Showing 63001 words to 66000 words out of 269010 words
Wani magana da ta fada sai da yaya saadu ya kadu bayan tafiyanta ne sadiya ta taimaka min don mu gyara gidan mu mai da komai inda yake.
Kuka nake ban iya aiwatar da komai ba a lokacin sai gasu sun shigo gidan da shida dan uwanshi.
Sun zauna suna fuskantar juna yaya saadu yace dashi matan bariki dama haka suke su raba ka da ta kwarai su kuma daga karshe su guje maka.
Kamayi arziki bata kai ga kore maka mata ba ta tafi ya dago ya kalli dan uwan nashi ai ba tafiya tayi ba barazana ne kawai.
Yaya Saadu yace yar bariki ne zata iya dawo ma rayuwana in yau ta ga dama ko gobe sai dai ka sani.
Yarinyar na Safiya yar uwan muce jinin mu ne ita kamar yar cikin mummy take a wurin mu infact dai kasan wanan auren naku anyi shine don kara zumunci.
A ganina bai kamata ace abinda iyayye sukai maka gata akan saba shikake wullakantawa.
Na tabbatar da mahaifin yarinyar nan na kusa ko yasan halin da yarsa take ciki da tuni ya raban auren ku da ita.
Ya kamata ace Safiya ta samu kulawan ka fiya da komai a gidan ka bata isa ta hanaka barikin kaba amma kabata kullawa yadda ya dace don kauce ma shiga hakki.
Nasan da mahaifinta yasan halin da yarsa ke ciki a gidan ka da duk wanan abin bakai ga yinsa ba.
Don basu san halinka na boye ba mummy ta rufe massu kokai waye ta aura maka karamar yarinya da yaci ace yanzun tana karatu ne.
Please Ahmed ka gyara rayuwan ka duk wani abinda kasan yana kawo nakasan rayuwan ka nesance shi.
Ba abinda ya zamo ma dan adam dole a rayuwa mussamman abinda zai nesantakan da ubangijin ka yazama dole ka yakeshi a ranka.
Musamma giya da mata ba alheri bane ga rayuwan dan adam ba dole bane ba kuma inda yazama ma dole sai kayi shi.
Don Allah bros ka rabu da wanan rayuwan ka rugumi matarka ka rike yarinyan nan amana zaka ga yadda rayuwan ka zai canza duk wanda ya samu mace kamar safiya yayi saa a rayuwa shi ga tsabata ga hakkuri da biyyaya.
Ya sa hannu ya dafe kanshi kamar maganan yana shiga zuciyar shi can ya lumshe idanuwan shi yana hango kyakkyawan fuskan na da suran da Allah yaimin da natsuwa da hakkuri.
Yace kai baka ko gudun ka dauko maku cuta ka manna wa yar mutane matar nan fa baka san iya mutanen da take hurda dasu ba har wata kasa take zuwa.
Yaji zuciyar shi da jikin shi yai sanyi saboda maganan da dan uwanshi ke fadi gaskiya ne ko abokan shi sun sha fada mashi hakan.
Gaba daya jikin shi yaji yai sanyi amma kuma yasan abu mai wuyane ya iya rabuwa da lilliya ko ya rabu da kowa bai iya rabuwa da ita wasan dadi.
Ya kalli yaya Saadu yace na gode daka tunarta dani wasu abubuwan da na manta dasu a rayuwa.
Yaya saadu bai tafi ba sai da ya tabbatar da ya daidata komai a tsakanin mu yabar gidan .
Abinda bai sani ba shine na kudiri aniyar kwatar kaina daga gare su bazan kara yarda da irin cin fuskan da yake min ba agaban matan bazan shi da yake kwasowa.
Kwana biyu kamar komai ya lafa sai dai a raina nasan kwanton bauna yayi kawai na kwana biyu.
Yana kawo min abinci kai da kai kuma idan zai fita zai sallamay ni kuma idan ya dawo nakan taso daga dakina ko nabar abinda nake yi nazo na gaida shi da dawowa.
Wata rana zai fita na tambaye shi zuwa wurin maman biyu indubata kamar ba zai barni in tafi ba sai dai kuma yace kada in dade.
Na gama shiryawa na rufe gidan na kama hanyan gidan ta nayi saa ta dawo wai ashe bata garin duk wanan dadewan da tayi.
Take tambaya na ko nazo bata nan ne sai nake fada mata irin kullen da yasani da dauko Lilliya da yayi ya kawo gidan.
