Showing 159001 words to 162000 words out of 269010 words

Chapter 54 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13370

sha.
Da yardan Allah komai mutum ya dauko a kanki sai dai ya koma mai badai ya kamaki ba.
Wayana yai kara sai na mike na koma daki na bar gwagon nan falo zaune da ummi da su Aisha.
Na dauko wayan da sauri gabana ya fadi don ganin lambar anty na kira na a lokacin wada dama ina tsamanin hakan ko yaushe.
Na dauka da sallama ta, sai naji ta katseni da cewa amarya ke nan ke nan kai duniya ina zaki damu ashe tsintaciyar mage dai bata taba zama mage.
Lalai mutane sunyi gaskiya da suke fada min cewa ke din tsintaciyar mage ce a gare tabbas ko ya tabbata hakane.
Kafin in magana sai naji ta kashe wayan ta dip ajiyan zuciya na sauke tare da sake murmushin bakin ciki lokaci guda.
Na a sanyaye na fito falo inda suke na zauna ban iya cewa na fahinci hiran su alokacin sai da naji tace ai kinga idan yaro ya na dauke dauke zaki samu kaucin malge a samu kashin mai satan a hada da malgen a shaya in ya bushe a daka in ya zama gari sai a dinga sa ma mai shi a kunu ko shayi yana sha har kwana bakwai da yar da Allah zai bar satan don da yaje daukan abu warin kashin shi dayaci zai hana shi daukan abu yaji satan ya fice mashi a rai.
Sai kuma mallaka da sai abinda kika ce a gidan zaki samu kaucen gwanda na daji ki dake shi ya zama gari a samun kan tunkiya da ta kosa adafa su tare in ya dahu sosai ki zauna kici duka amma bada kashin ba.
Allah sa mu dace naji tace sai lokacin na kallo ta ina cewa ummi yanzu anty ta kirani fa.
Da sauri tace yaya kukayi da ita ta sake fadin taji ke nan dai ko ?
Na gyada mata kai da alaman eh gwago ne tace may taji auren sai ummi tace eh gwago tace dama bata sani bane Aisha dake zaune ummi ta kalla sai tayi shiru.
Na ce ummi ai yanzu ba maganan boyo bane tunda abin na ta kamari tace wai may ke faruwa ne kumbar mu a duhu haka ?
Ummi tace ummi kin san sun samu matsala da uwar rikon nata tace subbahanallahi shine baku fada muna ba asan abin yi.
Ummi tace abin ne wallahi da daure kai zaman su ba wani matsala sai daga baya ne kuma wani hali ya shigo masu.
Don ita bayan ta hada su da kanin mijin ta sai kuma daga baya bata son hadin wai tana son hada shi da wata yar yar uwar mai gidan ta.
Shine ita ta risketa tana waya suna fadin wai zasu zo suyi kata korar kare a gidan da take zaune shine shi wanda ta aura din ya bata shawaran ta dawo gida.
To shine da nake fada ma malam halin da suke ciki sai malam din ya yanke shawaran cewa da sun zo tambaya sai a daura aure da yani.
To yanzu nasan taji ne shine wai ta kirata yanzu din sai gwago tace may tace dake to ?
Nakwashe abinda ta fada min na fada mata sai tace aikin banza ai Allah ya riga yayi ikon shi ko a kan su yanzu sai dai hakkuri.
Nace ni yanzu ce min da tayi wai tsintarciyar mage bata zama mage shine abin ke damu na wallahi tana ganin nice na yaudare ta ko may gwago ?
Tace kun ga yanzu duk ba wanan ne a gaban mu ba koma may ye idan kin tare daga baya sai ki nemi shiri da ita da sannu zata fahinci ke ba tsintaciyar mage ba sai ta soki fiye da magen da aka haifar mata a gida.
Ummi tace shine kan mafita gwago don yanzu duk yadda za a fahintar da ita ta riga ta hau ba ta yarda damu ko kadan.
Gwago tace may ake ciki ne don shi ya kawo ni yau din don nasan baku shirya komai ba ga auren nan gashi kuma ba kananan mutane bane su.
Ummi tace wallahi gwago abinda muke shawara ke nan akai tun jiya da malam ya daura wanan aure don nasan ba komai zamu samu a bangaren shi ba.
