Showing 138001 words to 141000 words out of 269010 words
Samira ni duniya yaya ya gama min komai Allah dai yabar zumunci ya raya min takwara na ta famnin addinin musulunci yasa mata albarka sukace amin.
Nan muka zauna muna hira yake ce min sai yaje gida ya samu baba ya samu lafiya sosai sai dai su ummi ba kowa a gidan anata gyare gyaren gida.
Na nisa nace bari yaya nan na fara bashi labarin yadda abin ya faru da irin taimakon da yake min shi da uwar dakina.
Sai da ya gama saurare na yace Alhamdullahi Allah maji rokon bawan sa Allah ya amsa min addua na kullun ina rokon Allah akan kada rayuwan ki ya kare hakana baki more ma rayuwa ba safiya.
Don ina ganin yadda rayuwan masu wanan matsalar yake karewa a lalace saboda rashin gata da samun kulawa da basuyi.
Nacs haka abin Allah yake yaya sai dai muyi fatan dacewa da rahaman ubangijin mu yanzu.
Amma yaya inda son samu ne asamu wanda zaiyi bincike kwakwara akan Sulaiman din don kada ai abu cikin duhu a dawo ana da an sani kuma irin na farko.
Ya nisa yace insha Allahu kuwa zanyi kuma da yardan Allah sai Alheri don yadda yake kulakin nan akwai alaman nasara ga abin.
Don da akwai matsala da tun yanzu zaki dan fahinci wani abu daga gare shi sai dai zaki iya tara matsololin da ake fadi nasa ki auna ki gani .
Amma dai duk da haka zanyi kokari in bincike a kan shi don wani lokaci yin binciken yana da kyau.
Na fara hamma yace naje na kwanta mu hadu da safe sai lokacin nace dashi yanzu wani sana a yakeyi ne ?
Jeki ki huta da safe mayi magana naga kin fara hamma ni yanzu fita zanyi ya kwala ma matarshi kira tazo ta kaini daki.
Naga ta nufi dakin su dani nace ai da kun barni in kwanta a falo ma nan ya yi min yace haba dai ai kinzo taya ta aiki ne don haka ni na bar ki da ita ke nan.
Yai muna sallama cewa zai fita ya dawo na mike zuwa dakin inda na samu gadon dakin yasha gyara dakin sai kamshi yakeyi .
Na yi shirin kwanciya dukkan mu a saman gado daya muka kwanta muka sa baby a tsakiyan mu asuba ta gari yan uwa.
Idan zaki fitar min da novel na barki da raddin ubangijin mu je ki tayi tunda baki san hakkin amana ba zaki fada ranan da baki baya magana sai hali.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,
🧕🏿4️⃣7️⃣🧕🏿
Ni safiya ace mutum bai tsoron Allah shi dole ne karatun nan ance ba a yafe ba an hada ki/ka da Allah an hada ku da darajan annabi amma kuna wasa dashi ku sani fa hada mutum da Allah ba karamar kalma bace akwai ranan haduwa dashi ranan nadama ranan da baka da abin bayar sai ladan da ka tara ma kan ka.
Mutuna ko yanzu ko anjima koyau ko gobe ko ko ko ko zamu koma ga Allah koda ciwo ko babu ciwo may zamu fada wa Allah.
Dabara ya rage ga mai shiga rami shi kadai ni dai tun da asuba na mike batare da samira ta sani ba nayiwa gidan ta kwal ga ruwan zafi da na sa masu na wanka ya ya tafasa na sauke na fara hada mata abin karyawa.
Sai da naje daukan baby dake barci a gefen tane ta bude idanun ta tana fadin subbahanallahi gari ya waye ne ?
Murmushi nayi nace madam ki tashi ruwan zafin ki na jiran ki a bayi ban saurara mata ba na fara cirewa baby kayan jikin ta na nufi bayin da ita inda maga kayan wankan ta aje a gefe.
Wanka nayi mata na gasa mata jiki dama na iya tun ina gida idan ummina ta haihu nakan taimaka mata da wankan yara.
Na fito na fara shirya baby sai lokacin Samira ta samu ta mike zuwa wanka tana cewa yau wata rana zamuyi wanka da safe haka yadda ya dace.
Nikan naji dadin ziwan nan naki Safiya wannan kokari haka ta mike take bin dakin da kallo tace wai ko kin yi barci safiya wanan irin aikin haka ?
