Showing 96001 words to 99000 words out of 269010 words

Chapter 33 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13315

wallahi.
Ta sake cewa yau dai kaki taba abincin gidan na mu ya dan yi murmushi yace mata yau bana jin yunwa ne shiyasa.
Ya fice a sanyayye tabishi da kallo tausaya mashi daidai lokacin Fati tashigo get din gidan bai ko kalli inda take tana gaidashi ba yaja motar shi zuwa wurin da ake masa aiki.
Ta shi go da yar fara an ta a fuskan ta tana cewa ashe uncle yazo gidan sai dai kuma bai dade ba ya wuce kuma ?
Anty ta kalle ta fuska daure tace ke Fati ki saurare ni dakyau kiji may zan fada maki naga kina wani rawan kai tun zuwan Sulaima.
To ki kama kan ki don sulaiman ba ajinki bane ya wauce sanin ki ki tsaya a matsayin ki idan kina son mu rabu lafiya dake ke ina ma kika ga haka zai yuyu dube ki ki dubeshi ina zaki hada kan ki dashi.
Kuma ni ina auren dan uwan shi ina kika taba ganin an yi hakan sai ta turi baki gaba tana cewa damay yafini kuma ni ba mace bane halan ?
Ta shige tana kumkumi ta bita da harara har ta bace mata dagani tana sauke ajiyan zuciya ina fitowa daga daki na.
Nace anty ashe kina zaune nan ban sani ba dana fito na taya ki hira ai tun dazu.
Ta kara sauke ajiyan zuciya tace ai bani kadai bane nida uncle din yara ne yanzu ya fita daga nan .
Nace ayya aiko da na ganshi kullun muna samun sabani sai ya tafi nake fitowa har yau ban sanshi ba .
Tace aikuwa da kinga shi yaro mai taken zamani don Sulaiman abin son a san shine bari rana da ya shigo zan kiraki ku gaisa don yace zai tafi gida ya duba su ya dade rabon shi da gida.
Nace Allah sarki dan uwanki ne anty ?
Tace a a dan uwan mai gidan ne iyayyen su guda sai dai tasu tazo daya da manjor ne kawai sai muke dasawa da shi sosai.
Bai iya boye min komai nasa nima haka shiyasa nake son shi da komai nasa don shawaran shi baya wuce ni shima.
Nan muka zauna tana ta bani labari da irin arzikin da yan gidan su daddy ke dashi da sauran su har Faiza tafito ta samay mu anan itama ta zauna.
Fati bata fito ba sai da yamma lis ta fito tana jan kamshi Faiza ne tace yau may ke faruwa da yar mulki ne naga tun dazun take fushi a gidan ?
Anty ta ja tsaki tace rabu da mara wayau kawai bata san abinda take yi bane shiya sa sai gata ta fito a fusace tana fada wai waya shiga dakin ta da batanan ya dauko mata hand dryer din ta.
Faiza tace itace don Safiya ta karbi nawa kuma bata bude kofa ba lokacin shiya sa na dauko naki din.
Nan ko ta shiga fada ta inda take shiga ba nan take fita ba sai da anty ta dakatar da ita da cewa.
Ke Fati kin ishe ni wallahi haba ke kika saye shi ko ni da zaki saka mutane a gaba kina masu fada haifan su kikayi komay ?
Don haka ki shirya kayan ki gida zan maida ke nagaji wallahi duk naji abinda kikewa Safiya tun zuwan ta garin nan ido kawai nasa maki inga gudun ki.
Tun farko ina sai da na hada ku nai maku nasiha amma kika shure magana kina yadda ran ki yaso dasu a gidan nan.
Wai halan kikai Faiza matsayi ne agidan da zaki dinga hura ma mutane hanci yadda kike so ya zama dole in mai dake gida don ban iya zama da wanan iskacin naki haka .
Jin anty na ambato gida yasa ta sausauta maganan ta ita ko faiza kai ya fasu jin ance tafi kowa matsayi a cikin mu sai wani budawa take yi.
Nan dai anty ta kafe akan lallai ta shirya ta maida ta gida sai na shiga ba anty hakkuri tana ta faman fada da ita.
Ds kyat na samu ta hakkura da zance sai dai tace wallahi ta shiga hankali ta don ta gaji da ita a gidan
Tun wanan lokacin ta shiga hankalin ta da kowa dama ba mai shiga tsabgan ta cikin mu don haka bamu damu da ita ba.
