Showing 99001 words to 102000 words out of 269010 words
ba walwala a fuskan ta.
Ta zauna tare da cewa ke kuma may kike anan din kije safiya na jiranki ki kama mata aiki.
Ta juya inda yake tana murmushi tace ina jinka sakon may kake magana akai ne wai ?
Ok dama account dinki nake so inyi amfani dashi in tura ma wani kudi miliyan hamsin mun sai injin ne a gurin sa .
Sai bayan sati biyu zaa fitar da kudin kinga kenan kema zaki iya samun wani abu daga yin hakan .
Tace sulaima ba matsala gayin hakan dagowa yayi yana mata dariya yace idan da matsala ai ba zan saki a ciki ba kedai ki bayar zaki gane abinda nake nufi.
Sai ya fara mata bayani a takwaice yace ashe ke matsoraciya ne kina tsoron kada a yaudare ki ko da irin haka yawancin mutane suke dagawa ina son inga account dinki yana motsine.
Nan ta shiga dariya don ta gane mafusa arlallan business yake son sakata ciki itama nan ta shiga yi mashi godiya daga mata hannu yayi yace haba madam ya idan ban maku ba suwa zan taimakawa ?
Yace sai dai gida da fili danake son saya a Abuja ta saki baki tana kallon shi don jin irin bayani da yake mata na gida da filin da yake so.
Ta sake cewa yanzu sulaiman ga gida ga fili kake shirin saya haka yace ai wanan ba komai bane sai tai wani irin shewa.
Tace iyyye tun yanzu ashe bari mu fara shirin buki ashe,
Dariya ya fara mata yace ba a sayen gida sai za ai aure ki rufa min asiri tun dawowan mu kudin nan nake son in sai gida da fili dasu, don ina yin wani aiki acan Abujan kuma dai ina ganin anan zan zauna don nafi son zama arewa da nan din.
Tace kayi dabara wallahi shawaran da nake ba daddy su kenan ko yaushe amma naga shi ra, ayin shi baison zama arewa sam.
Yace arewan ne babu dadin zama saboda mutane yan sa ido ga abin da bai shafe su ba sai suyi tama zargin banza ba gaira ba dalili kai kana neman nakan ka amma mutane idon su na kanka.
Mijin anty ne yashigo sai suka can za firan suka fara gaisawa dashi a daidai lokacin da na fito dauke da tiren a hannu na da na shiryo mashi.
Daddy din na fara gyarwa sai shi sai daddyn yace Safiya kike ko kina gidan nan ban gani ki sai nike tsamanin ko kin koma ne ban sani ba.
Murmushi nayi kawai sai anty ne ke cewa ita wanan ai in ka ganta waje su yan biyu ne suka fitar da ita dole zaman daki baya isan ta ko yaushe tana ciki kumshe.
Na gama jerawa zan wuce sai naji tace yauwa daddy shine nace ma mutumi na ko zai fada neman Safiya ne ya tsaya yana min kwana kwana.
Don Allah ba sai yar gida gida ba kawai ga mata har gida ya samu ba niba har mijin nata wani irin kallo yai mata nidai na wuce na barsu nan.
Ina ganin sun dade a wurin sai dai ban san maganan da sukeyi ba dagani dai maganan tana da muhinmanci a gare su.
Sai can naji fitan mazan daga gidan wanda ban debe tsamani sallah suka fita yi don lokaci da yayi yan biyu ne tazo take ce min mummy su na kiran su.
Ban tsaya ba na jawo dankwali na dora a kaina muka fito tare da yarinyar da tazo kirana din .
Tana zaune tana hada wasu takardu dake saman table din gaban ta tace kinga bai ko sami tafiya dashi ba yadda yace anan suka shanye abinsu shida major.
Ina kwasan kayan nake jin yadda anty ke ta faman yabon sulaiman din har take ce min wallahi safiya idan na samu nai wanan hadin a tsakanin ku kowa naki ya huta indai Sulaiman ne don bai da matse na tare dashi balle matar shi mutum ne mai sakin aljihun shi sosai wallahi.
Nidai abinda na saba nai mata watau murmushi sai dai a raina nace kardai anty ta zamo cikin masu rufe ido ayi cuta da ita kan abin duniya.
Ni dake da lalura har take zancen hadani da wani wanda baida matsala irin nawa ni yanzu aiko mai irin matsalata banda lokacin shi balle mai lafiya in cuta mai.
Na kwashe kayan zuwa kitchen da zan fito ma ban dawo wurin ta ba sai nai hanyan dakin na don zancen ta ba abin saurare bane a wurina.
********* ********* *********
A can gida kuwa ummi da kanina shafiu sun rike sanaar da na bar masu dakyau don takar ina gari ne don yaron bai da wasa ko kadan.
Saadatu inna ta kwaso ciki tun ba a gane ba har mutanen gidan mu suka gane ana ta kumbiya kumbiyar zubarwa sai dai Saadatun taki ba Inna hadin kai a zubar da cikin tace tsoro take ji.
