Showing 168001 words to 171000 words out of 269010 words

Chapter 57 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13364

da da mama zasu tsaya sai kuma aka tsaida shawaran mummy ta tsaya su yaya Saadu zasu biyo tanan sai su dauke ta.
Amma kuma na fahinci yan uwanshi kamar basu jin dadin shi kamar yadda Faiza ta taba gaya min amma dai koma may ne yanzu tun da Allah ya jefani cikin su da sannu zan fahinci komai.
Washe gari dukan mu muna zaune gaban hajiya baaba tana muna nasiha sai lokacin take ce ga yar kanin ta nan zahar ta karbo muna zamu zauna da ita .
Koshi ashe baisan da maganan ba sai naga yayi saurin dagowa yana duban mahaifiyar tashi don kawar da komai da sauri nace mun gode baaba Allah ya taya mu riko.
Tace keda kika fishi hankali baki ki alherin da nai maku ba amma shi har yanzu ban san abinda yasa baka mantuwa ba a ranka ana son musulmi da yawan yafiya ko yaushe.
Murmushi yayi yana mike wa tare da sosa kan shi yace hajiya mu zamu tafi ai muna fatan alheri.
Addua ta shiga kwararowa tana bin mu da fatan alheri har muka fice part din su gwago kan har an shiga motar da zata kaimu airport.
Sai da muka sauka ne naga ashe da Aishan shi zamu tafi zata koma itama gidan mijin ta tare muka shiga jirge gwago kan sai kama mummy take yi.
Mun bar yarinyar zata biyo driver da zai zo da motar da sauran kayan mu don suma sammako zasu yi don su isa da wuri.

Mun isa lafiya motaci biyu suka zo daukan mu zuwa gidan shi harda Aisha duka muka tafi gidan nasa.
Mun samu an kara gyara gidan anyi abinda ban san gidan dashi ba ya kara wani kyau da daukan ido na juyo na kalleshi da mamaki ya gyada min kai kawai yana lumshe idanuwan shi.
Gwago da mummy sun kasa boye farin cikin su na ganin gida sai yaba kyawon gidan suke yi har muka zauna nan mai aikin shi ya fara gabatar muna da abinci.
Mun ci mun sha a tare dasu mummy da Aisha don shi ana sauke mu ya shiga ya canza kaya ya fito bayan ya nuna muna dakuna ya fita.
Tare da Aisha da mummy muka gyara dakin da ke zaman nawa tana da sakewa sosai don tana jana da hira sai dai nine ban sake jiki da ita ba.
Take fada min yaran ta uku yanzu duka mata ta barsu nan Abuja ne a wurin kishiyar ta nace Anty Aisha kina da kishiya ne?
Tayi murmushi tace mu uku ne ai dayar tana can bauchi don a can take aiki ita kuma dayar da suke nan dama anan ya aure ta.
Sauke ajiyan zuciya nayi batare da na kara magana ba sai naji tayi dariya tace kwantar da hankalin ki yaya na mai son yawan tara iyali bane.
Idan kika dubi yanayin shi rayuwan shi kaf na turawa ne don dan kaida ne shi sai kinyi da gaske kafin ki fahince shi amma idan kin fahince shi zaku zauna lafiya.
Ina son ki jajirce wurin hakkuri da kawar da idon ki a alamuran shi bai faye son mamuwar mutane ba don Allah Safiya ki taimaka muna ya ja mu a jiki dan yazo kice kadai hope din mu.
Murmushi nayi kawai nace a fili Allah yasa tace yayana yana da saurin fushi amma kuma yana hucewa a dan lokaci musasnman idan kai mashi laifi ka bashi hakkuri.
Tace ina fada maki halin shi ne don ki kiyayye don naga kamar ba wani sanin juna kukayi sosai ba.
A raina nace ashe akwai aiki kuwa ashe ganin kitse saman ruwa nake mashi ke nan sai naji tace idan kin ga ya tashi bai son magana kada ki damu kanki kidan nisance shi sai ya nemo ki don kada ku samu matsala tace bani wayan ki in saka maki layi na don mu ringa waya dake.
Na mika mata tasa layin ta ta kira ya shiga tayi adding dina a contact din ta isowan driver da kayan mune yasa mu fitowa daga dakin muna taron su.
