iso gida a lokacin.
KUYI HAKKURI DA MAGANA NA YAN UWA MUNA CIKIN WANI HALI NA SAKACI DA ADDININ MU YANZU DON MUNA GANIN KAMAR WAYEWA NE.
MUN MANTA YAYAN MU NA TASOWA SUNA KOYI DA DABIUN MU MU CUSA ADDINI GA ZUKATAN YAYAN MU YAN UWA.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/14/20, 10:25 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , ,

🧕🏿8️⃣0️⃣🧕

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

Mun dawo gida mun samu jikin inna ba dadi ranan basu kwana da ita da dadi ba don maganin da ake mata allura a fara aiki a jikin ta sai ya jikin ta sakewa.
Dakin inna muka wuce don har baba yana gida ranan bai fita wurin sana,a shi ba don yanayin jikin inna din mun samu ta samu barci mun dade a wurin ta muka fito daga dakin.
Yan uwanta ma da suka zo a waje suka zauna suna tsoron shiga dakin inda take don gudun daukan ciwon da akace masu anayi.
Sai da na fito muka gaisa da su ban tsaya ba na wuce daki bamu dade da dawowa ba naji shigowan Saadatu gidan ashe dama tana nan ta fitane zuwa sayo masu abu.
Ina daki zaune da ummi na muna hira naji muryan ta tana cewa ashe bakin birni sun dawo nace eh anty Saa kin shigo ashe tace dama ina nan na dan fitane dazun .
Mun gaisa na jajanta mata akan jikin na inna ta samu wuri ta zauna a dakin ummi din tace ashe kin je wurin Amina ne birni nace eh munje ziyara wurin Amina.
Mun dade a dakin muna hira da ita tana bani labari har ta fara sana,a da fridge din ta kayan kallo kuma tun ranan aka hada mata su yanzu bata da wani damuwa ko zaman kadaici
Kiranta akayi waje ta fita na mike ina son in yi wanka dama sai ga mama ta shigo gaida mu da dawo nan na tsaya muka gaisa tana fadin ai babaku bai san zaku kwana ba ya dawo yana fada jiya.
Nace Amina tana da muhinmanci a wurina shiya naje na kwana mata daya yanzu saura kuma in tafi kauyen su ummi inyo ziyara in dawo in fara shirin tafiya don mun kusa cika kwanakin da aka bamu.
Tace au har can zaki tafi ashe nace ba dole inje in duba ma ummi yan tsofinta ba kada ta hake ni daga inda ummi take zaune tace ai ba a saki zuwa dole ba.
Dariya mukayi mata mama ne ke fadin ba a sata zuwa dole ba amma idan ta koma bata je ya isa ai mata gori ai tazo taki zuwa duba su.
Ummi dai dariya tayi da jin dadin zai tafi in duba yan uwan ta kuma nace kwana biyu zanyi a can fitan mama dakin yasa na mike na shiga bayi na watsa ruwa a jikina.
Na fito na samu shafiu ya dawo yana cika yana batsewa a falon ummi nake tambayan shi may ke faruwa shafiu yace bakomai cikin fushi.
Nace kuma ga yanayin ka ya nuna fushi kakeyi mana shafiu may akayi maka waya taba min kai nazo kusa dashi na zauna.
Ya wani turo baki a shagwabe yana fadin wai da su maimu zaki tafi indan kin tashi bayan na fada maki zan biki.
Murmushi nayi tare da dafa shi nace shafiu aikai namiji ne kuma in na tafi dakai wazai taimakawa ummi ga sana,an ta ?
Yace namiji bai zuwa gidan yayan shine akace nace kana zuwa shafiu idan anyi hutu sai yaya sani yakawo min kai hakan yayi maka ?
Dan shiru yayi kafin yace indai zaki sa ya kaini yayi mun don wallahi ina son zuwa wurin ki hutu anty nace zakazo shafiu.
Yanzun dai ka shirya zamu wurin su kawu dole gobe mukai masu ziyara kafin in koma yace ni sai kauye za a dani kun tafi birni bakuje dani ba ?
Wai shafiu yaushe ka zama haka ban sani ba bann saka da yawan hayayya ba fa ada ?
Ya mike yana fadin komai sai ace waini namijine namiji akace ba a yi dashi wallahi nima zan bar gidan nan ne.