Gwago tace karki yanke hukunci da sauri don baki san ajiyan shi ba nace humm gwago ai abar zancen baba kawai don yanzu baida yaushe ne ya fara fita kasuwa.
Nace akwai wasu kudi a hannu na barin dauko sai a kaima su mama asan shawaran da za a yi dasu na mike sai gwago tace dawo ki zauna zasu yanzu don na fada masu mu hadu nan ban san abin da ya tsayar dasu ba.
Sallaman su mukaji a tare suka shigo suka tsaya suna gaisawa da mama dake zaune a kofan ta tana raba abinci.
Suna shigowa suka fara gaisawa nima gaida dsu nayi da zuwa sukace amarya ke ce haka ba wani shiri da zai nuna farin ciki a gare ki?
Murmushi nayi nace kai haba mama tace ai gaskiya ne Safiya tun yanzu fa za a fara shirya ki don wanan auren ba irin wancan bane.
Tace to ai kune uwayen nata kuka tsaya nawa na fada maku mu hadu nan tun da safe amma sai yanzu kuka zo.
Yanzu dai ba wanan ba yanzu shafiu ke fada muna abin da bakar daga can tayi jiya kuma asirin ta ya tonu.
Gwago tace don Allah ku fita batun ta kuyi abinda ya kawo yanzu don ba isasshe lokaci ake dashi don tace yace a sati biyi yake son ta tare gidan shi.
Suna hada bakin wurin fadin sati biyu fa ?
Yo mai za a tsaya jira kuma aure ya dauro ba sai ta tare gidan ta ba yanzu duk wani abinda za ayi ai aladane kawai don wajibi ya auku ko tunda an daura aure may ya rage kuma ?
To yanzu gwago maye abin yi tace yanzu take fada muna akwai kudi a wirin ta sai a san abin yi nace ta bari har ku iso ne muga kudin sai a san yadda za a kasafa su.
Mikewa nayi na shiga daki tare da kirgo kudi dubu dari uku na kawo masu na mika ma mama Jummai don itace babba a cikin su.
Tana kallon kudin tace ai ina ga a dai tallakance wanan din zai isa ko sun kai dari biyu ai nake gani nace dari uku ne nan tace tirkasa.
Ta juya gun su ummi tana cewa may ye abin yi yanzu ga dai kudi sun samu gwago ta katse su da fadin akwai raguna na sai a kama biyu ku hada a laurar taku.
Nace gwago baki barin abinki tace ai don haka dama nake kiyon su yanzu ba sai ai lalura dasu ba sai dai zanso ku soya masu shi ku jefa a gara kun dai ga gidan masu shi zaku kai kayan.
Zan so ace kun tsaya kunyi abinda zai cika ido yadda ba za a raina maku ba.
Mama Suwaiba tace mu dai yi iya karfin mu amma ina zamu ita dasu nace mama may zai hana ku kira mama na nan gidan kada a kebe ta zaifi ace anyi komai da ita.
Gwago tace yanzu abin da nake shirin fadi ke nan kika riga ni fada sai ummi tace gaskiya kan kiranta aka tura Aisha da ta make dakin tana sauraren mu akayi .
Bata dauki lokaci ba sai gata nan dai akai mata bayanin ta nisa tace da son samu ne kada muyi kayan abinci mu dai tsaya ga wanda za a rabawa yan uwa da abikan arziki don shine abi magana.
Alabashi gaba in ta haihu sai ai mata wanan ko yaya kuka gani ta dago kai tana kallon su ko wayace sharan ta yayi.
Na suka fara kitasta abinda zasu inda za a kai yin cicin din a birni can wajen kaunan miji mama jummai dake zaune a birni su kuma zasu yi sauran abubuwan a nan .
Kowa ya dauki part din abinda zai yi a cikin su inda aka bar wa mama da ummi yin suyan kaji da ake so cika roba guda dashi.
Tun wanan ranan basu zauna ba kowa da abin da yakeyi don kar a girshe shi muna waya dashi ko wani rana yana kara kwantar min da hankali.
Faiza ne ke fada min cewa su anty uwa sun koma abuja a fusace wai Nafisa tana ta kuka tana fadin ba zata yarda ba.
Ita sai ta auri uncle ko ta halin kaka wai da kyat ta yarda ta bisu ta kare da cewa wai yanzu ashe an daura auren ku da uncle baki fada mu na ba sai a bakin mutane mukaji.
