Showing 102001 words to 105000 words out of 269010 words
ta zamay maki uwa da uba ga komai naki.
May kike nema wanda wanan boyar Allah batai maki ba a rayuwan ki muma da ba uba daya muke ba may ta rage mu dashi a rayuwan mu.
Kafin in fadi wani abu sai ta katseni da cewa bafa wani abu nake so gare ta ba kawai yardan ta nake so ga bukata na akan sulaiman kawai.
Na girgiza kai har wanan lokacin fuskana yana dauke da guntun hawaye wani irin kallo nake binta da shi mai nuna tsanan abinda ta fada min.
Sai ta hau cewa ni fa yarda da amincewa yasa na fada maki da ace nasan ke ba yar hannu bace ga wanan harkan ba abinda zai kaini fada maki .
Nisawa nayi nace wallahi zan fada maki gaskiya tun wuri ki daina wanan halin tun bai zama maki jiki ba ko.
Ta mike tana cewa yau hiran namu dake ba zai yi ba do bani son mutum mai kara min zuciya akan abin da na saka gabana.
Tamike tare da nuna ni da yatsa tace i hope wanan maganan ya tsaya iya ni dake kawai a gidan nan idan naji shi a waje zamu samu matsala dani dake sai ta fice.
Kallon mamaki na rakata da shi ta buga min kofan daki garau ta fita na sauke ajiyan zuciya ina mamaki halin matan yanzu har da macen da batai aure ba ta iya zuwa gurin boka don kawai a asirirce mata yar uwar ta ina ga in ta samu kishiya kuma ?
Tun wanan lokacin mukai sanyi ni da Fati Faiza tayi tayi tasan may ya hada mu bamu kaman da amma naki fada mata sai ce mata nake yi kila ta samu wata kawar ne a waje.
Yanzu anty bata faye zama a gida ba suna aiki sosai a wurin aikin su don haka sai kula da gidan ya dawo hannun mu.
Duk da dai sauran ba wani abu sukeyi ba sai ni da mai aiki zamu aiwatar da komai kafin masu gidab su dawo Faiza irin mutanen ne masu fuska biyu.
Amma bayan haka ta na da kirki sosai amma sai na fahinci akwaita da aikin ganin ido abinda bata sani komai da muke a gidan yana kunnen anty.
Ta san yadda kowa ke rayuwan shi a gidan ido kawai ta saka muna tana kallon kowa da halin sa ranan da rana anty tai muna dawowan bazata a gidan .
Ina daga ni sai mai aiki dake wankin kayan ta nikuma ina muna girki da zamuci ga yaran ta zaune suna kallo a falo na dafa masu indomie kafin an gama hada abincin gida.
Su ko faiza tana barci a dakin ta tayi dadaya a saman gadon ta Fati kuma ta fita yawan ta sai in yai mata dadi kafin yar ta dawo aiki take dawowa gida.
Tana shigowa ta samu yaran na cin abincin da na aje masu suke ci take tambayan su suka ce anty safiya ne ta dafa muna.
Jin motsi yasani fitowa ina yarfe ruwan da na daureye hannu a hankali naga itace ashe ta dawo nake mata sannu da zuwa.
Tace sannu da aiki safiya shiya yanzu sai in fita gidan nan hankalina kwace ba tare da fargaban wani abu ba ga yaran nan dako ban da kwanciya hankali idan na barsu a gida don kamar ban barsu da kowa bane saboda basu samun kulawa yadda ya dace..
Har na gama girki na kawo ma anty nata sai mai aiki ta shigo ta samay ta a zaune falo ta fara gaisheta da dawowa.
Tace yanzu na gane zuwan safiya gidan nan yai maki dadi don duk kin tatara aiki kin bar matayi daidai ina kawowa anty ruwan sha naji tana fadin haka sai nace a a anty tare, , , ,
Hannu ta daga mi alaman in shiru naja bakina naci gaba da jera mata abincin tana may ci gaba da fadan da takewa funke mai aikin ta.
Sai ga Fati ta dawo nan tabita da harara simi simi ta shigo tana kamay kamay fada tai mata sosai ranan har ni din bata bari ba.
Bayan kamar kwana hudu dayin haka kowa a cikin mu ya shiga taitayin shi don gudun laife gare ta daga ni sai Faiza dake charting a wayan ta.
