Showing 171001 words to 174000 words out of 269010 words
da iyalin shi kuma yaya sani zai zo don shima an sama mashi aiki anan.
Nayi murna kwarai ko banza nima na samu dan uwa a kusa dani yanzu abokin shawara ga matar shi Samira akwai shiri sosai a tsakanin mu da ita.
A ranan na biyar suka kama hanya nan suka barni cike da kewan su don dan zaman da mukayi ba karamin jin dadin hakan nayi ba.
Gidan ya rage daga ni sai gwago wace da kyat a rana ta fito falo sau biyu ko yaushe ta daki daga sallah sai lazimi tana kallo.
Sai in dare yayi ya dawo gida zai dan je gunta su dan taba hira wani lokaci har da ni sai Zarah da har yanzu bata gama sake jiki dani ba sai dai akwaita da son kallo ko yau a cikin kallo take ita.
Na tambaye ta karatu fa take ce min ta gama secondry bana jiran jerabawa take yi yanzu ina kula dashi da duk yazo ya samay mu da ita zaune sai in ga ya daure fuskan shi har yarinyar ta dan shiga tsarguwa da taga lokacin dawowan shi gida yayi zata shige daki bata kara fitowa kuma.
Ranan ina tambayan shi may sa yake mata haka sai cewa yayi dani cikin tsawa gada ki kara yi min maganan wanan yarinyar don ba zamana takeyi ba a gidan nan .
Da sauri nace Uncle in ba zaman ka takeyi ba zamanwa take a gidan ina kai hajiya taba ita muzo da ita don debe kewa bai yi magana ba sai mikewan da yayi ya fice dakin ya koma dakin karatun shi ya zauna.
Nikan abin ya daure min kai sai na ja baki na nayi shiru har naje gun gwago na zauna muna hira hankali na yana gurin shi don haka nace ma gwago ina zuwa.
Kitchen na shiga na hado mai snack da drinks na nufi dakin da yake da sallama na tura kofa ban tsanmani ya amsa min ba sai dai dan juyowa da yayi ya mayar da kanshi ga abinda yake yi cikin laptop din shi.
Sannu da aiki uncle sai da ya sauke ajiyan ziciya ya iya amsa min da yauwa sannu madam nace ga abin motsa baki nan na kawo maka kadan jika makoshin ka.
Na aje na juya zan fice daga dakin sai naji ya riko min hannu yana cewa ba tare da ya bar abinda yake yi ba bazaki karasa ladan ki ba kin kawo min abin sha baki zuba min ba zaki wuce.
Dawowa nayi na tsaya ba tare danayi magana na fara zuba mashi acin cup din dake saman tire din, mika mashi nayi tare da dan rusunawa.
Sai lokacin naga ya dauke kan shi saman sytem din yana fadin thanks nace aiki nane hakan ya zuke yana lumshe idanuwan shi.
Ya mayar da cup din cikin tire din yana maida kan shi saman laptop din jiki a sanyaye na fita daga dakin yana aiki yana cin dabun naman daya ji curry da kayan kamshi ya lumshe idanuwan shi.
Ban koma ta kan shiba na tsaya kitchen da falo na gyara ina gap da karasawa naga fitowan shi daga dakin har yanzu fuskan shi babu walwala a cikin sa.
Da gefen ido ya kallo ni ya shige part din shi tare da rufo kofan da karfi araina nace ga maganan Aisha ya fito take maganan mummy ya fado min a rai.
Idan yayi fushi ke ki kwantar da fushin ki ki bishi sai zama yayi dadi amma kin hau namiji ya hau wazai kwantar ma wani da fishin shi wata kila ma fushin da dalili yake yin sa.
Dakin gwago na leka na gaishe ta nake gaya mata lokacin sallah ya gabato tace ai har na dauro alwala wanan gida naku ba ajin kiran sallah.
Dariya nayi mata nace baga agogo nan ya sayo maki ba don ya dinga kira maki sallah kina ji tace kaiya ban faye amincewa da wanan abin nasaran ba ai.
Nace yanzu dai da kinji ya kira sallah sai ki mike lokaci ne yayi baya karya sai idan batir din da yake aiki dashi ne ya kare tace bakaji ba.
Ina dariya nace gwago kafin ya kare fa sai nan da kusan wata biyu tace wata biyu ni ina, ina yar nan ai kisa a dauke mu mutanen banza nifa har na fara yiwa maigidan ki tunin gida don naga so kuke sai kinyi ciki ina gidan nan kulle kamar kurkuku.
