Showing 114001 words to 117000 words out of 269010 words

Chapter 39 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13347

da halina ne tun yanzu idan zan ba mutum abu bana bashi ya sani sai baya na.
Tace kabi mun kauna a sannu ko muce mun fasa kaje gaba ka samu daidai da kai yace tuba nake babban yaya kin san kaunar taki sai a hankali.
Nan take fada mai zancen mahaifina da nazo mata dashi ya kama fadin subbahanallahi yazu yaya ke nan tace wallahi fa daddy nake son ya shigo musan yaya za a yi don tace zata tafi.
Yace OK kuyi magana dashi muji yaya za a tsara mata tafiyan don ba abin da za a tsaya bane wasa saboda ba a san halin da yake ciki ba.
Nan dai su kai sallama ta kashe wayan tare da mayar da kallon ta a kaina tana fadin dama yakanyi ciwo haka ne na girgiza kai tare da fadin gaskiya bai taba yin haka ba sai wanan karon.
Turo kofan da akayi ne muka mayar da hankalin mu ga may shigowa daddy ne yace a a kuna meeting ne haka komay ?
Tace dashi uhumm wallahi mahaifin ta ne aka bugo waya yanzu baida lafiya shi ka gan mu haka.
Subbahanallahi shi ma ya ambata yana cewa tunda suka bugo jikin ya matsa mashi ke nan kwarai tace ai itama maganan da takeyi yanzu ke nan hankalin ta ya koma can.
Yace dolle ne amm yazu dai abari zuwa safe sai inga yadda ya dace ayi ta tafi har ya juya zai fita daga dakin sai ya juyo yace shi sulaiman din yasan da zancen ?
Koda yake ma baridai zan sam abin yi akai adai bari har Allah ya kaimu gobe din tukun na ya fice daga dakin ta dawo da hankalin ta gare ni.
Tace yanzu dai ki kwantar da hankalin ki sai da safe din in Allah ya kai mu jeki ki kwanta har da safe.
Haka na mike gwiwa na yayi sanyi nace sai da safe anty tace Allah ya tashe mu lafiya ki dai kwantar da hankalin ki kinji na fada maki.
Nace tau anty na gode na fice tare da rufo mata kofan dakin ta bini da kallon tausayawa gare ni ta sauke ajiyan zuciya.
Tun da na tun karo dakin na fahinci an shiga min dakin na karasa shiga aiko nan naga kayana a hargitse alaman an tone min kaya ana neman abu.
Bandai san may aka dauka ba na gyara kayan tare da hayewa gado ina ci gaba da tunane a raina dole ne baba yai ciwo abu yai mashi yawa a zuciya yanzu.
Ga nawa matsalan ga na Saadatu sanan kuma ga na gida mazan gidan mu duk ba wanda ya mayar da kan shi abin kwarai.
Dole abu yai mai yawa a zuciya tausayin halin da gidan mu ke ciki ya kamani na kalli kayan da sulaiman ya kashe min kudi a kan su nace a raina ai wanan da kudin ya bani na sai wa yan gidan mu abinci dashi zai kai su har tsawon wani lokaci suna ci.
A haka har barci ya dauke ni sai asuba na falka na yi sallah ina idarwa kuwa na kira ummi ina tambayan ta yaya suka kwana.
Tace gaskiya kan jiya ba ai barci dashi da dadi ba yanzu ma yaya Sani yashigo yana shirin su koma dashi asibiti.
Nace a bashi waya mu gaisa in ji may ake ciki yake fada min wallahi kan baba yana jin jiki yanzu asibitin zasu koma.
Babu kudi da asibitin birni zasu tafi dashi aje can a duba shi a san may yake damun shi nace yaya ko yanzu can zaku tafi.
A ari kudi ko nawa ne idan nazo zan biya yace ai an nema ba asamu aro ba sai nace yaba ummi wayan muyi magana da ita.
Ya bata wayan nake ce wa tabada kudin da zasu sarin kaya tace jiya suka saro kaya dasu nace a je wurin gwagon ta duk inda zasu samo kudi a samu kafin in zo.
A haka muka rabu sunje sun samu kudi kudin dan gidan mama ne kaunar ummi na sadakin shi aka ara nace ba matsala insha Allahu idan nazo zan biya.
Ban fito ba yadda na saba sai ga anty dakin a lokacin nayi kuka idona yai ja ta zauna a kusa dani tana cewa kuka kikayi ne Safiya.
