Showing 174001 words to 177000 words out of 269010 words

Chapter 59 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13348

da sai kin dauko abinci a gidan ki kin kawo muna muci da sauran abin amfani.
Don haka ma kin madaiji abinda ya fada wai na kaso maki su duka idan mun fita da sauri naji tace waneni wanan kudi yai yawa da kashewa yar nan.
Haka dai na lalabata ta shirya driver ya fita damu mu uku da zara muka fita gwago batayi niyar a sai mata abin kwarai ba so tayi ta dunkule kudinta ta koma gida dasu.
Amma naki yarda sai da na sai mata abinda naga zasuyi mata amfani idan ta koma da tsaraban da zata kai ma mutanen gida.
A gajiye muka dawo gidan sai dan abin motsa baki da muka sawo muka zauna nan mukaci muka kora da drinks zarah ta mike ta shiga dakin ta tare da abinda na sayo mata a fitar namu.
Bayan mun huta na dora girki na dawo wurin gwago na dubata tare da dan taba hira na koma ban sake dawowa wurin ta ba saida dare bayan na gama komai kafin ya dawo don ranan yayi dare bai dawo da wuri ba na fara hada mata kayan ina mata bayanin komai da wanda na sayo masu mama Jummai zata kai masu tsara da yaran su.
Sulaiman ya dawo gidan da alamun a gajiya ya dawo don tun bai shigo gidan ba ya rage sassauta tie di wuyan shi tare da balle rabin anineyan gaban rigan shi.
Sannu da zuwa muke mai daga ni har gwago yana amsawa da kyat yana kaiwa zaune yace gwago ana nan anashiri ko tace kaidai dan Albarka sannu da kokari wanan irin abin arziki haka mai yawa baka gajiya da dawainiya damu ?
Yace kai gwago ai albarka ku muke nema ko yaushe don abinda muke nema yayi albarka tace haka nane ubangiji ya kara rufa asiri Allah ya kara daukaka da nisan kwana .
Ya amsa cikin jin dadi da amin gwago abinda muke nema ke nan gare ku addua da fatan alheri ya juya inda nake tsaye ina saurare su bayan na gama hada mata kayan.
Yace madam yaya gida yana mikewa tsaye yake fadin haka nace Alhamdullahi yaya gajiya aiki yace not bad nabi bayan shi muka fita tare har zuwa dakin shi dauke da briefcase din sa dana karba.
Muna shiga dakin ya zube saman gado gaba dayan shi na aje na juyo ina kallon shi bayan na aje jakkan a ma ajiyar shi takowa nayi zuwa wurin na duka a hankali na fara cire mai takalman dake kafan shi tare da safa sai naji ya sauke ajiyan zuci bandaki na shiga na hada mai ruwan wanka.
Na fito still yana kwance a yadda na barshi ga ruwa can ya hadu uncle na fada mashi ina kokarin fita dakin don na dora ruwa a kattle.
A lalace naji muryan shi yace madam na juyo da ina kallon shi yace da wanan yarinyar kuka fita sayayya dazun ?
Nace eh zarah ko ?
Sai naji yayi gajeriyar murmushi yace I know it dama mikewa yayi zaune bai bi ta kaina ba ya fara kokarin cire kayan shi.
Ya barni tsaye ina jimamay tambayan shi gare ganin baita kaina yasa na fita dakin naje yin tsabgan gabana.
Bayan ya fito yaci abinci bai dade ba ya koma dakin shi tun bayan gama kallon news da yayi tare da cin abinci.
Nima sai banyi nawa ba na gama na samay shi a dakin amma yana waya a lokacin ga yadda na fahinta kafin in shigo fada yakeyi a waya amma ina shigowa sai ya rage sautin fadan shi tare da fadin na fada maku bazan dauki wanan halin ba.
Wuce shi nayi na dauki flask din na tafi daga dakin har na dawo waya yake na aje na samu wuri na zauna a bakin gado wayan ya kashe yana mai sauke numfashi tare da wurga wayan saman gado ya shiga ban daki nikan kwaciya nayi kafin ya fito.
Banji fitowan shi ba sai muryan shi da naji yana fadi daga bayana don may kika dauki yarinyar na kuka je sayayya da ita?