Da irin horon da na sha a wurin su har yaya Saadu yazo ya kwace ni a hannun su daidai lokacin da nake ganuwan shan wahalan su.
Ta nisa tare dacewa safiya wanan mijin naki bariki ta aure shi rashin sani yasa mahaifinki ya nace da ki zauna dashi hakana.
Amma wanan da kike gani tuban mazuru yai maku kawai may yuyuwa ya canza mata gidana suna haduwa baki sani ba.
Nace inma gida ya canza mata baida may ni ba don ban gani ba abinda sukeyi bisa ga yadda suka zauna min gida ana iya shege a gabana.
Nifa anty yanzu cikin nan ne kawai matsalata badon ciki ba da duk abinda baba zai mun sai dai yai min ba zan zauna ba.
Sai dai nakan tuna furucin baba sai jikina yai sanyi da yake cewa indan aurena ya mutu in tabbatar da zaman ummina ma ya kare a gidan shi.
In badon wanan ba aida tuni na gudu na koma ga iyayyena ko don maganar kine wallahi don da dan uwanshi kemai magana ya rabu da Lilliya cewa yayi.
Wai abinda yasa ba zai rabuda itama ba sun jima tare ni tun baida komai suke tare tabar maza da yawa take zaman shi shi kadai.
Wai cewa yayi har musulunta tayi saboda shi saida sukai alkawari da ita cewa bazai wullakantataba kuma ba zai taba rabuwa da ita ba shi dalilin da yake duba.
Sai dan uwan ke tamabayan shi yana ganin Lilliya ta musulunts ne matar da ko shiga irin na musulmai batayi kuma ita bata daina hurda da wasu mazan banza ba har yanzu.
Kai amma mijin nan naki wani irin soko ne wallahi indan ka gan shi a fuska kamar mutumin kwairai inji anty.
Tace yanzu shi baiji kunyan fadar wanan dalilin nashi na bazan ba shi watau baiyi tunanen harcin da iyayyen ki sukai mashi ba sai na wata matar banza can.
Nace ai haka dan uwan ya fada mai idan yana son zaman lafiya da kwanciya hakali sai ya rabu da matan bariki.
Sai cewa yai mai wai bayajin zai iya rabuwa da lilliya ko ya rabu da kowa don baida matsala da ita tana binshi shi sau da kafa tana mashi komai ko wanan akasi aka samu suka sami matsala.
Kanin yace mai aiko ya zama dole ya rabu da ita don farin cikin gidan shi nace kin san may ya cewa kanin ?
Wai mau zai sa kanin na shiga mai harkan shi wai ai lilliya ma tarsa ce don haka zai zauna da wacce ya ga dama a cikin mu ya saki wacce yake son saki ko kuma ya zauna da mu dukkan mu.
Sai cewa yayi dan uwan ya rabu dashi kar ya caja mashi kwakwalwa don yana bukatan hutu tare dashi.
Na kinga kenan bazai iya rabuwa da ita ba ni ko yana iya rabuwa da ni inya so.
Haka dai dan uwan ya lalaba shi har suka samu suka rabu lafiya dashi ya wuce in ba haka ba ranan nasan ba karamin tashin hankali za a yi ba a tsakanin su.
Tace kin ga ni yanzu so nake ki kwantar da hankalin ki ga komai ki kula da kanki sosai don ki haihu lafiya.
A hankali na daga mata kai alaman na gane ta kawo kudi masu yawa ta bani da zan koma tare da kwantar min da hankali.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , ,
🧕🏿2️⃣0️⃣🧕🏿
YAR UWAN NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , ,
Abin yai min yawa a tare da ni ga yunwa ga ciwo ga ciki sai yar dadiron gida da tazo ta kakace gidan da zama .
Ga miji dani da babu duk daya a gare shi bai san cina ba bai san sha na ba ko ciwo gashi har wanan lokacin maman biyu bata zo gidan mu ni kuma ban fita ba.
Don da zaran nafita da ya dawo fada mai take yi ya samay ni yaita jibgana sai ya ga dama ya yabar ni.
Suna zaune falo sun sayo kaji gassasu suna ci ga kayan shaye shaye nan mai sanyi agaban su wasu ansha wasu ba a taba ba.
Kayan abincin da maman biyu ta bani duk sun kare banda komai da zanyi dabara dan kitson da nakeyi ya hanani wai ana cika masa gida.