Fita nayi na barta ina dariya kada in makara da dauro alwala a lokacin naga gittawan shi zai fita zuwa sallah don ko yaushe sallah jam,i bai wuce shi.
Bayan isha,i na gama komai har abincin shi yana saman table na koma daki na shirya tsaba a cikin wani dogon riga baki mai hanuwa shara shara yaji kwalliya har kasa da kananan duwatsu an dan buda kasan shi kadan.
Ban fito ba sai da na ji motsin shi a falo ya na sauraren News hakan ya sani fitowa daga daki ture kusan kala uku na shafe jikina dasu yan saudiya.
Kamshi ya hade da sanyin da AC falon yake saukarwa ya bada wani inrin yanayi a falon tun fitowa ya dago ya kalleni ya kauda kai yaci gaba da kallon TV dake gaban shi.
Har na karaso gaban shi cikin daurewa na karaso gaban shi na dan duka daga bayan shi tare da sagala hannu na daga bayan shi nace sannu da hutawa Uncle.
Dan murmushi ya sake da bai sauka ciki ba yace barka da gida madam din Uncle zagayo dani yayi zuwa gaban shi ya zaunar dani saman kujerar daga gefen shi yana mai ci gaba dakallon shi sai dai har wanan lokacin bai sake min yatsun hannu na da yake wasa dasu ba.
Cikin daurewa nace Uncle abinci fa yace dauko min nan zan ci na mike cikin wani tako da ban san na iya irin sa ba na nufi dining din kwaso kayan da na jera akai.
Sai lokacin ya sauke wani iri ajiyan zuciya har ina jin shi don na kusa kawowa wurin shi a raina nace su zuciya manya.
Ashe akwai aiki a gabana dan wanan magana yake ta jawa rai haka anya kuwa zan iya sai da na gama jerawa nace bissimillah na samu wuri a kasa na zauna tare da jan plate zan fara zuba mai.
Ganin kayan tare a gaban shi kashi kashi yasa yace min may ye haka yau John ya girka muna?
Banyi magana ba sai ci gaba da bude warmer din nayi inda na fara ziba mai tuwon shikafa da miyar shawaka da yaji agusi da manja sai nama manyan yanka da nayi amfani dashi wurin hadawa da dan man gyada kadan.
Kamshi me ya kaure falon alokacin da na bude ferfesun kifin dana hada wanda nayi amfani da kayan yajin mu na gargajiya sai ruwa dana zuba da maggi.
Gani nayi ya sauko kasa abin wanke hannu na jawo tare da dauko ruwanda na tanada don wanke hannun nashi.
A hankali ya miko hannuwa fuskanshi akan tv ina zuba mai ruwan ya na wankewa a hankali na jaye ruwan gefe guda sai ya kallo ni yace ke ba zaki ci ba nace munci da gwago da Zarah tun dazun dana gama.
Naga ya kara hade rai yayi bissimilla ya fara ci har ya kare bai yi magana ba ni dai ina zaune na saka ma tv ido nima kamar mai saurare abinda ake fadi nan ko zuciya ta tambaya kanta take yi mai ya kawo wanan matsalar haka wai ?
Naji yace amma ba John yayi abincin nan ba eh kawai na bashi amsa dashi na fara hada kayan ina kwashewa na barshi dana ferfesun yana sha a hankali yana kallon tv.
Bayan ya gama na kwashe na dauko kamshi na bude falon dashi yadda ba za a ji karnin kifin ba idan an shigo falon.
Zama yayi a kasan tare da jingina bayan shi da kujerar daya sauka a kai tare da mike kafafuwan shi a kasa yana kadasu a hankali zaman naji shiru yayi yawa don haka na mike zan leka gwago a dakin ta.
Yace jimana sai na dawo na zauna cikin basarwa yace gwago tayi min maganan zuwa gida yau da safe don haka nake son ku fita ai mata tsaraba zuwa gobe.
Allah ya kaimu nace sai na juya na wuce bina yayi da kallo komay ya tuna a ranshi sai yaga bai kyauta min ba sauke ajiyan zuciya yayi may ye laifina a cikin wanan magana daga tambaya kawai ya dora min laifin dabashi ba.