Da anty zata dawo ranan sai ta sayo min nawa in huta da aron nasu da nakeyi tare da yan sayayyen kayan makeup dina.
Zama na a gidan yasa yanzu zaka ga komai a gidan tsab don kai aiki iyakan ta girki nice ke tsabatace gida kafin duk su tashi na gama komai har in kama mata yin girkin kuma.
Wanan abinda nakeyi shiya na kara shiga ran anty sosai tana tausaya ma halin da nake ciki takan kaini amsan magani secretly ba tare da kowa ya sani ba a gidan.
Kuma ban taba jin wani ko ganin an kyan kyankyamayni ba a gidan zama suke dani ba wani nuna rashin yarda dani gashi bata rage ni da komai ba na fannin rayuwa kuma.
Sati uku da maganan mu ina daki kwance yan biyu ta tashigo da gudu tace wai inji mummy su inzo .
Na dauki dan kwalina dake saman gado nai rolling din kaina dashi tare da dan gyara fuskana kartai min kwankwami rashin gyara.
Na fito su biyu na samu a fali sai dai may shi ya hada baya ban iya ganin fuskan shi a lokacin.
Gasu yan biyu sun na wasa da hannuwan shi sai dai mai shi fari ne soll da ganin shi yan biyu tana ta jan yatsun hannun shi na iso wurin tace yauwa Safiya ga uncle yau a gidan.
Sai ya juyo da sauri yana kallon wace akace ma safiya din don bai taba jin sunan a gidan ba sai yanzu.
Juyo wan shi mukai ido biyu dashi sai da gabana ya fadi don ban taba ganin namiji hadade irin shi ba nan dai na gaisheshi ciki kunya kunya.
Ya amsa min da lafiya lau kawai ya juya yaci gaba da wasa da yaran dake damun shi nace anty gani.
Tace shike nan dama kiran ki nayi ku gaisa da uncle din yara da baki sani ba sai nai murmushi na juya na barsu wurin daya fahinci na wuce.
Sai yace ita kuma wanan din wacece ita anan gidan take itama da zama ?
Tace budurwan da nai maka kamay ke nan yace kai haba madam kikan fara maganan ki don ki koreni ko.
Tace daga maganan mace zan koreka wai ko sai mun kaika mararaba mun ma wanka ne zaka daina tsaron mata.
Yace kai don Allah bari wanan ma ta gama secondry ne tace tun yau she ta kare Allah da gaske nake yi inda kana ciki sai in kama ma kawai musha buki.
Take ya daure fuskan shi alaman ba wasa a tare da shi tace kai ke nan da an maganan aure sai ka bata rai may kake nufi ne wai ?
Bai bata amsa ba sai ci gaba da yayi da hira da yaran dake gaban shi sai da ta kawo mai zancen aikin da akeyi mai ta samu ya sake fuskan shi.
Ni ko tunda na juya na wuce ina ta mamakin haduwan wanan mutumin da anty tace dan uwan daddy ne mijin ta kuma wai may kudi naji anty na cewa.
Na gaji da tunane na watsar da zancen na kama sha anin gabana daya damay ni kwai sai ga fati ta shigo dakina abinda ban taba gani ba tun zuwa na gidan.
Tana shigowa ta fada saman gadon dakin nawa da yasha gyara sai kamshi ke tashi a dakin tako ina na dakin.
Safiya kin san kowa yau ina cikin farin ciki ga uncle can a falo yazo tun dazun yazo yana falo na dade dakina ina leken shi ta fada saman gadon tana wani irin dariya.
Nikan kallon mamaki kawai nake binta dashi don abin ya daure mun kai sosai tace wai kin san wani abune safiya na gyara zama tare da cewa aa.
Tace wallahi anty tana kawo min kubsawa don sam bata son zance da guy din nan ni kuwa duk yadda zanyi in ga yaso ni sai nayi kin san abinka da yan uba.
Sai nai saurin kallon ta don jin kalamin ta gamay da anty duk wanan halarcin da take mata amma wai tana kiranta da yan uba.
Ta kara lumshe ido tana ce min guy din ya hadu ne sai ma in kin ganshi wallahi yanzu tashi zan yi in dake kawai in je mu gaisa dashi ko bata so ni ban damu in dai bukatana zai biya.