Sai gata ta shigo gidan sun dawo unguwa da yaran zaune nake zugun nayi tagumi nayi zurfi acikin tunanen duniya.
Sai muryan ta naji daga sama a kaina tana fadin Safiya wallahi zamu bata dake a gidan nan matukar baki daina damun rayuwanki da tune tunen marasa tushe ba ke kadai ke gidan nan ne da kika kasa sake ranki cikin yan uwa kiyi walwala.
Na dago kai da sauri ina kallon ta a lokacin ya shigo da kaya niki niki da suka sayo ashe tare dashi suka fita unguwan .
Nisawa nayi ina mata sannu da zuwa sai dai bata amsa ba sai ci gaba da fadan da takeyi min kamar ba magana yake yi ba don hausa shi da baya fita da kyau yace.
Bata da lafiya ne ko may ke damun ta haka din ?
May kuwa uncle na rasa gane hankalin yarinyar nan tun da tazo gidan nan taki ta sake jikin ta kamar kowa sai zama tana yawan tunanen banza da wofi ita kadai.
Zaune yakai saman kujeran da fuskantar mu tare da aje kayan da suka shigo dashi din tace kamar wanan yarinyar da bata wuce 19 years ba zata saka ma kanta tune haka.
Jinayi yace keko may yasa kike haka din tunda antyn ki bata son yadda take ganin ki ba kamar kowa ba a gidan yana magana yana kallo na .
Yaci gaba da cewa don Allah ki kwantar da hankalin ki ki daina damun kanki koma may ye a ranki ki fitar dashi don tunane yana iya kawo maki illa a lafiyar ki.
Ya maida kallon shi ga anty yace bata dade da zuwa nan din bane ko may ko gida take tunane haka ?
Tsaki tayi tace wani irin dadewa kuma ai duk ta rigasu zuwa nan halintane hakana din kawai dason shiga damuwa.
Shi ya kawar da maganan da dauko maganan bude gidan shi da suke shirin yi yace sai in an gama tsarawa zai zo mata da yadda akayi ya mike yana shirin wucewa sai lokacin tace dashi ba zaka tsaya ta hada maka fruit din ba.
Yace no barshi kawai zan tafi don naga mai hadawan bata cikin hayacin ta mikewa nayi da sauri nace barin hada zan iya ai.
Ban dauki lokaci ba na hado mai nakawo yace dashi zai tafi don baida lokacin tsayawa yasha a nan din, har waje suka fita da anty sun dade sai gata ta dawo ciki.
Lokacin muna zaune da diyan ta da Faiza tace in bude ledan da suka shigo dashi gidan in fitar da kayan dake ciki.
Nan Faiza ta tayani fitarwa muka fitar da kayan wanda yawanci duk na twins din tane tufafi da kayan makulashen yara tace mu diba in kai saura dakin su.
Bata barni haka ba dana dawo na zauna sai da ta bini da nasiha kan in cire damuwa a raina Faiza ke cewa ta rasa may nake wa yawan tunane hakana.
Ba laifi nayi korin ganin na fitar da komai a raina sai dai ba abinda zan iya fitarwa kai tsaye bane yadda take nufi amma na dan rage yawan sa ma kaina damuwan da nakeyi din.
Mako biyu tsakani ranan muna zaune dukkan a falo sai ga ta ta sauko daga sama ta zauna take cewa Fati ta shirya mata kayan su yan biyu zata Abuja gobe tafiya ya kamata.
Sai ta juya gareni tana cewa ke ma Safiya ki shirya don dake zan tafi saboda yaran nan ba zasu barni ba inyi abinda ya kaimu da sauri Fati tace anty nima in shirya ina sin zuwa Abuja wallahi.
Tace da Safiya zan tafi ko ita don yara zan tafi da ita Sulaiman zai yi bukin bude company a can da gidan da ya saya a take fati ta shiga rokon ta wai taje da ita.
Tace karatun ki fa fati kina fa wasa da karatu gashi kun kusa rubuta jerabawan fita ke bakiyi ma kanki fada ne wai kamarki har yanzu a secondry school ?
Nan ta turo baki gaba tana fadin na dai gane kin fi son safiya damu a gidan nan komai sai kice safiya ita kadai.
Tace dole ne in ce safiya don tafiku hankali da tunanen abinda ya kamata ko ruwa kuna iya ba mutum ne in ba ya kama maku dole ba.