Nasan nayi laifi na kuma dauka ina binshi don yayi hakkuri ya kasa cire laifin da bani nayi shi ba akaina.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/15/20, 10:51 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , , ,
🧕🏿5️⃣7️⃣🧕🏿
NOVEL DINA NA KUDI NE IDAN KIN FITAR UBANGIJI YABI MIN HAKKINA A KAN KI/KA.
YAR UWA MAINE RIBAN KARANTA KAYAN ALLAH YA ISA KARATU FA IYAKAR SHI DUNIYA.
Karfe goma saura har lokacin ina zaune dakina na kasa zuwa dakin uncle don ban san da wani fuska zai karbe ni har nayi kamar in share shi saidai na mike na fara shirin zuwa wurin shi.
Komai na falon an an kashe alaman dai ya shige tuni dakin shi sai wutan da zai sadani da nashi part din ne kawai a kunne.
Ahankali na kwankwasa kofar tare da turawa sai najita a bude nasa kai na shiga dakin can na hango shi tsaye bakin window dake kallon wajen gidan yana tsaye ya rike labule da alama iskan dake busawa a lokacin yake shaka don yana mai dadi.
Shigowana baisa ya juyo gareni ba har na karasa inda yake tsaye batare da jin kunya ba na rungumay shi ta baya tare da zagaye hannaye na saman ruwan cikin shi.
Ajiyan zuciya naji ya sauke a sanyayye nace uncle may kake yi anan tsaye kai kadai batare da ya juyo ya kallene ba ya bani amsa da yanayin yana min dadi ne madam.
Sake shi nayi nima nakoma gefen shi na tsaya ina kallon waje sai naga motoci suna wulgaiya jefi jefi ga iska mai dadi na hurowa ta tagan dakin.
Gwaron numfashi na sauke amma a fili na kasa fadin komai sai tsayawa danayi ina kallon wajen kamar yadda shima yake kallo.
Shi ya kawar da shirun da cewa na dauka kinyi barci ne dana jiki shiru ai ajiyan zuciya na sauke nace uncle ina zan iya barci bayan miji yana fushi dani karo na farko a rayuwan mu tare.
Murmushi yayi tare da sanya hannuwanshi saman kirjin shi yace bada ke nake fushi ba sai dai maganan ki ce ta jawo min fushi na.
A marairai ce nace kayi hakkuri uncle ban san maganan zai bata maka rai ba haka da banyi ba ni gani nayi yarinyar tana zaman kane a gidan kuma bata samu sakin fuska a wurin ka ba.
Naji na gode amma ke bakuwa kike a cikin mu shiyasa zan daga maki kafa ga maganan yanzu amma indai akan zancen wanan zurian ne bani son daga yau ki kara yi min shi a gidan nan.
Ki barni da yan uwana ki zauna matsayin ki na matana a cikin su bani son ki zure masu har su samu kafar shige min haka.
Murmushi nayi na kwantar da kaina saman kafadan shi nace uncle yadda kake so haka za a yi har kullun a shirye nake da in maka biyayya a rayuwana.
Amma Uncle ina son ka zama mai yafiya ga duk wanda ya zulunce ka saboda kayi koyi da sunnan mai,akin Allah sallalahu Alaihim wassalam.
Yau uncle in har akwai abinda sukai ma rayuwan ka sai ince ya zama maka taki ayanzu don hassada ga mai rabo taki ne.
Uncle har kullun sai dai inci gaba da yima addua da fatan alheri a garemu uncle ba zan boye maka ba bantaba ganin mutum adali irin ka ba uncle.
Sai dai kuma cikar kamalan mutum baya kammals sai ya cika sharudun Allah a kan shi yanke zumuta dasu don sun taba yi ma rayuwanka illar killa can baya ba shine mafita ba a gare ka.
Kamata yayi uncle kai ka saka masu da alherin ka barsu da halin su Allah shine mai hisabi arayuwan biyan sa.
Amma uncle akan may zaka rike gawarshin wuta a hannuwan ka su kona ma aikin na alheri har ka gamu da fushin ubangiji ka ta sanadin su.
Uncle kafan Allah yana fushi da may yanke zumunci sannan na fahinci baaba tayi hakane don kawar da wani abu a gare ka.
Sannan Uncle ba, , , , ji nayi ya dora dan yatsanshi saman bakina yace ya isa haka naji na gode zanyi iya kokarina inga na fitar da abin a zuciyata.