Nan dai Aishan ta taimaka min muka kawar da kayan komai mukai mai mazauni munyi sallah la,asar mijinta yazo ya dauke ta tana mai ce min baya sati zata shigo ta duba mu.
Bayan tafiyan ta na sauke ajiyan zuciya naga yanzu may abin yi nan na fara shawaran ko girki zan dora muna amma sai na samu har mai aiki ya gama ko yana shirin wuce wa gida.
Wuein su mummy na koma na zauna nan muka fara hira dasu mummy ke cewa dani taji abinda kaunar mijina le fada min dazu don haka take son fada min .
Inyi amfani da baiwar da Allah yai min na mace wurin canza mashi halayen da suka ce yana da musali idan yai fushin ba kaucewa zan yi ba kokari zanyi in jawo shi a jiki ta hanyan yin kwalliya da girki mai dadi da nasan yana so.
In kuma tabbatar da na hada da addua da yaiwata sadaka din ganin haske ga alamarina in kuma yi kokari in koya mashi bin yan uwan shi ya saba dasu amma indinga boye sirina dana mijina tsakani na dasu .
Do ba komai nai ya kamata su sani ba tace kinga wanan yarinya da aka hadoki da ita to itace ido da kunnuwar uwar mijin ku.
Don haka koda zaki sake mata ba irin sosai din nan ba kada ki dingayin abu a gabanta do shine zai sa ta dinga kwasa tana fadi a gida.
Ga kayan kwalliya ga sutura Allah ya wadataki dasu don ha ki daure da yaiwata kwalliya ajikin kina lamshi da saurar su zurfin karatu ba shiba ba indan akwai kudi babu abinda mutum ba zai iya ba sai ki dan more ma wanda kika samu a baya.
Sai dai mijin nan naki naga mai wayayyen kai ne mai yuwa ya barki ki koma makaranta ki kara ilimi.
Nan dai muke sai biyar da wani abu ya dawo gidan lokacin naci kwalliya da wani English wear a jikina ina tsaye ina magana da zarah a falo yashigo gidan.
Sannu da zuwa mukai mashi nida Zarah bai amsa ba sai kallon zarah da yayi bat ta bar wurin kai tsaye yanufo inda nake tsaye.
Kai tsaye ya hada bakin sa da nawa ya manna min ragowar lemon plus din dake cikin bakin shi na rufe bakina da sweet din ina ce mai thanks.
Yace kin ga irin gaisuwar da nake so daga gare ki daga yau sai ki saba dashi murshi na sauke mai laushi.
Ya koma saman kujera ya zauna na wuce na dauko mai ruwa mai sanyi na kawo mai tare da kokarin zubawa a kofi ya dagakatar dani da amsan goran ya kwankwade ruwan roban gaba daya.
Yana sauke numfashi nace bakaci komai ba tun karyan safe ko?
Ido ya lumshe min na koma kitchen na hado mai kayan bukin da muka zo dashi na da alkaki da goran juice ya karba yana min godiya.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/15/20, 7:51 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,


🧕🏿5️⃣6️⃣🧕🏿


NOVEL DINA NA KUDINE KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA NA SAUKE HAKKINA A KAN KU MAI FITARWA KUMA UBANGIJI YA BI MIN HAKKINA AKANTA KO WACECE.


Bazan gaji da jan Allah ya isa ba a kanki mara tsoron Allah don ki gyara masu kike daukan nauyi a kan ki don baki san nauyin Allah ya isa ba zaki fadi ranan da nadama zata riske ki ko zata riskeka yadda baka/ki fasa fitar min ba nima ban gajiya da bin hakkina a kan ku dabara ta saura gyaraka/ki mara zuciya da gudun goben ta
Duk da gajiyan dayake tare da shi bai hanashi mike wa yana ce min sorry na barki ba bayanin komai a gidan.
Kamoni yayi ya mikar yana fadin muje kiga tsarin gidan naki ko ban musa ba na bishi yana rike dani yake nuna min ko ina na gidan.
Sai naga ashe kallon tsoro nakewa gidan dama duk ban san komao ba a tsorace nake kallon gidan ashe yace da fatan komai yayi maki yadda kike so.