Faiza ma ta marairaice mata saida tace duk su shirya mu tafi tare sannan aka samu lafiya don da Fati ta hau sosai ga maganan.
Kowa ya shiga shirin tafiya don tace sako zamuyi mu tafi kala uku kawai na dauka koshi dogayen riguna ne kawai na zaba.
Tun da safe muka kama hanyan abuja a mota mukai tafiyan don mijin ta baya nan suna ruwa wurin aikin shi basu fitowa sai bayan watanni a ruwan shiyasa ma bai faye zama a gidan ba.
Gidan su na abuja muka sauka wanda shi mijin tane wai yake dashi don harda funke mukayi tafiyan bamu bar kowa a gida ba.
Gidane mai dauke da dakuna hudu da falo daya na maigidan inda ta zauna a ciki sai dayan wanda fati da Faiza zasu zauna ni da yara tace mu shiga guda sai mu bar ma funke na farin shigowa wanda dama saboda masu aiki akayi shi.
Ba wani hira don kowa na da gajiya tare dashi wanka kawai mukayi sai abincin da aka kawo muna daga wani gidan abinci ina jin Faiza da fati na ta santin abincin don dadin shi niko takura bai bari naci sosai ba don na lura dukkan su biyu kamar yanzu sun tsane ni a gidan don yawan nuna mani kulan da maigidan namu takeyi ko a gaban kowa.
Na riga kowa shigewa ashe sulaiman din yazo gidan bayan na shiga barci nan Fati ta kama rawan kai saida anty ta tura ta ciki ta basu wuri.
Washe gari tun da safe da ta fita bata dawo ba sai wurare karfe hudu ta dawo gidan nan ma bata huta ba don wasu suka zo suna tsarare dasu.
Har na kwanta sai ga anty dakin na mu hannuta rike da tasbaha tana ja shiyasa nake son ta don wayen wata da tsabgogin gabanta bai hanata yin ibadan ta sam.
Mikewa nayi zaune daga kwanciyan da nake ta kalle ni tace wai ko kin dauko kayan kwarai kuwa Safiya don taro ne na masu hannu da shuni za a yi.
Nace anty na dauko wanan riga ne da kika sayo muna ranan na fadi tare da kallon ta don jin may zata fada gamay da shi.
Cike da tsukana tace min Safiya ai da kin tona min asiri a cikin taro da sai in nuna ba tare dani kike ba a wurin kawai kisa mutane su raina min da wayo ?
Dariya nayi itama abin ya bata dariya don jin nace anty wanan riga mai balain kyau.
Tace kin ga ni yanzu ma fita nazo kirakani muyi dama nayi tunanen hakan ki shirya ina fitowa yanzu zamu fita da faiza ba zan je da wanan mai rawan kan tsiya ba ta bani kunya.
Ashe harta fada ma Faiza ko koda na fito faiza na falo zaune tana kallo hijjab da dogon riga nasa ta kalleni ta wani kwashe da dariya .
Sai kuma tace min mutumiyar na ciki tana fushi wai za a fita damu bada itaba kafin in magana sai ga ta tafito tana saka ma kofa key tare da kiran Funke tana cewa ta kula mata da yara da sukai barci tun da magariba.
Na muka fita tare da rufo kofan gidan mukai ma Funke sai mun dawo wata mota baka muka samu waje a kunne yana jiran fitowan mu.
Baya muka zauna inda sai wani kamshi da ban taba ji ba ya daki hancina ga sanyi AC mota suka hade suna bada wani irin yanayi a motar, ita ta zauna gaba tare da driver muka kama hanya fita daga gidan kallon titi nakeyi inda naji Faiza tace ina wuni yaya Sulaiman .
Sai lokacin na dawo daga tunanena nace dashi ina wuni ya amsa muna a tare lokaci guda anty ke ta hira sai eh ko aa yake ce mata.
Tafiya mukayi mai nisa sai gamu bakin wani shago maigirma anan muka firfito inda muka barshi a cikin motar zaune muka fara shiga mu da anty.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , ,
🧕🏿3️⃣5️⃣🧕🏿
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA DON BA A YAFE MAKI BA HAKKIN KARANTAWA BA BIYA.
Tunda nake ban taba zuwa wuri irin wannan ba a rayuwa na sai dai ban nuna ba saboda natsuwan da Allah yai min.
