Showing 93001 words to 96000 words out of 269010 words

Chapter 32 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13318

nai masu wani mai kyau na hannu don dai indai kitsone Allah ya hore min iyawa ko wani iri.
Faiza ce ta fito ta samu muna kitson karshe dagani daga barci ta tashi tace wai ashe kuna nan na saba ba in fito ba kowa a falon dole nima na koyi zaman daki ta kai zaune tana yaba kitson da mukeyi tare da cewa ashe kin iya kitso ne haka ?
Na dai yi mata murmushi a raina nace ai kitson ne ya jawo min wanan alherin da nake ciki don lokacin da ta fara kawo su har sau biyu tana zuwa amma bana karban kudin su sai ince su din ai yara nane.
Haka yasa uwar ta daina kawo min kudi a lokacin sai dai wani abin da tafiya yai tafiya kuma ta fahinci halin da nake ciki ta shiga taimaka min.
Jefi jefi muke hira da ita na gama tare da daura masu ribon don shuku biyu nai mako waccen su sai take cewa nima gobe zan sance kaina ki mun ghana wiving don shi nake so nace da ita Allah ya kaimu kawai.
Fati ne ta fito daga dakin ta ko kallo inda muke bamu ishe ta ba zata wuce mu nace mata anty Fati ina kwana cikinciki ta amsa min gaisuwan ita ko Faiza ta ja wani tsaki tare da kawar da kanta.
Dining ta wuce ta bubude kulolin dake wurin ta wani tabe baki tace duk ma an jagule abincin ambar jagwalgwale.
Ba wanda ya kulata sai kuma naga ta zauna tana diba nan ta zauna taci ba tare da kula mu ba sai dai tana yi tana satan kallon mu a fakaice.
Ni dai ina mamakin ta a raina dayar yan biyun ta nufeta take cewa ta dubi kitson da Anty tai masu korar yarinyan tayi daga wurin ta ta wuto tana yi tana waigen ta kamar zatai kuka ganin haka yasa nace zo nan kada ki kuka kyale anty.
Ke naji ta fada kamar wacce ta samu diyarta don haka ban dauka da ni takeyi ba sai da ta sake fadin ke Safiya bakiji bane san nan na dago kai ina kallon ta.
Tace ban faye son ana shiga harkata ba don haka ki kiyayye yar kice ko yar yar uwata koda yake ma kalan dagi ce ke don naji anty na fadin wai kema kauna tace ko a ina ta samay ki oho ?
Ko da yake kila ta wurin mamanta kika fito ban sani ba nan na fahinci ba uwarsu daya ba ashe kila uba suka hada.
Ni dai ban ce da ita komai ba sai Faiza ce tace mata amma dai kin san ba girmuwanta kikayi ba da zaki fada mata haka.
Koda yake baki da laifi don ita ta fara kiran ki wai da anty shiyasa kan ki ya fasu haka kike jin kanki wata babba can.
Ya ishe ki gida dai ne baki iya korana don nima gidan yar uwata ce dariya naji tayi tace yar uwa ko muna yar uwa ai da yar uwan kwarai ce da kin so abinda take so ke yanzu baki ji kuyar korar wanan yarinyar a gurin ki.
Nan dai sukai ta cacan baki wanda nake gani ba yau suka fara irin haka a tsakanin su ba da naji abin yai yawa nace da ita ta kyale ta don Allah maganan ya kare ai mutum guda bai fada.
Sai kuma ta juya kaina tace wai ai dama taga zubina na munafukai ne don haka sai dai hassada ya kashe mu don ita ta wuce ajin muko.
A raina nace wata sabuwa kenan kuma nayi gudun gara na fada ma zago in na gudo gidan mu don inna ga wata kuma na samu a nan yan kuwa zamana nan mai dorewa ne kuwa.
Maigidan bata dawo ba sai hudu na marance daya bayan daya muke shiga muna gaida ita da dawowa koshi ban san ta dawo ba sai da Faiza ta fada min sannan na tafi.
Dama yaran na wuri na sun rigani isa don sai da na tsaya nai sallah na fita zuwa gaida ita din da dawowa.
Zaune take kasa yayin da diyan nata suke saman jikin ta ta mimike kafa suna zuba mata surutu saman jikin ta na gaida ita ta dago har kullun fuskan ta a cikin murmushi tace dani safiya yaya muka wuni nace lafiya kalau anty kin dawo lafiya ta amsa a sake da lafiya.
Sai na juya tace kin ga Safiya debo min abinci na nan don ban iya saukowa kasan nan yanzu na gaji yau da yawa.
Na juya zuwa dauko mata abincin ashe baya wucewa na sai yar tace mummy kin san may yau da baki nan mummy fati tana ta fada su Anty tana ta zagin su .
Sai dayar tace sai da wanan anty tai kuka ita gwagon mu batai kuka ba tana bata amsa sukayi ta fada sosai.
Na shigo dauke da ture tace dani ashe kunsha kitso ne haka sannu da kokari murmushi kawai nayi na aje mata tana cewa yauwa sannu yar gidan anty na gode.
Na juya na fita dakin har nakai kofa tace don Allah yimin magana da Faiza idan kin fita nace to anty.
Ina fita na nufi dakin faizan tana zaune tana waya na isar mata da sakon anty na fito daga dakin.
Sai da ta gama ta fita daki na koma na kira ummi na don jin lafiyan su da sauran mutanen gida .
Nan take fada min bayan wuce wana ai anyi fada da baba da inna har don bata san inda naje ba sai daga baya da taji take zage zage wai naje yawon dandi zanbarbada wa maza cuta.
Shikuma baba ya kasa kyale ta nan dai abin ya kaisu har da duka abin da bai taba yi wa wata mace ba a gidan nan.
Nace ni kuwa ummi may na tsare ma inna ne a gidan tafi dason in zauna in wulkanta tana min gori ko yaushe a gida ?
Yanzu dai ai ya dauki mataki a kanta don da wuya ta sake maganan ki kuma ai a gidan nan yadda suka kwasa dashi abin ba dadi wallahi.
Nan dai muka sha hiran mu kan matsalan gidan namu da ita karshe nai mata sallama na tashi don gyaran daki sam bani barin dakin da kazanta ko kadan.

