Showing 39001 words to 42000 words out of 269010 words

Chapter 14 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13367

ya gane gaskiya ya daina su kuma zai fahinci kutungwila da suke shirya wa a kanki.
Nace mhm anty kenan sai dai don kin ce Allah ya fasan gaskiya wani abin da biyu yake min shi don kawai ya kuntata ma rayuwa na.
Tunda dagani har iyayyena babu wanda yake shakkan zagi yadda rashi yaso idan yana jin tsiyan mutumin da kullun a buge yake in baisha da safe ba da dare zai sha.
Amma nai hakkuri da hakan ina zaune shi don bin maganan iyayye in yai amai na kwashe anty in yasha giya anan inda kike zaune zai bar kofi ko kwalban in dauke.
Haka zai shigo cikin mayen shi yai ta surfa min a shar ya danne ni da karfin tsiya yayi abinda yake so dani na karasa fadi cikin kuka.
Maman biyu tai tagumi tana saurare na cikin jimamay abinda nake fadi ina kuka.
Zuwa can ta nisa tace sai hakkuri Safiya don zaman aure a yanzu hakana ya kunsa ko wani gida da tasu lalurar idan kuma kin ga zaman wasu sai ki daga hannu kiwa Allah godiya ke.
Nace a hakan maman biyu har akwai macen da tafini wahalan aure a duniyan nan tace naki kika sani safiya Allah daiya kyauta zamanin nan.
Nace ni maganan mahaifina da yace idan na neme saki a gunshi da bakina bai yafa ma haihuwan da yai min ba.
Tace to kin gani ko sai hakkuri karki gaji da hakkuri kuma ki rike ibadan ki kina yin adduoin da hannun ki bibiyu bada wasa ba.
Ina kuka ina mata godiya tace zata tafi amma zata dawo kwana biyu ta duba ni in Allah ya yarda.
Nai mata godiya ta tafi ta barni ni kadai a cikin damuwa da tunanen rayuwa mai kunci da nake ci a gidan.