Na juyo da sauri yana goge jikin shi da towel nace uncle naga zamu barta gida ita kadai ne yace a harzuke ku barta mana sai may?
Ai dama bari nayi kisan halin su da kanki basai nayi warning dinki ba yanzu kin ji abinda tayi ta buga waya tana cewa wai kudi nake sakar maki kamar may don ko gwago da zata tafi wai ba karamin kudi na bayar ba akatafi kasuwa mata sayayya.
Ban san lokacin da na mike zaune ba yace yes dama na sani kadan daga cikin aikin su ne wanan.
A mairaraice nace uncle wani abu yafaru ne ?
Ya faru mana daidai lokacin da yake hawa saman gadon yace waya tayi gida wai take fada masu a hankali nace Zarah din yace dama may ya kawo ta ?
Shiru nayi a raina nace wai rufin kofa da barawo ke nan ashe idon su hajiya ce Zarah ban sani ba ashe da munafuka muke zaune a gida aiko nawa ya ya samay ni.
Tunanen may kike yi dama baki san ma,anan zuwa da ita da uwarta ta matsa ma hajiya sai munyi da ita ba.
Aisha ta fada min komai tun can hannatu ta fada min komai amma tunda naga ke kina da raayin zama da ita yasa na kyale sai tayi maki.
Da wanan bakin cikin na kwana a raina na Zarah da safe da na tashi bayan nayi sallah naje muka gaisa da gwago ban tsaya ba kitchen na shiga don dora breakfast.
Sai na samu har Jonh ya shigo yana yayanka kifin da zaiyi ferfesu dashi don shine mai muna abinci ni kuma kazantar cin abincin shi nakeyi shiko uncle bai damu ba cin abinsa yake yi.
Na gaisawa mukayi da shi tare da fada mai ya barshi zanyi baiso ba amma ban bashi fuskan tsayawa ba ya fita daga kitchen din.
Bai dade da fita ba sai ga zarah tashigo muryan ta naji daga bayana tana fadin anty ina kwana ?
Dan juyowa nayi ina amsa mata tace dani may zan kama maki anty ?
Nayi mamakin jin tambayan don bata fitowa haka da safe sai idan mun gama tace barci ne ya dauke ta bata san gari ya wayewa ba.
Yau kuma ko tafito ganin wani abin ne ta sake fada ban sani ba sai nace da ita ki barshi kawai ba wani aiki mai yawa zanyi ba ai.
Tayi dan jimmm sai naga ta nufi wurin dankali nace ki barshi yau ba zan soya dankali ba ai nan naci gaba da aiki na share ta.
Ta dan jima atsaye sai ta juya ta fita daga kitchen din na gaba na ba kowa nasa wanka nayi kafin ya fito na shirya cikin wasu atamfan Super mai launin makuba na fito zuwa wurin shi.
A tare muka fito dashi daya gama shiri tana falo wanan lokacin ganin mu yasa ta zamo daga saman kujera duk ta daburce da ganin ta bata da gaskiya ko kadan ta na gaishe shi a daure ya amsa mata.
Bayan kwana biyu gwago ta koma gida tare da abin arziki mai yawa da ta samu wurin maigida don har injin din tatsar mai ashe ya saya mata duk bamu sani ba sai da ta koma nakejin labari.
Naso bayan tafiyan gwago in daure ma zarah amma sai nayi shawara na fasa nuna mata nayi ban san komai ba gaba na da yawa ai.
Sai dai na bar yin komai a gaban ta yanzu na kuma rage bata fuskan da nakeyi sosai so nake ita da kanta tabar gidan batare da wani abu ya fito daga gare mu ba.
Wata na biyu cur a gidan uncle na canza acikin dan kankanin lokaci saboda abin more rayuwan da nake samu a gidan shi.
Don babu abinda ya rage ni dashi na fannin rayuwa duk wanda ya ganni sai yayi maganan canzawa na ni kaina nasan ina daga cikin matan da suka dace da gidan miji.
Banda tunanen komai a raina in ma ina da bai wuce na ciwon dake jikin mu ba kuma Alhamdullahi muna samun kula yadda ya dace sosai dama abinda ciwon ke bukata kenan.