********* ********* *********
Faiza na shiga dakin anty tace ta samu wuri ta zauna sai da ta kai zaune tace da ita yanzu yaran nan ke fada min abinda ya faru da bana nan.
Shi nake son ki fada min komai nan ta fara fadi yaran na tuna mata wani abin har ta kai karshen zancen ta.
Tace wanan yarinyar sai na fito mata ta bayan gida zamu zauna lafiya bata kara furta wani abin ba sai faiza da ta mike ta fice daga dakin tana masu yan biyu wasa.
Hankalina yanzu akwace yake babu abinda ke damuna araina Fati ce kawai matsalata ban kuma kulata bayan gaisuwa da yama kamar na dole a tsakanin mu babu abinda ke hada mu da ita.
Nayi wani haske na kara kyau sakamakon mayuyukan da Anty ta sayo min in dinga amfani dasu a maimakon vesiline da nake shafawa da.
Wanda ko vaseline din ban damu da shafawa da don oilyskine din da nake dashi sai dai ina da dry face amma haka nake barinsa ba gyara.
Nan ko anty ta maysa min son ita yar son kwaliyane taki jinin taga mace bata gyara fuska ba ko jikin ta tun ban iya ba dole na kowa duk kowa da ba inda nake zuwa daga gida sai gida.
Duk wanan halin da nake ciki nakan tuna da halin da rayuwa na yake ciki zamana kenan ba karatu ba aure tare da ni.
Duk da anty na iya bakin kokarin ta wajen ko dayaushe takan muna nasiha da gargadin mai kyau da nagarta .
Babu irin wanda batai muna badon komai ba ba sai don jin tsoron Allah takance ku kama kan ku daga duk wani nauin shiga tarkon shedan
Takance duk kanku amma kuke a wurina don haka ba zan yi sakaci da tarbiyan ku ba don baku gaban iyayyen ku.
Ta kuwa sa a don duk kan mu babu wanda baya daukan nasihan ta dan dama Fati wani lokaci sukan kwasa wajen saka tufafi sai taso tace zata saka irin na kabilu nan sukan kwasa da yar nata.
Bayan ita bata da wani matsala da kowan mu gashi yanzu zuwa na zatafi hankalin ta kwace don tasan yaran ta zasu samu kulawan da ya dace ko bata gida.
Don ni dama haka nake dayara kona waye sai kaga atake yaro ya lake min a jiki bai damu da uwarsa ba koda na zauna gida akwai yar makwaciyar mu data lake mun duk safe da an mata wanka zata zo gidan mu sai da yamma indan dare yayi zan maida ita gida.
Amma naiyyanar ciwon dake jikina sai uwar ta hana yarinyar zuwa wanda nasan aikin Inna ne don dama tana jin haushin hurdana da matar.
Dadine gashinan sai abinda mutum bai so a gidan anty mijin ta kuma baya kasan tun zuwa na wai yaje US wani aikin suna sojoji amma kwanan nan naji antyn tana maganan dawowan shi kasan.
Don haka muke yi yadda muka ga dama a gidan babu mai takura muna amma naji Faiza na fadin yanzu yaya zai dawo gidan zai koma ba dadi don in yana nan babu wali a gare mu.
Ni dai dama ba sanin shi nayi ba don haka ban damu ba don koda yana nan ba ruwa na sai in fake ma daki inda har yana gida baiko ganin giccina a gidan nace a raina.