Kafin ta fito na saka wa yarinyar kaya cikin kayan da nazo mata dasu uwar ta fito wanka tana kallon mu da sha a wa tare da fadin aa lalai takwara tazo wanan kaya ai da ki bari sai ranan suna ki saka mata.
Murmushi nayi kawai na goya yarinyar na na fita daga dakin sai gani na dawo da cup cike da shayi mai kauri dana hado mata.
Na aje a gefen ta dago kai tayi ta kalle ni nace madam sai a sakai a shanye kafin ya huce nace za a daukan maki kaya ne ki saka ?
Tace gaskiya Safiya zaki shagwaba ni da yawa ki wuce ki barni da kewan ki nace kada ki damu madam dama shi nazo yi yanzu aiki na ne nakeyi.
Batai sanya ba ta kafa kai ta shanye shayin duka sai ga zufa ya karyo mata nan ta mike ta dauko kayanta tana sawa.
Na fito falo naji ana bude karamin dakin nan dake rufe ashe yaya ne anan ya shige ya kwana na juyo don ganin ko waye mukayi tozali dashi.
Nace yaya barka da kwana yace an tashi lafiya Safiya nace Alhamdu lillahi yaya yace yau takwaranki ne ta samu goyo haka ?
Gaskiya banji kukanta ba yau da safe don kullun itace ke tayar damu da safe da kukan ta nace yau tasan gwagon ta na gari batayi kuka ba tun da nai mata wanka takoma barci.
Yace kai har wanka ta samu yau da wuri haka nace gwago tazo fa yaya zanbar diyana takai wani lokaci bata gasa jikin ta ba.
Nan ya fara bin gidan da kallo yaga gyaran da ya sha yace keko kinyi barci kuwa nace may ka gani yaya yace wanan irin aiki haka tun da farar safiya haka ?
Nace shiya kawo ni may zan kwata wa inyi ga aikin madam a gaba na yanzu lokaci ne da take sin hutu a jikin ta don haka ta kwanta ta huta jikin ta ya watsake.
Na shige kitchen na barshi yana mamaki ya raya a ranshi da haka uwar shi ta rike zumuncin da mahaifina yaso su kulla da abin yazo da sauki.
Ya shiga daki nan ya samu samira tana ninke kayan da ta cire ta juyo tana kallon shi tace kaga aikin kanwaka ko sai yau na karkare yarda da abinda kake fadi nata.
Na shiga dakin na samay su suna magana nace yauwa bari ma in baku sakon ku tunda gaka a dakin nan na jawo akwatin kayan da nazo dashi zuwa gaban shi na juya wirin hand bag dina na ciro kudin da na ware mashi tun a gida na bashi.
Sai bina yake da kallo yana neman karin bayani nace yaya kana kallona mana yace ban fahinta bane safiya nace to kaya da na takwara nane da uwar ta gashinan akwati guda sai kudi kai kuma ka kara kai hidiman buki da su.
Tsaye yake dama zai shiga bayi sai naga ya kai zaune a wurin yayi shiru can ya dago kai yace Safiya duka wanan dawainiyar ani kika yi shi bayan zuwan da kikayi kuma ga wanan wahalar.
Ba wahala bane idan duk abinda nake dashi zanyi maka bazan taba yin da na sani ba yaya kai kaja in maka hakan da nayi.
Samira kan kallo na take da mamaki da kyat ta samu bakin magana tace wai safiya kin wanke ni ga bakin jamma a kin gama muna komai a duniyan nan.
Kin san yayan ki aikin company yake yi gashi wata uku ba a biya su jiya jiyan nan muka gama magana dashi na yaya zaiyi ko zamu daga sunan nan har zuwa gaba.
Nayi saurin cewa a uzubillahi a daga suna kuma yaya Allah ya rufa muna asiri ashe gwama da na daure nazo don da anty ta so hanani zuwa na nace nace sai nazo.
Tace Allah ne ya kawo ki yar uwa ta fara jawo kayan tana bude zip din jakkan don na karshen ne babban duka duka nazo kasu dashi.
Shiko yayi mutuwar zaune ya kasa fadin komai har lokacin tana budewa ta sake karamin ihu da fadin wai Safiya ?