Ina alfahiri da kasancewar ki matana a yanzu don samu mace ta gari yana haifar da alheri acikin zuri,a dawamamiya.
Ya rugumay ni zuwa bakin gadon shi sai lokacin da ya sauke ajiyan zuciya yace may kika tanadarwa tafiyan gwago ne ?
Ban bata lokaci ba nace gwago mai za a tanadar mata dayafi jarin kuli da takeyi ba dare ba rana duk shi ya hanata zama hankalin ta na can wurin masu zuwa sarin mangyadan ta.
Kai naji yace yanzu kina nufin gwago har yanzu tana irin aikin wahalan nan na kuli nace da hannunta ko take komai wallahi.
Nisawa naji yayi yana kaiwa kwance nace Uncle kuna waya da anty kuwa ?
Yayi dan guntun murmushi tare da fadin ina jiran sai ta huce da kanta zata nemomu don yanzun ta hau sosai .
Nisawa nayi nace a kullun idan na tuna irin alherin dake tsakanina da ita ban jin dadi a raina da haka ta kasance a tsakanin mu.
Baiyi magana ba sai kamomi dayayi zuwa jikin shi muka kwanta anan labarin ya canza sallon shi.
Washe gari bayan ya gama karyawa ne alokacin gwago na da mako biyar a wurin mu kamar yadda yace kudi ya dora min saman cinya na yana fadin ku shiga kasuwa da gwago asaya mata duk abinda take so don Allah kada kibi son ranta a sai mata duk abinda ya dace da ita.
Dago fuska nayi ina kallon shi ganin yadda ya daure fuska yasa na kasa fadin abinda nayi niyar fada mai din.
Sai dai da ganin fuskana kasan so nake ince mai hidamar da yakeyi a kaina sunyi yawa haka gani nayi ya gyada min kai tare da fadin karki ce min komai indai ba so kike ki bata min rai ba.
Ajiyan zuciya na sauke tare da fadin Uncle ni may zance sai dai inci gaba da maka fatan alheri Allah ya saka da alherin sa.
Sai dai ba zan iya boye maka ba ban taba ganin mutum irin ka ba a rayuwa na har tsoro nake ji kada yan uwanka su fara zargina akan haka.
Murmushi nan nashi ya sakar min inda ya fara tafiya yana fadin yau ba zan samu rakiyan bane ?
Na mike da sauri ina fadin ban isa ba ai a tare muka fito ina rike da yar briefcase din shi har zuwa bakin motar shi inda iya nan nake tsaya dama.
Sai da yayi kissing din goshina ya fara tuki yana cewa ku fita da wuri don idan yamma yayi tafiyan ba dadin fita garin.
Na dawo ciki cike da murna a nan falo na samu Zarah ta fito ban tsaya ta kanta ba na nufi dakin gwago tabi bayana da kallo.
Zaune na samu gwago ta kura ma tv ido ga tasbaha a hannun ta tana ja tayi kyau ta kara kiba da haske sosai nace kai gwago wanan irin kyau haka karfa ki koma inji zawarori sun fara zuwa wurin ki.
Dakuwa ta nuno min tana fadin wani shegen bazawari zai zo wurina yanzu ai sunyi nacin su sun barni nan so sukeyi su dan cinye abinda muka dan gada su barmu muna leke a gidan wasu.
Don gaskiya gwago batayi tsufan da za a ce bata da aure don kunsan yadda aure yake a kauye irin auren nan na wuri atara zuria da wuri.
Sai da na zauna kusa da ita sannan na fito mata da kudin na aje a gabanta tabini da kallo sai kuma ta juya ta kalli kudin dake gaban ta tare da zaro ido.
Dariya nayi nace gwago kidin ki ne yace zamu shiga dake gari a sayo maki duk abinda kike so kuma ya ce don Allah a saya maki abinda naga zaki bukata indan kin koma gida.
Zaro ido ta karayi tare da fadin yar nan duk wanan uban kudin duka nawa ne haka gaskiya sunyiwa ki raba uku ki maida mashi da kashi biyu kice na gode.
Sauran na samu na kara jari ai sun isheni sayen buhun gyada goma nan gaba kin ga jari ya tasa ke nan nan gaba.
Da sauri nace a a gwago Allah ne ya kawo muna hutu a karkashin shi Allah ya duba wahalan mu na can baya lokacin