A wani dare basu san baba yana waje yana alwala ba rikici kan azubar da cikin ya hada ta da inna a dakin su tun bai sauraren su har takai baba ya saka kunne ga maganan su.
Nan yaji abinda ya tayar mashi da hankali ya koma dakin shi sai kuka koda gari ya waye bai fito ba har wani lokaci.
Mama ne ta shiga dakin shi don taga may ya samay shi ta samay shi a cikin wani hali take hankalin ta ya tashi.
Zata tara mashi jamma a yace taje dai ta kira mai inna da su ummi da yaya Sani su zo.
Kowa ya taru suna jiran suji may zai fada masu sai can yace ma mama yanzu har da ke ashe za a hada kai a cuta min gidan nan.
Abu na faruwa haka amma an rasa wanda zai iya fada min sai da Allah ya sanar dani jiya da dare nan ya kwashe abin da yaji tsakanin inna da Saadatu yake fada masu.
Nan Inna ta kama fadan karya wai baidai ji da kyau ba mama ne tace haba Rakiya ko makaho ya lalube saadatu ai yasan halin da take ciki.
Don baki samu bane shiyasa muka kawo ido muka saka maku kawai amma batu duk ya gama bin gari ai.
Shiru wurin yayi sai yaya Sani ne ya kawar da shirun da cewa Inna kin kai ga yadda kike so ba abin da baki fada akan matsalan Safiya agidan nan.
Yanzu gashi ke Allah ya nuna maki nashi isharan sai ku san yadda zakuyi da ciki ai maza basu son ta da aure amma suna son ta da lalata.
Baba yai magana karo na biyu yace ba mai zubar da cikin nan a gidan nan don bani kunya biyu abarshi ta haifi abinta kuma duk wanda yace zai yi yunkurin zubar da cikin nan sharia ce zata raba mu dashi.
Nan ko inna ta aza hannu akai wai dama ta sani baba bai kaunar ta da diyan ta ai yafi son yaga sun lalace a gidan.
Yace yadai ji amma ba mai zubar mai da ciki a gidan shi sai inna tace zata kaita wurin yan uwanta a wani kauye a zubar can.
Amma ba yace bai yarda ba da kuyan lahira ya kwmmace yai na lahira don zunubin shi bai kona shiba na yar shi ba zai kona shi ba.
Haka dai aka watse baram baram a wurin inna ta shige dakin ta tana kuka diyan ta ma suka bita kukan sukeyi suma.
Gidan dai ya koma masu ba dadi na kira ummi da safe don inji lafiyan su take fada min halin da ake ciki nan ko na tausaya masu sosai.
Ummi tace min abinta ne Allah ya mayar mata ta gani ko tafiyan nan ba abinda bata fada ba wai karuwanci kika je yi acan.
Yanzu gashi taga abinta har a kuryan dakin ta ta koma mujiya a gidan don ko fitowa bata son yi tsakar gida.
Abin su na kishi a yadda ummi ke magana sam bata tausaya ma inna da Saadatun ba sai nine nace ummi wanan abin fa ba inna kadai ya shafa ba har daku dake da diya a gidan.
Don suna gidan mu ne zai lalace ga banza sai ai muna bugun dan kadanya gaba dayan mu ba wai za a ware ta ita kadai bane a zaga.
Sai naji tayi lau shi tace abin tane ai da ban haushi wallahi nace hakkuri za a yi a rungumi kaddara tun da baba yace ba a taba cikin.
Nan dai na bata shawara nakuma ga ta dauka san nan mukai sallama na kashe wayan cike da jimay abunda naji din.
Banyi niyan kiran saadatun a yanzu ba sai hankali ya kwanta zan kirata in kwantar mata da hankali don nasan bayin ta bane sherin uwar ta ne Allah yake nuna mata abin ta tun a duniya.
Sai dai kwana biyu na shiga damuwa sosai har anty ta fahinci haka ranan ta kirani dakin ta dama nasan kira dakin ta magana ne na muhinmanci.
Nan ta shiga tsoratani da nasihohi iri iri na ban tsoro don ita tana zaton halin da nake ciki ne nasa damuwa akan shi.
Nan dai nace mata anty bashine ke damuna ba yar uwata ce ta shiga wani hali abin yake damuna arai.
Ba abin da zan iya boye mata yanzu sai na kwashe komai dake faruwa na fada mata sai da ta bari na gama fada mata komai sai tace dani.
Lallai Safiya kina da imani a zuciyar ki in bashi ba matar da take son taga bayanki zaki dauki damuwar ta ki saka a ranki karfa ki jawa kan ki wani sabon lalura gaki yarinya karama dake.
Addua zakiyi mata kawai shiya fi nace anty ban taba jin tsanar diyan Inna araina ba don itace maisa suke min abinda sukeyi din tace ai shi nace kiwa yar uwar ki addua Allah ya rabata lafiya don aikin gama ya gama ko.
Nai mata godiya zan fita tacevin dakata ledan dake gefen ta ta miko min nasa hannu biyu na karba ina godiya tace bani zaki godewa Sulaiman ne ya saya maku.