Shago ke nan ta fara budan kayan tana azawa a saman gado karshe rufe akwatin tayi tai tagumi kawai sai can ta nisa tace dear ka ga ikon Allah.
Sai lokacin ya nisa a sanyaye yace na gani samira ban san may zance bane kawai imani da tsoron Allah sun cika min zuciya samira.
Kawar da zancen nayi da fadin ni kaga malam kai wanka ka shirya kazo ka karya in ka gama ka fita ka sayo muna abinci azo a aje a gidan na ciro kudi ina mika mai.
Ido ya zaro yace na may ye kuma wannan kudin nace abinci zaka sayo mana dashi wanan ba na hidimar suna na baka kayi ba sai naji yace haba kai safiya haba dai.
Tare shi nayi da fadin ka gode ma Allah adduan ku gareni ya karbu ga ubangiji shi ya wadatani da wanan niimar idan ban gode nima na na rama maku ba may zanyi da kudi.
Kudine ina samu alhamdullahi don sulaiman yana wadatar dani dasu kuma yana fada min in yiwa yan uwana alheri daga niimar da Allah ya wadatar dani.
Yace Allahu akbar haka abun Allah yake safiya shiya sa idan kaga ubangiji ya yi ikon shi akan mutum kai dai kabishi da addua don baka san hikimar ubangiji ba a kansa.
Abinda nai maki a baya har ga Allah nayi maki ne a matsayin ki na yar uwata ta jini da kuma matar yayana da hadi na musulunci banyi don zaton wata rana zaki zama wani abu har ki rama min ba.
Nace na sani yaya nima kuma ba zan taba iya rama maka abunda kai min ba har abada duk wanda yai maka abu a lokacin da kake bukatan taimako a kan shi ai baka da kamar mai shi a duniya ba don kai ba da yanzu na wullakanta.
Yai saurin cewa Allah bai yoki wullakantata ba dama safiya ki godewa niimar da Allah yai maki tun farko tunda kin samu kiyi karatun boko.
Nan dai mukai ta hira dasu har ya gaji ya mike zuwa wanka yafito ya karya ya fice daga gidan baby Safiya ta tashi na kaita wurin uwarta na dawo na ci gaba da aiki na.
Tuwo na tuka mata na Semon da na gani a kitchen din da miyar yauki ina gamawa yaya ya dawo gidan da kaya niki niki tare da abokin shi.
Wai ya kirashi yazo yaga abinda na kawo masu abinci na gabatar masu bayan sun gama gani yaya yace safiya sai kina sa ina ganin gidan yau kamar ba nawa bane.
Muna tsaka ga magana Samira ta fito daki da wayana a hannu tana mika min ana kirana a lokacin.
Na karba naga Sulaiman ne da sallama na koma gefe daya ina amsa wayan yace gida yai maki dadi kin manta da kowa ko ?
Murmushi nayi nace yallabai an tashi lafiya yaya aiki yace lafiya kalau watau ke dai baki kiran mutum ko nace tsoro nakeji kada in kira ka kana cikin uzuri.
Yace don gani agogo sarkin aiki sai ba zan tsaya na saurari kiran mata na ba ko ?
Nace tuba nakeyi katse shi nayi da fadin ga yaya na ku gaisa yace af yana kusane nace yana nan yanzu ya shigo namika ma yaya Saadu wayan.
Sun gaisa yake ma yaya barka da samun karu sai yaya yace Allah ya mayar gare ku kuma da kunyi aure a sama mana tagwaye.
Murmushi yayi kawai yaya yake mashi godiya a bisa ga kokarin da yayi masu yace na komai ai anzama daya yanzu.
Yake tambayan yaya din wani aiki yake yi sai yace mashi a wani company yake aiki yanzu kuma company tai sanyi sai dai dan buga buga da suke yi sunyi hira sosai kafin yaya ya bani wayan mu ci gaba da magana dashi har yake tambayana da yaushe ne zan dawo ?
Nace jiya fa nazo har ake batun dawowa na yanzu sai nayi a kalla wata daya ko biyu kafin in dawo sai takwara na tayi kwari zan dawo.
Yace kina hauka ne nifa in badon madam ta fada min yadda kuke dashi ba kuma yanzu a wayan da mukayi na fahinci mutumin kwarai ne don gashi har yana min fatan samun tagwaye da auren mu.
Da hankalina bai kwata da zuwan ki garin nan ba sam nace sace ni za a yi komay ?