Murmushin da yake so nayi masa daidai lokacin da muke komawa falon don zama yace yanzu may kike son a karo maki a gidan koda na nauin kayan kitchen ne nace komai yayi a yanzu daga baya idan ina so zanma magana.
Hannu na ya kamo ya danka min mamullaiyan da alama na gidan ne sai wani wanda ban fahinci ko na maye ba.
Kallon mamaki nake mai sai naji yace makulin motar ki ce tana waje aje sai ki shirya koyon mota yanzu sauran kuma na sauran dakunan gidan ne don ni ba zaunin gida ba ne koda bukatan shiga ya taso maki.
Ban iya magana sai mikewa da nayi na durkusa a gaban shi gwiwoyi na biyu na saman carpet din falon hannaye na biyu na dora a kan cinyan shi na fara zanbga mashi godiya.
Yace No no stop it safiya do you know how much i care for you?
Na gyada mashi kai hawaye na zuba min a idona bayana naji ya fara shafawa a hankali tare da share min hawayen dake zuba min a fuska da hannunshi na dama.
Cikin raunin murya na craking nace uncle dole in yi kuka ka nuna min kaunar da ban taba zaton samu ba a rayuwa na.
Sai naji ya sunkuya ya rungumoni zuwa jikin shi ya na zaunar danu saman kujera yake fadin you deserve morethan this a wurina kin dawo min da farin cikin da na cire tsanmanin zan sake samu a rayuwa na.
Yan zuma haka in bakiyi hankali ba ina dap da in baki kaina gaba daya ji nayi kamar dariya zai kubce min a hankali na zare jikina daga nasa na zauna kusa dashi.
Gaba daya rikewa bayi wai yau nice a cikin wanan rayuwan da na dade ina mafalkin samu wanda sai dai inga anayi a tv ko wani gida gani yau na tsinci kaina ciki tsundon.
Sai nake ganin abin kamar yar koyau na koma don ban saba da irin wanan rayuwan ba tun daga farko ji nayi yana tsiyaya lemon dake gaban mu a cup ya dan kurba sai ya miko min sauran gaba daya na zuke.
Naji muryan shi yana fadin baki ce min komai ba batun kara karatun ki ko da yake idan son samuna ne ki zauna gida as a house wife zai fi min dadi naki jinin mace mai yawan fita a rayuwa na sha fada maki hakan a baya.
Zan maki kokarin da duk wani abin da zaki bukata na rayuwa idan kin yi laakari da irin halin da muke ciki na rayuwa rayuwan ma har nawa take a gare mu yanzu ?
Na dago idanu na dan kalle shi kadan sai naga ya zuba min idanun shi yana yana sauraren amsan da zan bashi.
Haka yasa nayi saurin sauke idanuna kasa ina wasa da yan yatsun mu dake hade a hankali na iya furta mashi uncle na hakkura da karatu.
Kin hakkura fa kika ce da karatun na kada mashi kai alaman eh yanisa yace saboda may ke fa kika ce min kina sha, awan karatu a baya .
Na nisa nace yanzu na fasa a hankali.
But why , ?
Ko dan abinda na fada yanzu ne kika fasa cika burin ki ?
Nace a hankali eh to duk mai hankali yayi tunane haka din ne don may kuma nake bukata ga karatu yanzu banda in zauna dakina in nemi ladan aure.
Don maganan ka gaskiya ne har wani rayuwa zai ba ni shawa yanzu kuma bayan wanan da nake ciki indan nayi duba da dafin mutuwan da ke a jiki na karatun ma karshen inyi ban mora ba gara kawai in zauna in rugumi kaddarata da hannu biyu yafi.
Yace hakan yayi maki don ban son daga baya ki koka dani ko kadan duk da zanyi iya kokari na wajen kare maki hakkin ki dana bukatun ki.
Na na insha Allah yayi min zan zauna in kula da gida da bukatun ka na lura kaima hakan yafi maka don dai kaga ina sha, awan karatun ne ka mara min baya akai.
Guntun Murmushi naji yayi mai alaman da magana na dago kai na kalle shi sai yace hakan na dakyau don kin fara cinye jerabawan da nake gwadawa akan ki.
Saboda haka nayi maki alkawarin zaki rika amsan albashi kamar yadda nake ba sauran maikatana duk wata.