Sune a gaba ina binsu baya a hankali anty tace mu diba mu gani sai ban tafiba nabi bayan anty din wasu jakka da ta kalma take dubawa bata san ina bayanta ba.
Sai nace kai anty wanan kayan zaiwa su yan biyu kyawo sosai ta juyo da sauri tana cemin har kin duba ne?
Jin nai shiru yasa ta juyowa tana fuskanta tana tare da cewa mai kika zaba ne nace ban dauki komai ba kai ta girgiza kawai taci gaba da daukan abinda take so.
Tafiya takeyi tana fadin sai ki zabar ma diyan naki kayan a tare mukaje wurin kayan yara na fara duba masu sai kuma na gaza itace tai ta zama musu kalloli masu kyau.
Batai min magana ba sai wucewa da tayi layin riguna ina biye da ita can ma zaban taitayi tare da atamfofi.
Ni dai har muka gama a shagon banga sulaiman din ba sai nai zaton ya ajemu ya tafi ne to wa zai mai damu gida daren nan haka.
Acan wurin biyan kudi muka hade dashi bai sai komai ba sai turare guda biyu ya dauka bazaka ce tare muke dashi ba yadda ya nuna a wurin.
Ni dai kafana ya gaji da tsayawa sai na fita daga shago na samu bayan wani mota na jigina jikina dashi.
Sun gama suka kwaso kaya niki niki suka fito zuwa motar na tako inda suke na samay su ta dago tana ceman yayi da ake sakayan a both din motan da muka zo dashi.
May yasa kika fito daga ciki nace na zata magana zasuyi ai shine na basu wuri tsaki taja kwai tana bude kofan motan muma muka nufu motar muna budewa.
Har muka iso gida ba wanda yai magana a tsakanin ni da Faiza sai da motar ta tsaya ne muka fito nan muka fara jidan kayan zuwa ciki dasu sai a lokacin naga ashe ba karamin sayaya mukayi ba .
Dakin anty muka nufa dan kai kayan can amma sai tace mu zube su a falo na ta zauna tare da jawo wani laida sai naga ashe nama ne gadade suka saya a wurin .
Tana fitar da kayan tana cin nama hankali kwance ta miko min wani laida shake da kaya tana cewa ungo naki matsoraciya kawai ta kuma mika min wani karamin laida da kayan sanyi da naman ciki faiza kuma ta dauki nata zuwa dakin su kowa ya shige muka kashe wuta muka watse wurin.
Da safe kowan mu ya makara don haka bamu fito da wuri ba ni dai ina kwance bayan nayi sallah sai na koma barci.
Banyi nisa da barcin ba sai ga anty ta shigo daki da hijjab din ta tayar dani tayi na mike zaune tare da gaisheta da kwana takalleni tace safiya kinyi sallah kuwa ?
A girmamay nace nayi sallah anty tun dazun sai tace madalla tashi mu fita gidan nan tun yan bakin nan basu tashi ba mu fita daga gidan nan maza ki tayar min da wa yan nan sarakunan barcin yanzu mu tafi.
Har muka gama muka fice daga gidan basu sani ba wurin gyaran gashi suka tafi don har dani anyi mawa ina ban so amma sai da anty tasa akaimin gyaran na koma kamar bani ba.
Ni kaina nasan gyaran ya fitar min da kyaun surar fuskana don ban taba gyara irin haka ba bamu dawo gida ba sai shabiyu da rabi muka shigo gidan.
Mun samu sun cika fam sai dai ba mai iya yin magana a cikin su dole kuma suke gyashe mu da dawowa .
Nan muka zube a falo tare da muna neman abinci ina yawan mamakin yadda sam anty bata kyaman mu,amula dani kamar yadda gidan mu suke gwada min.
Sai da muka gama ne sai Faiza ta kula da gyaran gashin da akai mun din tace wai dama anty wurin gyaran kai kuka tafi ba tare da muba.
Tace fuska gimtse eh idan kun shirya driver yana waje sai ya kai ku kuma bata da daman da zatai mata wani korafi ba.
Sai harare harare suke aikamin a fakaice bandai kula suba anty ta shige dakin ta sai lokacin Faiza ta samu yi min magana akan fitan mu nace nine nace zan bita da zata fita tace idan