Nace haka za a yi kije ku gaisa ko ki samu shiga ai ba a bori da sanyin gwiwa tace ai shi na gani wallahi.
Ta mike tana wani juye juye tace yaya kika gani na hadu ko da gyara nace cikin daga kai komai tsab wallahi.
Ta fice daga dakin na bita da kallon mamaki nace oho zamani ina zaki damu mata cusa kai ga maza haka ?
Acan falo tun da anty taga ta tun karo wurin su tace kin ga Fati kira min safiya ta hada ma uncle fruit salad wai abinda yake so ke nan.
Tace anty bagani ba zan iya hada mashi ai tace don Allah ki raba ni da shirmay ki ranan da ta hada masu bacewa kikayi ke baki iyaba.
Sai tace ai naga yadda ta hada din kin ga kira min Safiya nace don Allah ban son shirmay ki hakan nan.
Ta wuce tana mai jin haushi yar uwar nata data kwabsa mata a gaban shi sai gata dakina tana cika tana batsewa tace tana kiran ki .
Niko ina cewa yaya anyi nasara dai ko kin samu magana dashi tace ina yar bakin cikin zata bari ai komawa zanyi ko bata so.
Nace antyn ne yar bakin ciki tace to in ba bakin ciki ba ko zama bata bari nayi ba ta koreni da karfi da yaji ban san abinda take nufi da hakan ba.
Mikewa nayi zuwa amsa kiran anty na je da sallama na ce anty ance kina kirana tace eh kin ga don Allah wanan gwauron zaki hada ma fruit salad wai yake son sha yau.
Ban tsaya ba na juya zuwa kitchen din ya dan kalle ni ta witsiyar ido a ranshi yace ba laifi yarinyan sai dai akwai shamaki a tsakanin mu.
Ban dauki wani lokaci ba wurin hadawa don akwai komai na bukata kankara na jefa yadda zai yi saurin yin sanyi bayan na hada din.
Na nufo dashi nan na tsikayi Fati zaune tare da su tana wani kwarkwasa yar nata nata hararan ta bata damu ba nazo gaban shi na aje yace dani thanks kawai na juya zan wuce..
Anty tace dan tsaya ki zuba mashi nima ki zubo min karya shanye ba sha ba nan na juya na sake dukawa gaban shi ina diban mata kamshin turaren madina dana shafa ya dokan hancin shi sai lumshe ido yake yi cikin sytle.
Na diba na bata na dago muka hada ido da Fati sai naga tana harara na ni dai na wuce abina ban kara juyowa ba.
Sai gata dakin ban bari tayi magana ba nace kai amma Fati kunyi balain dacewa da wanan mutumin gaskiya.
Da da fushi ta shigo amma jin abinda nace yasa ta washe baki tana fadin gaski Safiya nace kwarai kuwa kiyi kokari anty tafahinci ki .
Tace haka za ayi ai don haka sai na zauna ki fada min ta inda zamu bullo mata nace niwa aini yar kauye ce ban san komai ba wallahi..
Da yamma muna falo gaba dayan mu Faiza ke cewa wai ni yaushe Yaya sulaiman ya wuce dazu ne ?
Kafin anty ta bada amsa Fati tai carab tace ai kedai yau ya dade gidan nan sai anty ta balla mata harara tace ke aka tambaya ko kin san wucewar shine.
Wai ke may yasa baki da hankali ne Fati sai tai wani turo baki kamar karamar yarinya nace anty kin sani ko za ayi yar gida ne.
Tai saurin cewa haba Safiya don Allah kibar wanan zance ki kyale ta da shirmay ta can so take mukai ga yadda ba a so.
Ita ke haukan ta nan shi yana da wace zai aura ko ina ma zai kai ki haka kazama dake sai tai fushi ta daga wurin Faiza tace da gaske anty ya samu mata.
Tace insha Allahu muna fatan hakan amma sai komai ya kankama zamu je ayi magana don ba yar kasan nan bace yace.
Nan ta hau murna don jin dan uwan nata ya samu wace zai aura ashe maganan ya fada kunnen Fati dake wuce wa.
Sai da na dawo daki ta samay ni da maganan nace tayi kokarin cusa kan ta dai in Allah yayi ai ba wanda ya isa ya hana ta sauke ajiyan zuciya tace shiyasa nake son ki wallahi don fadin gaskiya.