Katse shi nayi da fadin a a Uncle gaskiya ni hakan ya, , , , ji nayi yarufe min bakina da hannun shi tare da fadin Shhhh, , , , .
A hankali yace min shine magana na don may ake aiki ba saboda neman kudi da tallafa ma kaiba don haka shawaran da na yanke ke nan a kan rashin karatun ki.
Duk kuma lokacin da naga kin samo sallon batani da irin takon ku na mata sai in canza raayina zuwa wani nauin don kin san mace bata da wuyan bata namiji da halin ta don gashi kwana nawa da auren mu har kin koya min rasgin zama gurin aiki gashi yanzu sai da na dawo gida don ki.
Mikewa nayi tsaye ina kokarin gudu cike da jin kunyan shi amma sai ya kamoni zuwa jikin shi yana fadin.
Where do you think you are going ?
Yana sakin dariya yana kokarin janyoni jikin shi ina fadi kada mummy tafito fa ta samay mu haka yace may zai kawo mummy nan part dina.
Da kyat na samu ya sake ni koshi don an fara kiran sallah ne a lokacin don haka muka watse zuwa sallah.
Da dare har dakin da su gwago ke ciki ya samay su akan yana son su fito muci abinci tare dasu basu so ba amma haka suka fito yana jan su da fira har suka sake jiki da shi suna cin abincin.
Bayan mun gama na kwashe kayan ya zauna dasu suna mashi hira anan yake fahintar yaya Saadu company da yake aiki dasu yanzu sun durkushe.
Ni dai daki na koma na fada wanka don naga sabon angon nawa ba na wasa bane wurin son tsabta da lalubar mace bayan na shirya waya na dauko muna magana da Amina don wani ruwa da ta bani ina son tai min bayani akan shi.
Nan muka tsaya tana min hira bayan komawan su gida yadda suka kwasa wirin rabon kudin da aka basu tukwaici acan.
Kofa naji an turo ko ban duba ba nasan cewa shine ya turo kofan dakin ya shigo yana tsaye da jallabiya baka mara hannu.
Ya rike cup yana shan abu a ciki sai dai bani iya cewa ga abinda yake sha a cup din kai tsaye ya nufo ni sai da ya zuke abinda yake shan ya tambaye ni da kin sha maganin ki kuwa ?
Kai na girgiza mashi alamar a a zama yayi yana fadin dauko tare da fadin kina wasa da shan magani ko safiya baki san in kin kiyi kwana daya baki sha ba zai iya tambayan ki ba.
Mikewa nayi na bude wardrobe dina na dauko kwalin maganin ina barewa sai yace miko min in gani ya karba ya dan duba sai ya miko min tare da fadin akwai wanda na anso a italy zan baki ki gwada sai dai yana da matukar karfi sosai idan kin sha zai sa ki cin abinci sosai amma yana aiki sosai a jiki.
Kofa na nufa don in dauko ruwan da zan hade maganin dashi sai naji yace dani no barshi in munje daki kya hade.
Kallon shi nayi da sauri yace yes dakina zamu yau ko kin fison kullun dan kwali ya jawo hula har a saka muna ido a gidan.
Don ni gaskiya ba yanzu nake son gwago ta koma ba so nake ta dan zauna damu na dan wani lokacin kafin a maida ta in son samu ne har da mummy din don matar na da dadin zama.
Murmushi nayi nace uncle ai sai kasa a zage mu daga kawo amarya sai su samu wuri su zauna.
Ina fadi kamar zanyi kuka yace common wa zai san ma suna gidan nan balle a fadi haka ko baki son zaman su ne sun takura maki keda angon ki.
Wani kallo nayi mai na ba haka bane sai naji ya sukkuce ni bai tsaya dani ko ina ba sai tsakiyar gadon dakin shi.
Da kyat ya barni na sha maganin nawa duk rokon da nake mai baijini ba sai da yayi abinda yake son yi ya samu natsuwa.
Washe gari su yaya Saadu suka iso Abujan don daukan mummy su tafi amma sai Uncle ya dinga masu delay da tafiyan sai da suka share kwana hudu tare da mu.
Ranan da zasu tafine yaya ke gaya min Uncle ya dauke shi aiki a company shi tare da bashi wuri zama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login