********* ********* *********
Na mike na shiga daki dakin duk yayi kura na rashin mutum a cikin sa duk da jikuna da dan sauran tsami amma haka na daure na gyara shi har zuwa falon gidan da duk yai kura nasan ko sau daya bai taba gyarawa da ban nan.
Sai zuwa marance na gama har da girki da na dora na shiga nai wanka na fito na gyara jiki na sai yamma lis ya dawo gidan daidai lokacin da nake fitowa cikin daki ya shigo.
Cike da girmamawa irin na macen da tasan darajan wanda take aure na gaida shi da dawowa bai takan ni ba sai umhum din da yace dani.
Nan ya zauna saman kujera yana debe takalman kafan shi da safa sai na je fridge na dauko mashi ruwan sha ban kai ga kawowa ba ya dakatar dani fuska daure yace ni bance maki ina bukatan ruwa ba.
Da sauri na kalli idanuwan shi kamar zanyi magana amma kuma sai na juyana mayar da ruwan ida na dauko da farko.
Ya na cire takalman ya shige dakin shi baiyi magana ba nidai ina tsaye daga kofan kitchen na bishi da kallo kawai.
Abinci na dauko na jera mai saman dan taburin cin abincin dake falon na juya na shige ciki abina tare da turo kofan dakin.
Can bayan kamar awa daya naji yana turo kofan dakina ya shigo yace ke nazo in maki kashedine akan fada wa Saadu sirin gidana da kike yi.
Ban taba zaton munafuncin da mummy ke fadin uwarki nadashi ya shafe ki haka ba sai yanzu.
Da sauri na dago kai don jin abinda ya fada gamay da ummina ina kallon shi cikin mamaki.
Nace ita gwago tace ummina muna fukane ita yaya akayi ta sani ko ta taba yi mata munafuncin ne .
Yace karya mummy zatai mata kike nufi komay ?
Nace wai may yasa iyayyena basu da daraja a idon ka baka jin nauyin fada min magana a gamay da su.
Ya a cikin tsawa wanan ke ya shafa kin dai ji na fada maki in ba haka ba daga ke har saadun zaiyi karanku ina ce tare kuke kuna cin amana na.
Da sauri na sake dago kai na kalle shi a cikin mamaki abinda ya fada na wai zai muna kazafi dani da yaya saadu akan muna tare .
Ya ce eh muddin baki daina jawo mani shi a gida ba abinda zanyi maku kenan a gidan nan ya juya ya fara takawa sai kuma ya juya yana cewa uhmhum dama ina son in tanbaye ki
Ina son insan wanan matar mai zuwa a inakika santa ne uta din wacece may ye alakarki da ita da take taimaka maki haka.
Nai shiru ban bashi amsa ba saida ya sake maimaitawa na ce yar uwar ummi na ce ita a kano take acan tai auri wani babban sojja ita din kuma custom ce.
Da sauri yace mayne ita din da nake gani custom ne ashe no warder take abu a gadaran ce don tasan abinda ta taka.
Nidai ban tanka shi ba sai shirun da nayi kawai yai huce ya fice daga dakin na sauke ajiyan zuciya tare da fadin Allah ya sauwa ka.
Kwana biyu ba wani fitina a gidan idan ma zaiyi shedan shi bai yi min a falo saidai ya shige daka cikin dakin shi ya dadaki giyan shi yayi talil ya lamay a wurin.
Dan kwana biyu jani shakat a raina ga maman biyu tazo ta kawomin abinci na boye a dakina duk da shima ya sayo koma amma bata yarda tuban mazuru ba tace indai boye wanan.
Na kwasa nakai dakina na boye tana shirin wacewa ne ya shigo gidan basu hadu ba tun ina aaibiti sai yau din nan suka sake haduwa dashi.
Ya shigo yana ganin ta yadan sake fuskanshi suka gaisa sai a lokacin ya samu yi mata godiyan dawainiyar da tayi damu a asibiti.
Ta katse shi da haba babu komai ai, adaiyi ta hakkuri koda yake nasan kana yi sai ka kara kasan safiya yarince karama bazaka hada hankalinta da naka ba.
Ya dan sosa kai yace ba komai komai ya wuce ai na gode kwarai ta mike tana saka hannu a jakar ta kamar yanzu ne zata sallame ni tace ke kuma karbi wanan kyadan rike karki dami mijin ki da bani bani.
Zai shige ciki tace ya tsaya shima ta debo ta bashi yana aaa amma ta matsa mashi ya karba na rakata har waje ta tafi na shigo ciki.
A falo na samay shi tsaye yana jirana ina shigowa ya miko min hannu da cewa na kawo kudin nan da ta baki nan na dago da mamaki ina kallon shi.
Ya sake fadar miko min su nan nace kuma idan kika kuskura kika fada mata cewa na karba sai na lalatsaki a gidan nan.
Jiki na rawa na mika maisu ya shiga kirgawa yaga dubu biyar ne nashi kuma goma ya hada yace sha biyar kenan.
Ya tura a aljihun ya shige dakin shi ya dade da shiga ina kitchen naji muryan shi yana cewa ni zan fita idan kinga nakai sha daya ki rufe gida bazan dawo ba a xan zan kwana.
Nace dashi to kawai ya fita ya sha kananan kaya sai kamshi yake nace a raina yau an samu kudin sheke aya ke nan.
Kamar yadda ya fada bai dawo gidan ba sai safe ko safen sai wuraren sha dayan rana shigo man har zuwa lokacin bai gama warwarewa ba daga mayen shi.
Ya shigo ido yai mai ja sai zage zage yake zubawa ni dai ina daki ban fito ba har ya gama ya fada dakin shi ya bingire sai barci.
Bashi ya falka ba sai karfe hudu na rana koshi yunwa ta tayar dashi ba ibada ba ko wani abu don daren jiyan da yake jin kudi a aljihun shi club yaje suka kwashi rawan su suka sha giya da matan banza su gama suka shiga sheda da matan a wurin.
Ya fito ya samay ni zaune ina kallon wani film din magic ya samu wuri ya zauna fuska daure yake tanbayana abinci fa.
Na dago nace dashi babu nama ya kare hakana na dafa abincin don shi baicin abinci ba abin miya a ciki.
Har zaiyi magana sai yai shiru ya ja tsuki yana fadin zubamin hakana don yunwa nake ji haka na zubo mashi ya lashe daki ya koma ya kwanta.