Barci nayi ranan ban ko fito tsakar gida ba din ina son in dan huta ina jin ummi suna faman rikici da Abba a falon ta amma na kasa tasowa inzo inji may ya samay shi.
Har yaron yayi shiru ban sani ba don barcin dana koma a lokacin shigowan yaya Nura wuri na yasani tashi zaune.
Falo naa fito wurin shi mmun gaisa nace yaya Nura yaya akayi ne yace wallahi Safiya garin ne yayi zafi yanzu sam babu aiki tunda dama ya kama mutane sun mayar da kudin su gona.
Nace yanzu may ye shawara yaya ya shafa kan shi yana dan murmushi yace zuwa nayi wurin ki ki dan taimaka min da wani abu in dinga juyawa.
Shiru nayi ina nazari a raina sai nace yanzu dai ba wasu kudi nake dasu anan ba yaya gashi zan shi kauye wurin kawun ne na sai dai indan mun koma idan zaka iya shigowa Abuja sai musan abinda za ayi a can din .
Zaiyi magana na rigashi fadin barin in baka dubu ashirin duk da nasan zasuyi ma kadan amma kayi hakkuri dasu jibi zan koma ba dadewa zamuyi ba dama sai kazo mu san abinda za a yi don yaya Saadu na can.
Bva zai rasa wurin da zasu saka ba yafi wanan aikin da kakeyi a nan zaifi ma sauki nake gani idan zaka iya idan kuma kafi son zaman nan zan sama maka abin juyawa yace sai nayi shawara da mama ummi dake kofa tace shine daidai.
Na shiga daki na fito mai da dubu ashirin din na kawo mashi ya mike yana godiya ya fita daga dakin sai lokacin ummi tayi magana.
Kin san dai Nura ba kamar Sani yake ba karki saka shi a cikin harkan mijin ki ya yaudare shi bake kadai abin zai shafar mu nan zai iya shafan mu.
Nace har yanzu yaya Nura bai daina halinsa bane ummi tace ina zai daina tunda bajin maganan iyayye yake yi ba.
Shi haka rayuwan shi take a tsatsaye yake har yanzu baya ganin kowa da mutun ci a idon shi ko gidan nan ya shigo bai iya gaida mutane yanzu ma mamakin ganin shi a wurin ki ai.
Murmushi nayi nace amma duk abinda yake ummi ai bai kawo gare ki damu ko iya wanda ya shiga harkan shi yake tsayawa.
Ina dai ja maki kunne kisan abinyi tun wuri nace ummi ki bari a gwada shi ko sau daya ne kin ga ai mama bata jin dadin ganin da yaya sani kawai muke mu,amula a gidan nan ranta baya dadi nunawa kawai ne batayi.
Ba fa gwadawa a fili amma nima nasan abin yana damun ta nace ba a dukiyar uncle zan sakashi ba ai ummi nima nasan abinda nakeyi.
Washe gari muka isa garin kakan nina mun samu taro na mutantawa a wurin su irin taron da mutanen kauye kiwa wanda suke mutuntawa aikai muna a gidan.
Su yaya sani basu kwana ba suka dawo bayan sunci abi mukai sallama dasu suka tafi naji dadin kasan cewa a cikin yan uwan ummi danayi saboda yadda suke nuna muna don dukkan mu yaran ummi mukaje garin.
Mun so zuwa da ummi amma baba yahana ta zuwa don haka muka zo bada ita ba sai yamma mazan suka dawo daga gona wurin aiyukan su don da aiki noma da kiwo suke dogara su.
Sai da suka huta muka bisu daya baya daya muna gaida su a part din su najin dadin ganin mu a yadda sukaga munzo mu duka.
Mun fi dadewa a wurin kakan mu wanda tsofa ya kama yanzu har dan rankafa abu ga dogon mutum wanda ya manyanta don ko diyan shi ba yara bane balle shi tsawo rai daine daya samu yakai hakan.
Washe gari da muka tashi jumma a ne don haka kowa na gida basu zuwa gona duk ranan jumma, a ranan suke samu su dan huta a gida don yin sallah jumma a din.
Tsaraban da muka kawo masu ake ta rabawa a kofan kakan mu mace duk da ita ta haifi ummi mu ba wanda ta haife ta ta rasu tun ummi bata girma ba.