Haka zai sawo abubuwan kara jini ya sakani a gaba sai munci tare magani kuma idan yana gari a tare muke sha kullum kafin mu kwanta don ka,idar shan shi ke nan.
Yaya Saadu yazo sau biyu a lokacin don ba a gama gyaran gidan da zai zauna ba sai yake zuwa yana komawa.
Ranan ina daki kwance dakina da yamma daidai lokacin dawowan uncle gida ta kusa sai ga zarah ta shigo da sallaman ta dakin tayi sallama na amsa mata ta shigo ba kasafai take shigo min daki ba sai idan da wani dalili.
Anty kin yi baki tace min na dago daga kwancen da nake ina fadin baki tace eh suna falo zaune suna jiran ki.
Dama bani zama babu kwaliya a gida tsab nake banda wani kushe a jikina kara dan gyarawa nayi dakyau na fito don ganin ko su waye suka zo.
Mata na hango zaune su hudu a falo sai dai ban sheda ko su waye ba daga nesa sai da na karso wurin ina fadin sannu ku da zuwa gaba daya suka juyo sai da gabana ya fadi.
Fon ganin bakin nawa don ba kowa bane anty Uwa ce da yaranta uku gaba daya a gidan namu, , ,


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/17/20, 10:17 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , , ,


🧕🏿5️⃣8️⃣🧕🏿


NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN KIN FITAR UBANGIJI YABI MIN HAKKINA A KAN KI/KA DON WALLAHI BAN YAFE BA, , , ,


Ganin bakin nawa take naji gaba na yayi wani irin bugawa don tsoro da fargaban ganin su haka a gida na may ya kawa su kuma nake tambayan kai na.
Muryan anty uwa ne ya dawo dani daga duniyan tunanen da na lula da farko naji tana fadin a, a tau, amaryan ce wanan masu gari tana bin zanin jikina da kallon tun daga sama har kasa na binshi da kallo sukeyi.
Allah ya rufa min asiri yau da safe bai fita gidan da wuri ba don haka na sha kwalliya tun da safe da atamfan brocade a jikina.
Dinkin shi mai kyau tun daga Dubai ya sayo min shi hakana din kakken shi murmushi na kakaro a fuska na ina cewa dasu sannuku da zuwa tare da sakin fuska sai da na zauna nake cewa ina wuni Anty Uwa kamar yadda naji anty na na lagos na kiranta dashi.
Waya na dauka ina latsawa mai aikin mu na kira ina fadin make something special for our visitor's.
Na gama na dago tareda cewa sannun ku da zuwa duk naga sun kura min ido sai bin gidan suke yi da kallo sauran yaran nata itako sai faman tabe baki take yi.
Mun gaisa sai dan shiru ya biyo fallon anty uwa din ne ta kawar da shirun da falon yayi a lokacin.
Ji nayi tace dani maigidan ya fitane ko yana ciki nace ya fita yana gun aiki sai zuwa yamma zai dawo gidan.
Dakatar, ni , wata daga cikin diyan nata, tayi da fadin ai dama bashi muka zo gani ba gun ki dai ke snacher muka zo,
Murmushi nayi don jin sunan da suka kirani da shi wanda su ya dace a kira da sunan tun farko amma sai gashi suna lakakamin sunan don basu da kunya.
Uwar ne ta dakatar da ita da fadin dakata lawisa sai ta juyo gare ni tana fadin ke wama kike da suna what ever dai ba mun zo bane nan don dogon surutu sai don mu zo mu ga idon yar kauye kamar ki da har ta iya kwacen maza haka son ranta.
Tun wuri ki san da sanin Nafisa zata shigo gidan don haka ki zauna da shirin taron ta ke wanan gidan ma ai sam bai dace da irin ki ba yar kauye ga gida har gida amma wai yar kauye gaja ce irin ki a gidan ba ilimi ba komai.
John ya shigo da tire shake da drinks da sauran abin taba baki ya girke a gaban su don basu da kunya sai suka zari guda guda suna balla bakin su tare da kafa kai.
Duk da uwar taji kunyan abinda sukayi sai dai banda ita Nafisa din fada ta fara yi musu akan su natsu mana suyi abinda ya kawo su.