Babu batun cika ibada gare shi don ba zance yana cika sallah shi ba don ko da safe sai ta hantse mashi zai tashi haka kuma da rana ko yana zaune akai sallah baya tashi yayi sai jefi jefi yakan yi.
Yau ma shirin fita yake a gidan sai naji sallaman yaya saad ya shigo har na taso da yar fara a ta zan tare shi sai na tuna kashedin da yai min a kansa.
Haka na tare shi kadaran kadaham nai mashi sannu da zuwa yake cewa lalai kauna ta jiki yai dama ya zauna a saman kujera yana cewa ashe kana ciki a dadaure ya bashi amsa umhum.
Shika yaya saadu ya share shi ya shiga tambaya na yana kuma min hiran tafiyan su har kasan togo suka tafi.
Ganin ban saka ba kamar yadda ya sanni sai ya dan shiga tsarguwa a take ya fara tambayan make faruwa ne Safiya ki fada min ni yayanki ne fa.
Na share kwalla dake fuskana nace dashi ba komai yaya saadu ya mayar da duban shi a kan dan uwanshi da ya mayar da hankalin shi ga abin da yake yi da waya shi yace .
May ke faruwa ne bros.
Sai yace ai gata nan ka tamabaye ta kaji abin da ya samay ta din ya matsa min da tambaya nace don Allah yaya Saadu ka bar zuwa don yaya yace zai kulla muna sheri ni dakai wai tare muke a gidan nan.
Mikewa naga yaya saadu yayi yana huci yake fadin kaika dade baka kulla muna sheri ba.
Ban san rashin mutuncin ka ya kai hakka ba sai yanzu don ta na yar uwa nace kaga ina kula mata inda wata ne can bare ka dauko ba abin da ya damay ni da ita.
Wanan wani sallon yaudara ne ka dauko kaika dade bakai muna sheri ba cike da tsoro na ke magana a, a yaya na fada mane don kawai ka dauke kafan ka.
Na sake cewa cike da tsoro na dan kalle shi nace na fada ma a gaban shi ne don ka san gaskiya nake fada don ka kiyaye.
Ya dago jajayen idonuwan shi ya ce dani indan baibar shiga maganan ki dani ba a gidan nan zan iya mashi komai tunda bai da mutunci.
Bai kai aya ga maganan shiba saiko yaya saadun ya taso mashi kamar zai dake shi da kyat na samu suka hankura ya fice gidan a fusace.
Ranan nasha duka sosai a wurin shi sai dai bai yarda ya kaini kwance ba amma na zagu a gurin shi .
Ban damu ba don zargi da sherin da yake son muna da yaya saadu shine abin da ya tsaya min raina tun lokacin da ya fadi hakan.
Amma yau sai naji na samu sukuni akan wanan maganan na gyagije naci gaba da har kokina kamar kullan.
Na koma yin kitso idan yakawo in dafa muna kowa ya ci indan bai kawo ba kuma na dan jawo kayan abincin da maman biyu ta kawo min na hada wani abu na ci.
Wani lokaci haka zai dawo gidan da abin amfanin gida duk ranan da naga ya shigo haka nan nasan yar arzikin na a kai.
Zai zauna baisha min taba a falo ko giya ba sai dai yai ta yawan waya da matan banza ranan kuma duk matar da tazo kitsu ranan sai dai ta koma bakitso don bai bari nayi .
Yakan zauna ranan mace nake yakan wuni darza na sai ya gaji ya kyaleni don kan shi indan yai haka yakan dade bai neme ni ba kuma sai lakacin da yai mashi dadi a rashi zai kara kusanta ta.
Ranan da naje gaida gwago dakuka na dawo gidan mu don tun case din da na fada ma yaya saadu abinda ya fada ashe sun je can gabanta suyi kaca kaca da juna su a gaban ta.
Tun wanan lokacin taka nema na ta fada min kada inyi sanadin raba kan diyan ta da munafunci na dana iya a tare na gansu kuma tare zan barsu.
Idan na kara hada diyanta fada sai daukeni ta mayar dani gidan matsiyacin ubana naje can mu karata can dasu.
Zagi ta ida take shiga ba nan take fita na har cewa tayi wanan kaddararen aure nawa da ta tauye ma danta jin dadi dashi.
Ban wani dade ba don ko ruwa ban sha ba a gidan na juyo na dawo gida ina kuka a idanuwa na,
Nazo kofan gida na samu maman biyu tazo gidan bata samay ni ba tana shirin wuce wa sai gani tafe ina sharan kwalla a idona.
Ta tsaya da mamaki tana kare min kallo tare da tambaya na ke lafiya kike tafe kina kula haka .
Nan nake fada mata duk abin da ya faru a bayan ta har dukan da yai min tace wanan mijin naki ya zama abinda ya zama sai addua kawai gare shi.
Ina kuka nake cewa da ita ni gaskiya gidan mu zan koma na gaji da wannan halin baida ranan gyara halinsa sai dai gaba gaba dakeyi.
Tace kada ki fara cewa zaki gidan ku don mahaifin bazai barki ba ba kuma zai goyi bayan kiba don haka gara ki zauna kiyi hakkurri da halinsa tunda kin saba yanzu.
Mutun sai kace mara imani komai a ziciya har yanzu fa bai daina abin da yake yi ba yanzu har rashin kwana a gida ya tsiro dashi.
Tace kardai ince wurin matan banza yake kwana ta fiddo ido waje don mamaki tace wanan kuma sabon sirfan da ya dauko don mugunta fa.
Nan na soma kuka ina fadin san anty ba sona suke yi ba sin cuce ni sun cuci iyayye na, sun muna rufa rufa an hada ni da alkakai na soma kuka wiwi.
Tace meye haka kuma Safiya so kike ki tayar min da hankali nima cikin kuka nace da ita ba haka bane anty.
Wallahi ni kadai nasan halin da nake ciki yanzu haka abinci sai yaga daman bani zai kawa a gidan nan ga uwar shi har fadi tayi wai ina mashi wayo ina karbe mai kudi.
Kenan ashe tasan dan ta yadda yake amma taiwa mahaifina rufa rufa ta aura wa danta ni hakana.
Hakkuri tai ta bani kan indan kara bashi lokaci idan bai daina ba zata bani kudin mota in koma gidan iyayyena da zama.
Ranan bamu rabu ba sai da ta kaini har gidan ta na gani kamar ba a kasan nan suke zaune ba mutum zai dauka a Amerika yake don kyawon shi.
Naci na sha ta bani kyautan suturu masu kyau da tsada dama tun da nazo ko kyale bai taba hada ni dashi ba.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGO, , , , , , , ,