Jin motsin su a falo da dariye dariyen su yasa ni fitowa na samay shi, da farko da nai magana tankar bai jini ba.
Sai da na kara cewa yaya wurin ka fa nazo tun jiya ban ci komai ba a gidan nan sai ya dago ya dubeni wani irin yai karfin halin daga Lilliya daga jikin shi.
Ido ya zubamin na sake cewa tun jiya da safe banci komai ba a gidan nan, Lilliya ce ta sake kwanta mai a jiki tana wani iri da idanuwanta.
Yai karfin halin sake daga ta daga jikin nashi again yace baki ci abinci ba mai kike jira da baki dafa ba.
Nace wanda ka saya min ya kare sai ya juya ida take zaune yana kallonta ya zuba mata ido yana kallon ta.
Yace baby kin san ba a horo da yunwa a bari ta dinga dafa abinci tunda akwai shi kuma ke ba damuwa da dafawa kikayi ba.
Ta wani ya mutsa fuska tace abata badon halin ta ba don albarkacin wanan baby dake jikin ta.
Tsayawa nayi ina masu kallon mamaki abincin ma da zanci wai sai ya nemi yardan karuwasa idan ta yarda a bani indafa.
Ganin ban wuce ba yasa yace bakiji ba abinda tace kinci albarkacin cikin jikin ki tace eh don kuwa babyn dear na ne kinga kuwa bazamu barshi da yunwa ba.
Kije mana ya daka min tsawa yana harara na wai na wuce mana tunda an bani na kalle shi nace haba yaya kaji tsaro Allah.
Yanzu cikin daren nan karfe goma ya wuce wani abinci kake son na dafa inci a wannan lokacin.
Ya zuba min ido yana kallona da idanuwan shi da sukai ja amma ya kasa fadin koma sai bina da kallo da yake yi.
Sai a lokacin Lilliya da ke jin mu ta dago jajayen idanuwanta da suka rine tace wannan abinda muke ci kike so komay
Kasan mai ciki da gwada zai yiyu kamshin shi taji tafito daga dakin ta, idan har shi ko kika biyu wallahi kwalelen ki idai wannan ne.
Kofan da aka turo ne yasani juyawa bani ba harsu din suna diban kofan don suga mai shigowa lokacin.
Bakowa bane illa yaya saadu ya shigo gidan fuskan shi a daure da alaman har yanzu yana cikin zafi da maigidan.
Tunda yai sallama ya shigo gidan jikin shi ya bashi cewa akwai wani tsiyan da aka shukawa a gidan.
A hankali murya a sanyaye na gaida shi da zuwa sabanin yadda na saba gaida shi abaya idan ya zo.
Tambaya na yake a gagauce yana yi yana kallon inda suke zaune a ciken hasala maynene matsalan safiya may sukai maki nace , ?
Ganin shi yasa kuka da banyi niyar yiba yazo min a lokaci guda .
Durkusawa nayi a gaban su ina tsananin kuka kamar na fita yacina Yaya Ahmed ya daga zaune ya zuba min idonsa da suke jawur , ya kasa fadin komai, .
Kumshin naman kazan daya rage guda daya basu taba ledan shi ba shi ya dauka ya miko min yana fadin.
Indai wanan ne kikewa kuka don ba a baki ba gashin nan kije kicke baby bari zan saya maki wani kafin mu kwanta.
Ban karba ba kuka kawai nake yi ya sake cewa karbi mana kibani wuri da kukan nan naki hakanan.
Yaya Saadune yace safiya in nama kikewa ki karba gashinan ya baki sai na dan tsagaita kukan da nake yi nace yaya tun jiya ban ci komai ba a gidan nan .
Na fada mashi yace wai wanan ta bani indafa yanzu yaya yaushe zan dafa har inci da daren nan .
Na juya ina fuskatan shi nace yaya ina cikin wani babban matsala da tashin hankali da ban taba tunane ko tsanmanin zan shige shi ba.
Yaya Saadu ka mai dani gida inyakani baba zai yi kan naki zama gidan dan yar uwanshi sai dai ya yankani a kan hakan ko dabba aka daure a gida ana bata abinci taci balle mutum.
Yaya saadu kai kadai nake jin saukim rayuwa a wurin ka sai kuma maman biyu da tai min tsaye, .
Ita ma bakin ciki da takaici ya sa ta dauke kafanta da zuwa dubana bani da kowa dake zuwa dibani sai kai da kazo yau din nan.