Na dukar da kai ina zubar da hawaye nace anty jikin na baba ya matsa mai jiya wai basuyi barci ba dashi.
Subbahanallahi suko sai su zauna da mutum gida haka yana jin jiki ba zasu kaishi asibiti sai su zura mai ido.
A sanyayye nace da ita wai ba kudin da zasu kai shi asibitin ne suka ce ikon Allah toh Allah ya sauwaka.
Yanzu dai ina gani sulaiman zaki bi yau ku bi jirgi idan kun isa Abuja sai ya saka ki mota da za a kai ki gida yau zasu tafi da shi da daddy can.
Jin tace da daddy zamu tafi yasa hankalina kwanci don da zance mata ta bari in tafi a mota yafi don gudun zargi amma jin da daddy zamu tafi sai hankali na ya dan kwanta.
Yanzu dai ki tashi ki shirya zan fita inga abinda ya dace ayi kafin ki wuce ta fita nikuma na tashi na shiga shirin tafiya.
Su faiza basu san da zancen tafiyana ba sai da na fito don daddy yace ace na fito shine suke tambaya anty ke fada masu mahaifina ne baida lafiya.
Fati tace shine kawai zata bi daddy da uncle don mahaifinta baida lafiya sai dai inda wata manufa zata tafi.
Da sauri anty tace may kike nufi ko may kika mayar damu ne kina nufin mu din mutanen banza ne komay ?
Shiru tayi don maganan itama haka yazo mata nan yar nata tai mata tas sai da ta raina kan ta Faiza cewa tayi zata rakani.
Anty tace da ita kema kin san yayan ki ba zai yarda ba ki tafi kar ma ki dauko wa kan ki wani magana a na zaune kalau.
Haka muka shirya muka fito motan daddy muka shiga zuwa airport din inda anty tai muna rakiya ita da Faiza .
Acan muka samu sulaiman nan sukai shige da fice har aka kira mu tafiya ya tashi ban san lokacin da kuka yazo min ba.
Anty tace dani a a kukan may kuma safiya kamar wacce ta tafi ke nan ashe akwai aiki randa zaki tafi gidan mijin ki.
Daddy yana muna sheri haka na barsu don anty itama ta karaya da kukan da taga ina yi din har sai da jirgin mu ya daga suka koma gida.
A jirgin kujeran su daya da daddy inda na samu wata mace tana da yawan surutu don har muka kawo hira take min a inda take ce min wai tazo ganin mahaifan ta ne a lagos.
Abuja take zaune ita da mijin ta sai dai mijin nata bayerabe ne ita kuma uwarta bayeraba ubanta bauhaushe.
Yaran ta biyu yanzu take tambayana ni a lagos nake zaune nake bata amsa da a wurin anty nake zaune zanje gida ne mahaifina baida lafiya.
Ta tausaya min har ta karbi lambana tace inda mun sauka zata kirani taji lafiyan mahaifin nawa.
Mun sauka duk a tsorace nake don ban taba ko ganin jirgi ba balle in shiga sai gani yau a cikin sa kuma mun sauka lafiya da kudirin ubangiji.
Mota yazo ya dauke mu muka tafi gidan daddy bamu dade ba suka fice suka barni ina zaune tunane ya cika min zuciya zuwa .
Zuwa sha biyu da rabi sai gasu sun dawo gidan sai dai sulaiman ne kawai bai ko son kallo na sosai ya zauna a kujeran yana fuskantana.
Yace sorry ko yanzu dai ki fara isa ga mota nan za a kaiki har gida sai kudi da zan baki ki yi duk yadda ya dace ayi.
Naso mutafi tare amma hakan ba zai yuyu ba don wasu yan matsalolin da nake dashi ki tabbatar anyi masa abinda ya dace dashi don Allah kudi ba matsala bane duk yadda ake ciki sai ki buggo min.
Nace a hankali na gode sai dai akwai kudi a hannu na don wanda ka bani anty ta bani kuma ta kara min wasu.
Yace bana son gardama kin san abunda zaki sama a can ne ya mike yana cewa ki kula da kanki kuma ai mashi duk abinda ya dace don Allah in akwai wani matsala a bugo min in sani .
Ki fito mota na jiranki a waje ku tafi daddy yace in maki sallama aiki ya rike shi bazai samu zuwa kuyi sallama ba.