Muna zaune falo da anty take cewa wani sati maigidan zai dawo kuma tana ganin shida sulaiman zasu dawo.
Faiza tai saurin cewa harda shi zai dawo anty tace ba dole ba yana zuwa ya zauna a kasar mutane gashi arzikin shi sai kara habbaka yake yi yanzu ai gara dai ya dawo gida asan abin yi kan case din shi.
Kamar yadda anty ta fada hakane satin da muka shiga bamu da hutu a gidan don shirye shiryen taron maigidan da kanin sa da zasu dawo kasan.
Kusan aikin nice a gaba don banda kasala akan aiki duk yadda yake kuwa kafin wani lokaci mun hada komai yadda ya kamata muyi.
Sai a wanan lokacin naga Fati na rawan kafa don har takan dan saka hannun ta ga aikin da mukeyi ayi tare da ita.
Tai ta faman murna tace ance harda Uncle sulaiman zai dawo ashe gidan namu zai cika ke nan kwanan nan.
Da yake ba hira muka saba yi da ita ba babu wanda ke kulata har tayi ta gama sukiburutsun ta ta bar wurin.
Don ba sabawa tayi da irin haka ba don haka bata da jimirin dade wa tare damu a falon ranan da zasu dawo kuwa tun safe muke murzan aiki sai yamma muka gama kowa yaje yai wanka kafin shigowan shi.
Tun da nai wanka na jawo dogon rigata na saka a jikina na koma nabi gado na haye don dama a gajiye nake don mun sha aiki sosai.
Ban fito ba ina jin ana ta hayaniya a gidan nasan matafiyan namu sun iso kenan zuwa dare anty ta leko daki na tana cewa najiki shiru ga bakin mu sun iso gida lafiya har sunci abinci baki fito ba ke .
Nai murmushi nace sun iso lafiya anty tace kalau suka iso nace da safe indan sun huta mu gaisa dasu ai wani kallo tai min.
Tace amma Safiya baki ko kyau ta min ba in kin ce sai gobe mutum ya kwaso gajiya na mike zubur nace tuba nake anty ta dan harare ni tace ke kika sani ai.
Tace ai har uncle din yara ya tafi abishi don shi dama bai son yawan magana na fita da zumbulelen hijabina yana shirin tashi sai gani shi kadai na gani a wurin sai anty da yaran ta har kasa na kai ina cewa daddy barka da dawowa.
Ya juyo da sauri tare da amsawa yana kallo na yace Safiyar taki ke nan ashe ma karamar yarinya ce haka yace mun samay ku lafiya nace lafiya kalau.
To yaya hakkurin abinda ya faru aita hakkuri haka duniya yake dama ba komai ne ke zuwa wa mutun daidai ba a sanyayye nace nagode a huta gajiya don har idona ya kawo kwalla ko.
Na juya zan tafi naji anty tace dani Safiya a rage kayan nan daga wurin nan na juyo na fara kwasan kayan ida ba wani cin abincin sukayi ba sosai dan tabawa sukayi suka barshi duk uban wahalan da mukaci na aikin yin shi.
Na saka na fridge a cikin sauran kuma na adana su inda ya dace a jiye su san nan na koma dakina na rufo Asuba ta gari indan tunane ya barni nai barci yadda ya kamata