Ya tausaya min sosai yace kinyi hakkuri safiya tun jiya na dawo motana ne keda matsala sai na tsaya gyara da na dowa nike tambayan mummy ke sai take fada min wai kina nan da ciki kuma kuna samun matsala.
Ya juya wurin dan uwanshi yana cewa yanzu kai rayuwar daka zabawa kanka ke ga ka dauko karuwa har cikin gidan kana sunna kana fifita ta sama ga matar ka.
Yaushe zaka girma kasan ana mutuwa ayi hissabi wai har ace kace matar ka ta zubar da cikin da kuka samu wai har ka tsaya kana mata wullakanci akan hakan.
Wanan matar banzan daka dauko ka kawo mata gida fa a matsayin may take ita in ma har zakuyi abin ku , ku tsaya can kuyi inda bata ji balle ta gani.
Yanzu bakajin nauyi da kunya kana ciyar da matar banza abinda kake so ka kasa ciyar da matarka ta sunna ga ciki ga bakin cikin ka da yunwa yaya kake son tayi.
Tsawa ya daka mai yace ya isheka Saadu ya isa haka gidan ka ko gidana ka sani matar da kake kira da matar banza matatace.
Mata mata fakace yai masu wani kallo yana tafa hannun shi yace dakyau wanan ce matar kake nufi ko may .
Tun wuri idon ka ya bude akan wanan ya nuna Lilliya yace wan yan kaddangarun bariki masu ma mutum shigo shigo ba zurfi.
Yanzu ka dubi wanan yarinya wata take dashi garin nan bayan mu bata da kowa Allah ne gatan ta kaine gatan ta amma ga ciki jikin ta kuma ga horo da yunwa.
Nice na katse su nace yaya bansan yaya zanyi da matsala ta ba ya zama wajibi na zubar da cikin nan dake jiki na.
Gaba daya suka dubo ni nace shine kwanciyan hakalina a yanzu ina ni kadai ban san yaya zanyi da kaina ba ina ga mun zama mu biyu nan gaba.
Na san idan na zubar ina da daman yin wasu abubuwa , ban kai ga fadin abinda zan fada ma sai naji yaya Ahmed yace duk kika taba cikin nan a yanzu bakin auren ki.
Nai mai wani irin kallo na juya ina fuskantar shi nace tsaron mutuwar aure na shine zai hana ni fitarwa ba, indai zubarwa zai kawo min kwaciyan hankali..
Matsala ta guda shine baba don nasan bazai barni in zauna mai gida ba don ya rantse kan haka.
Tausayina ya kama shi baisan lokacin da idanuwan shi suka kawo hawaye ba ya kalli wan nashi da yake hassale shima yana sauraren mu .
Wani kallon yake min ga alaman yunwa a tare dani da rashin kwaciyan hankali, kai bashi ba ma duk wanda ya ganni sai ya tausaya min saboda nayi kankanta da shiga irin rayuwan nan.
Shi kanshi lokaci na farko da yadan tausaya min kenan a gidan don wanan shine lokaci na farko a rayuwan shi da yaji ya tausaya min ya sake kallona ina cikin kun ci da tashin hankali.
Shiko yaya Saadu wani irin radadi da bacin rai ya dinga ji a zuciyar ji yake kamar ya samay su yai ta dukan su a lokacin.
Do yana tausaya min ya son abani kulawa yadda ya dace amma wan nashi yaki ya saurare shi.
Ganina da tayi cikin wanan halin kuncin fa ciwo ga yunwa da bakin ciki ya fi komai bata mashi rai.
Ya kasa jure gani na cikin wanan halin ya fita waje ya barmu a yadda ya samay mu shiko gogan harara ya watsa min yace.
Ban san abinda yasa kike son hadani da dan uwa na ba a dalilin ki bamu shiri yanzu da shi.
Sai liliya tace munafunci mana munafuka wai harda cewa zata zubar da cikin jikin ta da da akace ki zubar uban wa ya hanaki zubarwa.
Ke kilaki rufe ma mutane baki don ba a kasa dake ba a zancen nan kibar masu magana suyi.
Nan cacan baki ya kaure tsakanin mu don bazan in mata bane ko banza tafini karfi ga tsayi ga komai turwa kawai nakeyi ina maida mata martani ganin shi zaune.
Shiko gogan taba ya jawo ya dinga kunnawa yana zukewa yana fesar da hayaki sama kwakwalwan shi ta dinga caji yana neman mafita.
Yaya Saadune ya dawo ya