🧕🏿 1️⃣4️⃣ 🧕🏿


YAR UWA WANAN NOVEL NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,


Tafiyan dare mukayi sai wajajen sha daya da wani abu na rana muka isa garin mu duk jikin yai min tsami dama yaya jikin yake balle an tabashi kuma.
Mun sauka yaya ya nema muna mashin muka hau zuwa gidan mu tare da kaya na niki niki shi yai wahalan daukan kayan da kansa.
Suna hada hadan su na safe sai jin sallama na kawai sukayi yara suka dauka ga Safiya ga safiya tazo.
Da gudu kanena suka sheko suka rungumay ni suko su mama sun fito da mamaki suna kallona mama ne tace safiya kuna tafe ashe ke daya ne take sai idanuwa suka ciko da kwalla.
Na shige dakin mu ina kuka shigowan yaya Sani da kayana niki niki ya na kokuwa dashi yasa aka samu masu taimaka mashi daukowa.
Kowa sai mamaki yakeyi sunyi tsaye cirko cirko suna mamaki Inna tace babu lafiya kan gaskiya.
Wanan tafiya da gani bana dadin rai bane sai aka fara lekowa don gulma wai ana gaishe ni da zuwa sai a fita ana dariya waje don sheri.
Inna ta koma kan yaya sani wanda ya gama aje kaya a wahalce dashi ta tsare shi da idanuwan ta tana cewa daga ina ka tsinto Safiya kai kuma.
Baiyi magana ba sai samun wuri da yayi ya zauna yana neman ruwan sha yana jin inna ta matsa tambayan shi saida ya gama kwakwadan ruwan shi ya sauke numfashi.
Ya dago kan shi yana fadan can lagos mana inna sai ya mayar da kan shi a kwanon da yake shan ruwan.
Cikin mamaki da dafe kirjin ta tace har lagos katafi ka dauko ta dakin mijin ta kana ko da hankali kuwa.
Sunyi tsaye akanshi cirko cirko suna sauraren shi maimakon ya yi magana sai ya mike kawai ya fita daga gida batare

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login