Yar uwa ina zaki da hakki a kan ki na mutane ance ba a yafe ba baki barin turawa kina daukan nauyi a kan ki,
Karatun nan fa ba dole bane kiba kanki lafiya mana da daukan nauyi don neman suna kike turawa ko don kina ganin haka ba komai bane.
To nace Allah yai min gagawan isa ga mai fitar min da novel waje .


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,


🧕🏿3️⃣2️⃣🧕🏿

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,


Washegari muka hade a falo duk kan mu sai anty dake wurin mijin ta Fati sai faman murna take yi uncle Sulaiman ya dawo,
Hararan gefen ido Faiza tabita dashi tace wai kina ta murnan dawowan Sulaiman wanan dan bakin rai jiya kin ga ya dubemu ne ma.
Kai wallahi turai ya karbeshi kin ko ga yadda ya kara girma yai wani fresh dashi kamar bashi ba don Allah.
Faiza ta watsa mata dan harara tace yanzu ai kanki ake ji shi baki ko isheshi kallo ba, ta bata rai tana fadin oho dai ko bai san ina yi ba wata rana zai sani ai.
Mako uku cur da dawon su amma sau biyu naga daddy a gidan haka wanda Fati ke maganan shi ko yaushe ban taba ganin shi ba kuma sunce yakan shigo gidan wani lokaci amma Allah bai taba sawa mun hadu da shi ba.
Yau ya shigo gidan anty tai mai tayin abinci yace bai jin cin komai a lokacin kai ta girgiza tace wai kai har yanzu kana nufin baka fitar da zancan Samira a rayuwan ka bane ?
Yai murmushi yace kai samiran may can ai ni yanzu in ba lokaci ba ban faye kawo ta a raina ba sai dai ai kin san yazama dole ba zan taba mantawa da ita bane.
Anty ta nisa tacd dashi Allah ya sauwaka amma don Allah ka rage yawan tunane ka koma alamarin ka kamar kowa ita fa har naji ance tayi wani aure ko.
Yace nima haka naji gun wani dan uwan su can.
Ta dade tana dan kallon shi sanan ta gyara zama tace na cewa dashi ya kamata ka manta da komai hakana ka samu wata wace kake zuwa wurin ta ku shirya.
Sai yaneme ya katse zancen sai ta hana shi samun damar yin hakan tace kyale ni har in gama tukun yanzu sulaiman da hankalinka da ilimin ka da komai kaifa ka iya sa wani agaba kai mai fada idan kaga zai kauce irin haka.
To yaya za a ce kai da kan ka ke irin haka kuma.
Kar fa ka manta Allah yana sane da komai na bawan sa shekara biyar kenan ka kasa cire hafsat a ranka sau kace ba musulmi ba ?
Haba sulaiman shi fa musulmi da tawali,u aka san shi saboda hadisi ne ingantacce daya tabatar muna da hakan imanin dayan ku baya kammala har sai yayi imani da kaddara mai kyau da kuma akasin hakan.
To what come over you ?
Sulaiman
Da zaka manta da duk wanan a ranka ?
Gaba da daya lamannin shi suka sauya a lokaci guda ciwon da dade yana cin zurciulyar shi ya dawo mashi sabo fil, wanan dalilin ne yasa dama yake gudun gida don kowa na shakkun fada mai zancen aure.
Ko ita kanta anty sai daga baya taji dama bata dauko mai zancen ba don kawai ganin yadda ya sauya alokaci guda.
Ta kalle shi a sanyayye tace sulaiman ban dauko wanan maganar ba don in tayar maka da hankali amma kayi hakkuri kayi tunane akai.
Kar kaga na dauko ma maganan da kowa yake gudun fada maka nayi hakane amatsayi na wacce muka shaku dakai don zaman ka a haka yana damun kowa.
Ya mike don bai son maganan yai nisa yace zan fita sai na dawo sai dai ba lalle ne in dawo kusa ba don ina son in leka bauchi kwanan nan.
Ba damuwa haka na da kyau ai aje gida adubasu yafi amma kayi tunane aka magana na don Allah shi yafi.
Ya sauke ajiyan zuciya tare da karfin halin fidda murmushi a fuskan shi yace zan diba madam ni zan tafi tace aiko danafi kowa jin dadi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login