Amma ta rike su kamar ita ta haifesu yadda ta rike su a gidan nan suka fara shigowa godiya a gare mu duk mazan shaddan da ya bani na kawo masu dama na aje masu nasu.
Mun je wurin kakan mu gaida shi sai jan mu da hira yake yi yana bamu labarin rayuwa shi na baya yana kuma fada muna dan tarihin ummin da tasowan wata har auren ta a kauyen da tayi ta koma wurin gwago a garin mu.
Abba ke rikici a gaban shi yayi murmushi yace miko min shi nan khadija ta mika mashi yaron ya dauke shi tare da kara shi saman kafadan shi daidai saitin kunnen yaron ya dora bakin shi a hankali yana karato adduan daba mu san may yake fadi ba a lokacin.
Kara juya shi yayi bangaren hago ya kara maimaita abinda yayi mashi a bangaren dama ya gaba sai ya dan hura mai fuska take yaron ya zauke numfashi a hankali yake rage sautin kukan da yake yana ajiyan zuciya shikuma yana dan jijigashi a hankali saman kafadan shi har yai shiru ya lafe sai ajiyan zuciya yake sakewa a hankali.
Mudai mana kallon abinda yakewa yaron yace idan kunga yana kuka haka daukan yaro akeyi aimai kallaman shada sau uku a ko wani kunne da bissimilah zaku fara kowani sai kuga yaro ya yi shuru koda kuwa shedanune suka shafi yaro yana yawan kuka akai akai.
Nace aiko mun karu tsoho ya nisa tare da tambayana jiki na nace da sauki sosai yanzu gaskiya don ina shan magani kuma ina cin abinda zai gina min jikina ko yaushe.
Yace kin dai daina amfani da fitsarin rakumin ko don banga kin kara aikowa in sama maki ba nace gaskiya malam tunda na shanye wanda ka bani da farko ban kara amfani da shi ba kuma naji dadin shi sosai wallahi.
Yace tsiyan ku ke nan yaran yanzu baku tsaya ma magani har kuga aikin shi da kyau sai ku camza wani .
Nace tsoho ba inda zan samu ne a can kaga muna da nisa sosai yace kinzo a saa ai yau jumma a za a soke rakumi ayi tom tom din shi zan sama maki wasu abubuwan amfani da dama a ciki sai kije kiyi amfani dasu can idan kinji dasin su keda kan ki zaki aiko a kara maki wani.
Godiya nayi mashi tare da dan bashi kudin da na riko mashi duk da ina ganin basu da yawa amma shi sai washe baki yake yana saka min albarka.
Tashi mukayi daga wurin shi wanka mukayi muka shirya muka zagaya gaida dangin da suke a cikin gari
Bamu dawo ba sai yamma lis agajiye kowan mu yake abincin da suka aje muna na rana muka samu ba wani ci mukayi ba dama na bada sakon a saya min ganye da kwai da man shanu mai yawa da zan koma dashi Abuja.
Ganye nace khadija ta dan gyara min naci har dare dashi na kwanta a cikina don banji wani yunwa ba kuma.
Washe gari sai shirya muna tsaraba suke yi kin san kauye da kara wanan ya kawo wanan ya kawo sai gashi mun tashi da tsaraba mai yawa a gidan.
Sha buyu rana driver dasu yaya sani sun iso daukan mu bamu jima ba mukayi sallama dasu muka kama hanyan gida biyu da wani abu muna a cikin gidan iyayyena.
Kwana biyu yarage muna a garin sai shirya muna ummi da mama keyi nan ma dai tsaraban ake ta kawo min don duk wanda na ba tsaraba dana zo sai da ya dan samu abin da ya bani da zan koma sai dana ragewa su ummi wani abin.
Ana gobe zan koma ne da safe sai ga maimu da kuka ta samay ni wai baba yace ba zan tafi da kowa cikin su ba.
Hakkuri na bata nace zanyiwa baba magana da yamma da yadawa gida naje gaida shi yana zaune yana cin abinci mama na gefe shi na shiga wurin shi.
Gaisawa mukayi nayi mai yaya kasuwa ya amsa min cikin fara a na samu wuri na tsugun na yace kuna ta shirin komawa gobe ko nace eh baba.
Shine ma nazo fadama zan tafi da maimu da hindatu suyi min hutu idan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login