Ban san lokacin da nakai har kasa ina mashi godiya irin wanan harcin da yai min ba dan haduwan mu dashi haka.
Murmushi yayi yace haba haba ba komai ki dai kula da kanki sai yai gaba na tashi a sanyayye nabi bayan shi.
A waje naga wata mota da driver naji yana cewa driver indan dare yai mashi goben in ban gama ba zai iya kwana ya bude min na shiga ina mashi godiya.
Muka wuce yana daga muna hannu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya ina mika godiyana ga Allah da wanan baiwan da yai min dan lokaci guda.
Motar mu ta halba saman titi ina ta kallon yanayin garin zuciya fam da tunane kala kala muka nausa ga tafiya.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,


🧕🏿3️⃣8️⃣🧕🏿

UBANGIJI ALLAH YA BA MU IKON BAUTA MASHI, BAUTA TSARKAKKEKE,
YA ALLAH KA KARBA MUNA IBADUN MU, , , ,


Tsura ma dan uwan nashi ido yayi yana sauraren bayanin shi daddy yaci gaba da cewa kamar dai yadda aure ya cika kan wanan cutar haka itama aure ne sanadin samun wanan cutan a gare ta a halin yanzu.
Innalillahi yake iya fadi acikin ranshi da fili yace wai kuna nufin wannan yarinyar ta taba aure har an cuta mata irin haka.
Yace cikin garin nan na Lagos tana zauna da miji ta sai dai auren anyi zaman ne a cikin ukuba sai kuma ga wannan cutar ya baiyyana mata.
Ya ce Ya Allah kaza ma gatan mu yanzu wanan abin da mai yai kama mutum yasan cewa yana da cuta a tare dashi amma don ha inci sai yaki fadi har sai ya lika ma dan uwansa abu ya baci adawo ana dodofar tsiya.
Sun dauki lokaci suna magana daya kafin ya mike yace zai tafi har a lokacin ranshi bai mashi dadi sam don abin yadawo mashi sabo a rayuwan shi.
Yai masu sallama anty tana tabayan shi yaushe zai bullo kuma tasa aimai girki sai yace yana dan aiki idan ya rarage zai shigo.
Daddy ya mike suka fice daga gidan tare dashi sun shiga gari tare don duban wasu aiyuka da ya bayar aimashi tun wancen lokacin.
Washegari anty da zancen nama turkey ta dole shi aka dafa mata nai miyan shi nan aka taru a falo kowa na kwasan dafuwa.
Sai da anty ta bari sunyi nisa da cin abincin ne take cewa damu aduniyan nan babu abinda nake kamar wanan namar .
Nan kowa ya shiga fadan albarkacin bakin sa akan naman bandani dana ce ban taba cin shi ba a rayuwana dariya suke min sosai saka su daddy sun shigo gidan shi da Sulaima a bayan shi.
Daddy ne ke muna kallon mamaki ganin irin dariyan da sukeyi din yake tambayan maiyai maku dadi haka irin wanan dariya.
Fatine ta iya bashi amsa da cewa wai Safiya ne ke fadin ita bata taba cin naman turkey ba shine tabamu dariya sai daddyn ya mayar da kallon shi inda nake yana zama a kusa da matar shi yace.
Kauna na kada ki damu da dariyan su watarana sai kin ci abinda duk kan su basu taba ci ba don haka kema zaki rama nan ba da dadewa ba insha Allahu.
Yanzun dai tashi kin ji ki debo muna muma mu dandana muji santin da sukeyi akai don da gani yayi dadi tunda naga Fati yau haka baje baje.
Na mike zuwa hada masu abinci daddy ya kalle matan shi da dariya ya cika yace kar kuyi mamaki zama kauye don nan da wani lokaci ta fiku bude ido .
Dariya ya ci karfinta tace ai bamu haka da Safiya yadda take juya naman a kyamace ne yaban dariya.
Sulaiman ya katse ta da cewa ai cin nama ra ayi ne idan bata so sai a saya mata wani mana taci kuma kuna kallo.
Sai gani na dawo ina ce ma daddy na hada abincin dama na hada tun basu dawo ba anty tace dani to ke kin ji uncle yace tunda mun bata maki rai zai fita dake ki zabi naman da kike son ci a sayo maki muna kallo.