Nace wallahi Faiza nima ban san za a daura min aure ba a wanan lokacin kawai daga zuwa tambaya sai gashi ance daurin aure za ayi.
Tace ai dake da madam din mu ne yanzu don naji tana ta zage zage tana ta fada daga ke har uncle din wai kun munafunce ta.
Nayi murmushi kawai nace ba haka bane wallahi kowa baba bai fada wa zancen daurin auren nan ba sai da akazo yi aka sani wallahi ki yarda dani Faiza tace wallahi na yarda.
Tace yanzu yaushe ne tarewa kuma ?
Nace da ita babu rana Faiza don bamu tsaraba sai ya dawo zai saka rana tace aini abin yayi min dadi wallahi sai dai nasan yadda madam ta hau ba zata barmu mu zo wurin bukin ba.
Kin san may nace a a Faiza tace naji suna magana wai ai gidan ku ba abinda zasu kai tin anan zaiji kunya ita ko mutumiyar kullun tana daki tana kuka wai bata da lafiya.
Allah ya kyauta nace da ita ban yarda na furta wani kalma da zata kaini gaba ba don sanin halinta da nayi.
Mun gama wayan ta barni cike da tunane halin da muke ciki da anty don da ka gan ni na ramay babu walwala a tare da ni kamar wacce za ayiwa auren dole na koma.
Nasan dawowan shi Nigeria sai da ya kwana biyu ya wuce bauchi wurin mahaifiyar shi don kiran gagawa da tayi mashi akan maganan mu.
Ya iso sai dai mutane basu bari ya samu kebewa da ita ba sai da dare suka samu ganawa da mahaifiyar tashi.
Yana zaune kasa tana saman kujera ta kafa mudubin ido a fuskan ta da ke taimaka mata vurin gani.
Shiru dakin yayi kafin tace babana wata irin mace ka dauko muna don ban ji dadin labarin da ya kawo min ba.
Ko da yake mutanen duk da bamasu karfi bane amma sun san mutuncin kan su a yadda mahaifin yarinyar bai karbi sadaki mai yawa ba kuma da irin taron da sukai ma wayanda na tura daga nan.
Sun yaba kwarai da mutuncin da aka nuna masu a gidan sai da abin damuwa wanan labarin da Nafiu yazo min dashi shine banji dadin shi ba.
Nafi son kayi bincike mai karfi kafin yarinyar nan ta tare don ni ban kita ba don kaine mai zama da ita amma tunda kananan magana ya fara fitowa daga gare su sai a tsaya a bincika a hankali kada azo ai abu a cikin duhu.
Ban son ka kara auren dana sani kamar yadda kayi a baya auren da baida amfani a gare mu sai barnan suna.
Shiru yayi kafin ya dago kai yace hajiya akwai abin da nake boye maki da dadewa wanda baki sani ba har yau.
Gyara zaman tabarau ta tati dakyau ta dago kai tana sauraren shi tare da fadin baba na maye kake boye min wanda ban sani akan ka.
Ashe akwai abinda zaka iya boye min wanda ya shafi rayuwanka yace hajiya kiyi hakkuri don Allah fada maki wanan zancen tashin hankali ne a gare ki.
Nan dai ya fara bata labari tun auren shi da Samira matar shi ta farkko sai innalillahi kawai take furtawa har yakai yadda anty ta hada ni dashi dakuma yanzu da take shirin ruguza auren namu.
Innalillahi take ambata tace yanzu shi Nuhu da matar shi sun san maganan ga suka iya boye maka sirin ka ta yadda ko ni da na haife ka ban sani ba.
To amma ita maimuna may zai sa tayi haka bayan ta hada alheri kuma ta bata rawanta da tsalle a karshe.
Yanzu na gamsu da kai sannan ita wanan yarinyar itane rufin asirin ka ga kowa ta yadda ba kowa zai san abinda kake ciki ba.
Allah ya albarkaci aure ya baku zuria mai albarka ya amsa da amin tare da mata godiya ta kara kwantar mashi da hankaki tayi tare da cewa tasan yadda zata kashe maganan daga bakin kowa.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , ,


🧕🏿5️⃣4️⃣🧕🏿



NOVEL DINA NA KUDI NE WANDA YA SAN BAI IYA RIKON AMANA TA FADA MIN IN BATA KUDIN TA , , ,


Shirye shiryen buki aketayi amma ni hankalina baya gare su cike yake da damuwa don ban san yadda zai kwashe da mahaifiyar shi ba.