Ina zaune na kafa masu ina kallon abinda ke wakana nasa yatsan hannu na guda na tallaba haba na dashi tare da kura masu ido.
Bayan sun dan natsu ne uwar taci gaba da fadin yanzu ke har kin san ki yaudari matar da ta tsamo ki a cikin talauci da wahala ki tsallakata bayan ta gama maki komai kin gudu kin barta don halin dan adam butulu saboda kina hangen nesa.
Yanzu ke baki ji kunyan asirce ta da kikayi tun farko ba bai maki ba kuma kika asirce mata kanin miji da bakar asirin ki don kawai kin samu labarin yar waje na yake nema yanzu.
To ai baki sani ba idan asiri kike takama dashi nafiki idan kuma barikanci da iya duniyan ci kika ce kin iya duk na dama ki na shanye.
Gidan nan sai Nafisa ta shigo shi ko yau ko gobe ki zauna a cikin shiri don da ta shigo waje kika yi ke.
Don gidan nan ba gidan zaman ki ba bai dace da mace yar kauye kazama irin ki ba don haka ki sani, , , , , , ,
Madam yaya gida ya fada ba tare da ya kallo mu ba driver shi na binsa baya da jakkan shi na ai har ya nufi hanyan dakin shi sai kuma ya juyo yana cewa sorry baki kikayi ne ?
Murmushi nayi tare da fadin anty Uwa ne fa da yaranta da, , , ji nayi ya katse ni karasa magana na da tambayan da ya daure min kai.
Uwa waye uwa ya fada yana maimaita sunan cikin daure fuska dan gyara zama tayi tana fadin Sulaiman baka gane ni bane ?
Uwa sister din yaya Lawal soja dake Lagos minjin maimuna wai kana nufin ka manta dani uwa na gidan malam garba teacher.
Katse ta yayi da fadin kenan ke sister din lawal ne ko kece ke zaune a nan garin da sauri tace eh nice ai , yace anzo diba madam ne ?
Wani kunyan ne ya kamata ba ita ba har diyan nata sai da sukaji nauyi don yanzu suka gama cika baki akan shi gashi kuma ya shigo ya nuna baida halaka da su asalima bai san su ba.
Yana batun wucewa na bude baki da sauri ina fadin Uncle bakin ka ne fa , don wurin ka suka zo da mamaki yake kallon fuska na kuma ya dan kallon su sai ya dawo ya zauna.
Na mike zan nasu wuri ya ce No zauna idan sunzo wurina ai kamar wurin ki suka zo so ki zauna ba wani abu bane ya juya wurinta yana cewa lafiya ko hajiya ?
Duk sun natsu ta kasa magana sai mai bi ma Nafisan ce ta fara mikewa tana fadin sai da na fada maku kada muzo gashi munzo an wullakanta mu a banza.
Karamar tace wai kana nufin ba ka masan Anty Nafisa ba ko may ta juta wirin uwar tace mummy duk wanan abin da akeyi dama bai san ku ba ne ?
Mikewa yayi yana fadin tunda baku ma san abinda ya kawo ku ba zaku iya fice min daga gida don Allah bana son a shigo ana damuwar mu.
Waima yaba su daman shigo min gidane ya fadi tare da mikewa yana fita hanyan waje suma da sauri suka mike zasu tafi nace to Anty uwa na gode da ziyaran da kuka kawo min sai gani na biyu kuma.
Ban san ko ina gidan ko kun fitar dani don yarki yar birni zata shigo niko yar kauye ne bankai matsayi zama da su ba.
Sai dai zaku ya tafiya da drinks din nace ma yaran tare da nuna masu tire din da suke ciki nace don naku ne ku aka kawo ma kushi daga haka na juya na fara tafiya komawa ciki nan na barsu tsaye da takaici.
Suna jin yadda yake ma maigadi fada duk wanda yazo kada ya sake barin shi ya shigo mai gida kai tsaye batare da an bashi umurnin ya bude mai ya shiga ba.
Ko ba komai naji dadin yadda uncle yayi masu a raina don da bai dawo ba Allah kadai ya san irin cin fuskan da zasu yi min su tafi sunci bulus.
Da ya shigo nan falo ya zauna yana huce har yana fadin zai kori maigadi da sun shigo sunyi wani abu fa may zaice shi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login