Ni dai na samu ta fita na rufe kofa na asuba ta gari sai kuma in Allah ya kaimu lafiya muji da wace zata zo min kuma a gidan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , , ,


🧕🏿3️⃣3️⃣🧕🏿


YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BAN YAFE BA IDAN KON FITAR MIN DA NOVEL UBANGIJI YA SAKA MIN A KANKI CIKIN GAGAWA.


Wanan abin yasa yanzun muke shiri da Fati don ko yaushe tana dakina muna hira abu daya kullun na yadda zata shawo kan shine a gidan.
Zata shigo ta fadi nidai ina ta mata dariya indan ta gaji ta fice ta koma dakin ta, sai dai abu daya ne wanda ban yarda da shi ba.
Irin yadda take kushe maganan anty ko take sukan ta da munana kalamai marasa dadin saurare.
Don haka sai na dakatar da ita nace idan zamuyi hiran mu mubar saka sunan kowa mudai nemi mafita akan yadda zamu fito mazancen ta da sulaiman din.
Taso tai hushi alokacin amma sai tai tunanen ba ida take kai maganan ta ba tare da wani yaji ba sai gurina, sai gashi ta dawo da kanta.
Ina kwance daki sai gata ta fado min daki tana dariyan jin dadi nace halan mutumin ya shigo ne.
Tai wani far da idanuwa tace dani bai shigo ba tukun amma naji mijin anty na waya dashi wai su hadu karfe hudu nan gidan.
Nan dai mukai shawaran abinda ya dace tayi tabar dakin tana ta murna nikan fitan ta dakin na kwanta abina don ina fashin yin sallah a lokacin ban son shiga mutane.

Kamar yadda Fati ta fada hakan ne yazo gidan bayan hudu ya dan gwauta kadan yana falo da anty daya sama a falon ita da yaran ta.
Tun shigowan shi take faman sake murmushi a fuskanta kamar yadda ta saba indan sun hadu.
Ya zauna suna gaisawa da ita yace komao lafiya ko ta amsa mai da lafiya kalau muke, tace yaya aiki kuma?, ya lumshe idon shi yana cire hular kan shi .
Yace aiki muna kai wallahi yai ajiyam zuciya yace yanzu ma mijin ki ne ya kirani koda yake dama yau ina da niyar shigowa gidan naku.
Sai ga mijinki ya kirani kuma tace ka kwana biyu baka shigo nan din bane ya sake cewa wallahi yau nake da niyar shigowa don ina son in baki wani aiki ne.
Ta nisa tare dacewa tau fa, ina jinka rankaya dade,
See you nine ranka ya dade kuma ni dai kisa a hada min wanan abin don yau dashi zan tafi don ina son shi sosai wallahi.
Mikewa tayi don yaran sun shige don bude tsaraban da ya shigo masu dashi da zaizo don haka babu yaro kusa sai anty taje kirana da kanta.
Tana wucewa Fati ta fito acikin wani irin kwaliya tana kashe ido wai tana mai sannu da zuwa takai zaune a dayan kujeran falon.
Niko ina daki na kwanta wuri daya na dunkule wani iri kamar maijin sanyi idan ka ga yadda na kwanta.
Tabani, tayi tana kiran sunana a hankali, inda na bude ido na sauke a fauskanta ina mai kallonta cikin magagin barci sai naji ta tambaye ni dacewa lafiya kike kuwa kike ta barci haka ?
Na murza idona tare da cemata anty barci ne kawai ya dauke ni tun dazun tace to tashi don Allah aiki zan saka ki don wanan bakin batauren ya shigo wai fruit salad yake son aimashi.
Na sake murza idona nace to anty barin tashi yanzu zan fito ta mike don barin dakin nawa har takai kofa nace ina mike wa Fati na nan ne muyi tare.
Tace Fati ko mashiririciya may zata iya wanan don Allah fito ki hada mashi tunda har yai magana kada ya tafi ba a hada mai ba kuma.
Hankalin shi naga wayan shi baiko san tana zaune a wurin ba ita kuma sai wani gyare gyare take yi daga zaune kamar wacce ake tsunkulan ta.
Anty ne ta iso gurin tun da ta ganta ta daure fuskan ta har tazo ta zauna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login