Na kwanta zuwa dare naji kiran wayan shi ya shigo min a sanyayye na daga wayan gami da sallama a bakina.
Yace kin fara barci ne nace ina naga barci ban san hukuncin da baaba zata yanke a kaina ba kuma ma ai yanzu barci bai ga idona ba tunda nace aure nake so.
Dariya yayi sosai har yana lyalkyatawa yace fada min may zai hana ki barci don Allah ?
Na abubuwa da yawa mana Uncle yace kamar su mai nace wayan san iyaka sai dai ranan da na tare a gidan ka.
Don kullun cikin kawo kudi ayi kaza nake yace look nafa fada maki bana son tarkace daga ke sai boxes din ki za a kawo min na fada maki .
Nace naji uncle amma dai ai za ayi abinda zan ba yan yinin buki ko ?
Yace kai mata ho wanan kuma kina son ki sawa kan ki nauyi ne nace ki bari inzo in dauke ki daga ni sai ke sai gida na amma kin ki.
Nace wani gidan uncle yace gidana na Abuja mana ba anan zaki zauna ba ?
Nace haba uncle kai ka ga haka ya dace ga hajiya baaba da ranta da lafiyan ta a dauke akaini gidan ka na Abuja ?
Ai ka bata damarta na mahaifiya ta sa muna albarkan aure dariya yayi yace Safiya wanan halin ya kara sa ina son ki wallahi yanzun dai sai an kaiki bauchi ke nan wurin hajiya baaba ko ?
Nace a wani irin murya mai sanyi shiya yafi mutunci uncle yace to shike nan hakan yayi kyau zan fada mata su shirya nan za a kawo ki direct idan an dauko ki.
Muka dan taba hira yana fada min yadda suka kwashe da mahaifiyar tashi nace uncle dama bata san halin da kake ciki ba duk wanan dadewan yace bata sani ba.
Kuma ko yanzu na fada mata ne don kada daga baya tazo ta zargeki ga abinda ba laifin ki ba ya kawar da zancen da fadin zan turo maki da sako gobe sai ki kara kiyi hidimar bukin dashi yan uwa na zasu zo ranan alhamis da kayan lefen ki wanda naso ace madam ne zata zo dashi.
Amma wanan matsalar yasa baaba tace daga wurin ta za a kawo komai yadda ya kamata nace Allah ya kaimu lafiya amma ni da an bar lefen don baaba ta riga ta aiko min da akwati biyu yace ta fada min wanan ai mun gani muna so ta hada maki wanan kuma ni na hado maki shiya kaini Dubai dama.
Mukayi sallama ina mai kara yi mashi godiya ya kashe wayan na sauke ajiyan zuciya.
Ina mai ci gaba da tinanen wanan baiwa da ubangiji yai min amma ma kuma baiwan sai yazo min a bahaggon rayuwa.
Washe gari ya shiga gaida mahaifiyar tashi nan yake fada mata yadda mukayi akan nafi son in tare anan bauchi don ta sa muna albarka.
Murmushin nuna jin dadi tayi tace mashi shiya har kullun bani dana sani da zaben ka don nasan bakayin abinda za a yi da an sani cikin sa.
Ko wanan auren kaddaran na Samira da kayi don yan uwanka ne da sukai hadin ba bincike yanzu gashi an bar mu ciki.
Daren jiya banyi barci mai dadi ba a rayuwa na amma da nai tunane sai naga bawa bai wuce kaddaran sa mutuwa kuma tana iya riskuwan bawa a ko wani lokaci.
Don haka yanzu kafin ka tafi sai a fara shiye shirye tunda buki ya dawo wurin mu don da ina dauka acan za a yi komai.
Bai baro bauchi ba sai da suka gama shirin komai da za ayi a nan ya san nan ya baro garin ina kwance naji waya alaman sako ya shigo min ina dubawa kudine wanda sai da ya sani kaduwa.
Na duba na kara dubawa naga milayan guda chur ya turo min tare da sakon da ya biyo baya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login