Yace yana da wuya ne nace ni ko kofan daki ban taka ba tun zuwa ina ciki kumshe ina za a gani har a dauke ni ?
Yace ki dai bi sannu don Allah ban son yawo please zan ma fada ma yaya don ya saka maki ido sai nace ai ka hutar da kan ka ni din kifin rijiya ce fita a guna sai ya kama dole nake fita.
Yace daya fi maki ashe ba zamu samu matsala ba ban son mace mai yawo a rayuwa na ko gadan.
Yace kin san may ?
Na ce aa yallabai yace yau yayan ki ya fama min wani ciwo a zuciyata sai nayi sauri cewa subbahanallahi.
Yace dakata mana kiji ai ba wani abu yace min ba illar cewar da yayi Allah ya bamu tagwaye da munyi aure.
Sai nayi murmushi yace ban taba jin ina son haihuwa ba nima sai yau daya fada min haka naji nima ina son in ga zuria na a duniya koda kuwa bazan rayu tare da su ba.
Nace balle zamu rayu tare dasu insha Allahu ai Allah shi ya fimu sanin daidai ga rayuwan mu ni dai mu bar wanan zancen ba yanzu ba tukun.
Yace saboda may ?
Ko ba kya son haihuwa ne ke nace wai kuwa kasan sunan yarinya Safiya ?
Kin kawar da zancen ke nan ko?
Safiya yaya yasa wa babyn namu nace wallahi ina zuwa yace ga takwara nan yayi min ya ce Allah ya raya muna ita a tafarkin addinin musulunci nace amin.
Yanzu yaushe zaki dawo lagos ba wasa nake yi ba fa ina son in sani ne ?
Nace kaida baka ko kasan kake tambayana yaushe zan dawo bafa a gari daya muke zaune ba balle kuma baka ma kasar baki daya.
Murmushi yayi yace ina son in san lokacin da zaki dawo idan yayi daidai da dawowa na Nigeria don ta lagos zan sauka.
Nace gaskiya ban sani ba tukun sai dai idan anyi suna naga yadda yanayin ya ke zan saka ranan dawowa na.
Munyi sallama dashi naci gaba da aikina na fito inda na samu su yaya sun gama cin abinci sun cinye duka sai kwano.
Na kwashe zuwa kitchen tare da kokarin dora girkin yamma don inyi in gama da wuri in huta ina aiki yan barka suna shigowa jefi jefi kamar yadda ake zaune a bariki.
Na gama na gyara wurin na koma ciki nayi wanka sai lokacin na samu zama da samira muka fara hira wanda hiran namu akan yanayin garin nasu take min da kuma bani tarihin ta.
Da yadda suka hadu da yaya saadu yan uwanta suka so su hana auren su wai ba a san asalin shi ba sai da kyat aka yarda ta aure shi don suna son junar su.
Nace ai yanzu aure babu inda bai kai mace gashi ban taba zuwa bauchi ba amma aure yana shirin kaini can din.
Tace wanda zaki aura dan bauchi ne shi nace mata dan bauchi ne tace a can yake zaune nace da ita a a .
Sai nayi dariya nace shi wanan ai baida takamaimai zurin zama dan kasuwa ne baya zama sosai sai dai ina ganin abuja zai aje ni amma dai ban sani ba dai.
Waya na jawo na kira anty don nasan yanzu ta dawo gida kira uku ta daga wayan tana fadin mutanen kalaba kun sauka lafiya yaya baby da maman ta.
Nace lafiya lau anty baby safiya tana gaida ke tace a a safiya aka sama yarinyar nace eh anty .
Tace ashe gaskiya kika matsa da zaki kin san abinda kuka kulla da yayan na ki nace wallahi anty ban san safiya ya samata ba sai da nazo naji.
Tace sai yaushe zamu ganki nace anty sai anyi suna zamu zauna da yaya saadu don yanzu bai samun zama a gida.
Tace yana da buki yaushe zai zauna gida kuma Allah yasa a watse lafiya ki gyayar min dashi don Allah ina mashi barka idan ya shigo .
Mun gama ina cewa ta gyayar min dasu yan biyu tace kin sa sun zo sun damay ni da tambayan ina kika je nayi murmushi nace nasan dama zasu tambaya ai.
wayan nake aje wa sai naji samira na fadin