Na da yi mata murmushi nace ni fa anty kin san nama bai damay ni bane kawai ba wai wanan ba.
Kowa wurin yai mamakin jin abinda uncle ya fada do cewa yayi idan baki son nama sai a sayo maki wani abin don haka dana gama zamu fita.
Da sauri na dan kalle shi sai naga ba wasa ga maganan shi sai Fati ne tace Safiya muje mu shirya dama nima ina son fita kin ga sai mu tafi tare.
Anty tace waya kasa dake a ciki babu inda zaki sarkin son yawon tsiya kawai daga jin za ayi fita sai ki ara ki yafa har kina wani muje ki shirya kedin a shirye kike.
Faiza ne tace don Allah anty ki bari mu fita muma mu lakaci arziki ta sake cewa na fada maku ba mai bin su ko ina nice nace amma da twins zamu anty?
Ke kan ana kau da wasu kina jan wasu ai gara zuwa da wa yan nanbda zuwa da wa yancan yan sa maganan.
Shine yace da ita dana ai sune gaba wa yan nan din dai da kika hana su sun hanu babu wacce zamu fita da ita sai dai suga mun dawo.
Nai mamakin jin ashe yana magana mai tsayi irin haka don ban taba jin yayi magana mai tsawo ba duk sani na dashi.
Amma yau tun shigowan su na fahinci akwai canji a tare dashi sosai kodan ganin daddy tare dashi ne oho ?
Daki na shiga ba wani dogon shiga nayi ba dogon riga ne kawai sai dankwalin shi dana yane kaina dashi.
Zama nayi ina tunane ni kadai a daki na yadda zamu fita dagani sai shi sai ga su yan biyu sun shigo da murnan su wai in fito in ji uncle mu tafi.
Sai da na dan bata lokaci na fito anty bata falon sai su Fati ba wani magana mai dadi sai harara da suka raka ni dashi.
Ina tambayan su anty sai Faiza ne ta bani amsa da cewa tashige ciki nace in ta fito ki gaya mata mun tafi tace a sayo dawisu idan anje sai musan ke yar gaban goshin tane.
Nasan magana tasa min ban kulata ba na fice kawai abin yana sosa min zuciya fati ko tsaki naji taja tana bakar magana .
A mota na samay su shida su yan biyu zaune a baya hakan ya nuna min ke nan a gaba nibzan zauna kenan.
Kafin ma in karaso ya bude min gaban mota haka na daure na shiga duk a takure dani muka fice a gidan.
Tafiya muke babu mai magana sai su yan biyu dake ta hiran su a bayan motan basu ko kula mu ba fuskan shi na kallon titi niko na mayar da fuskana gefen da nake zaune ina kallon yadda garin a kullun yake da da girma da bunkasa duk da an dauke headquater anan.
Naji yace Safiya kin san abin da madam ke shirin shiryawa a tsakanin mu ko ?
Na kalli yaran dake bayan motan naga hankalin su baya wurin mu nace a hankali nadai ji tana fadi amma bamu yi magana da ita ba tukun.
Yayi ajiyan zuciya sanan ya nisa yace ya kamata in san raayin ki kiyi hakkuri muyi magana anan don bamu da wani lokaci na sake haduwa irin haka.
Shiru na dan yi kafin in sauke ajiyan zuciya ince dashi to uncle , uncle ina anty ta fada maka matsalan da nake ciki, din haka ni naga kawai ayi hakkuri ba abu bane da zai yuyu a tsakanin mu.
Saboda gaskiya sai na kasa magana karshe dai nace uncle mudai yi hakkuri kawai ya dakatar dani da fadin saboda may zamuyi hakkuri da maganan bayan abune wanda zai yuyu.
Ko bata fada maki cewa nima a halin da nake ciki ke nan ba sai na dan kalle shi kadan yace yes nima victim ne amma sai wanda ya sani zai sanda hakan.
Idana na kallon kasa look safiya ba wai abune da zamu tsaya muna yi wa juna kwana kwana ba da maganan.
Ina son ki sani wanan abinda mutanen nan suke kokarin hadawa a tsakanin mu gani sukayi mun dace da junane.
Ina son ki sani koda wanan matsalar ko babu shi akan mu wallahi ni son ki nakeyi tsakani da Allah ina mai tabbatar maki ba zan iya hakkura dake ba a yanzu.
Ya nisa ya sake cewa wallahi ina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login