Yaji ina maganan saya maki waya yace in bari zai kawo maku waya yau ina office sai gashi dasu guda uku shi na zaba maki wanan farin ga sauran nan zan ba su faiza nasu ita da fati .
Nan shiga mashi godiya da addua ita ko sai dariya ta min tace ai wanan karamin aikin shine wallahi .
Ranan haka muka kwana da murna tare da mu kowa yana farin cikin rike babban waya a cikin mu wanda kudin shi zai iya kai dari da hamsi.
Ranan ina kwace falo saman doguwar kujera kasalance sanyi da iskan dake fitowa daga naoran sanyayya falon na barazanan saukar min da barcin marance.
Sai ga Fati ta fito falon daga dakin ta take cewa dani wai dama dakina zata ashe ina nan zama tayi gap da kaina tace .
Dama wani abu nake son kin min Safiya sai na dago ina kallon ta don jin may take so na dashi.
Ta dan nisa take cewa ba wani abu bane nake so sai ki dauko min lamban mutumi na a wayan anty idan kin samu hali don bata yarda in dauki wayan ta sam.
Ke naga kuna dasawa da ita don jiya naga ta baki wai ki tura abubuwa a cikin wayan ki.
Ban kai ga bata amsa ba sai muka ji sallaman shi a kofan falo ya karasa shigowa yana rike da brief case din shi tare da su yan biyu a bayan shi ga katuwan leda da ya riko a dayan hannun shi wanda nasan tsaraban su yan biyu ne a ciki.
Daga inda nake kwance mukayi arba dashi ban riga na kai ga tashi zaune ba.
Har suka karaso inda nake yaran suka fado min suna cewa yau uncle ya kaisu yawo birch sun ga ruwa da kifi .
Na yun kura na tashi zaune ina kamo dan kwalin kaina da ya zamay min don a kwance nake.
Ita ko Fati duk ta rude da ganin shi zuciyar ta ya rinka saka mata tunane daban daban ba gaira ba dalili na samu na kai zaune ina mashi sannu da zuwa.
Bai dago ya kalle ni ba sai dai a ranshi yana nasawa tabbas yarinyar kyakyawa ce mai cike da kwarjini da kamala ya fadi a zuciyar shi.
Sai naji Fati cikin rudewa tana cewa gashi ko anty ta fita har yanzu bata dawo ba kamar bai son magana naji ya bata amsa da tana tafe sunyi waya da ita ai.
Mikewa nayi zuwa kicthen na hado mai abin sha da ruwa na kawo mashi sai ga anty ta dawo har fati ta zauna tana mashi zuba a gaban shi.
Nan mukai mata sannu da dawowa nikan na bar wurin sai yaran suka biyu ni suna bani labarin fitan su da uncle din.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
🧕🏿3️⃣4️⃣🧕🏿
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA A YAFE BA, , , ,
Anty ce ta shigo gida da karfe shidda na yammaci duk muna a falo zaune sannu da zuwa muke faman yima ta tana amsawa a gajiye takai saman kujara ta zauna tare da fadi wassh Allah yau na gaji sosai ga shi kuma gobe zan bi hanya da safe.
Gaba dayan mu maida mata hankali mukayi don jin ina zata tafi kuma da safe da tace din, mike kafa tayi saman dan stole din da ke gaban ta tana gyara zama take fadin .
Gobe tafiya zamuyi da uncle Sulaiman zuwa abuja zamu tafi muga wurin da yake son saya ya matsa sai baban su yan biyu yaje yaga wurin dani kafin ya saya.
Faiza ne tace ai hakan nada kyau mutum ya dinga sa ba gabatan shi gaba kafin yaya abu sai anty tace wanan ai halin Sulaiman ne.
Har sukaci suka sude ban saka masu baki ba ina daga kwance ina sauraren hiran tasu anan na dan fahinci wani abu a tsakanin su.
Tun da asuba ta shirya wai ashe ta jirgi zasuyi tafiyan bakwai yai masu a airport jirgin su bai dade ba ya daga zuwa abuja.
Muna gida zaune ni da faiza ita kuma fati tun tafiyan su ta fita daga sunan baza ta dade ba sai gashi har hudu na yamma yanzu.
Hudu ya gwauta sai gata hurjanjan ta shigo gidan bata ko kalle mu ba ta shige dakin ta Faiza ta kalle ta ta tabe baki.
Nidai na mayar da hankali ga tv don karamin aikin faiza ne yanzu ta dauko topic din fati aduniya taki jinin Fati da komai nata.
Itama fatin na kula da haka bata kaunar Faiza don takance min munafukace wai don haka zama a taka tsantsan ya kamani a cikin su sai bani yarda daya yayi da daya a bayan shi.
Ban jima ba a wurin na mike na shige daki da yan biyu don bada su aka tafi ba na zata kwana zasuyi sai gashi sun dawo da yamma .
Tana da gajiya don haka bata zauna da mu ba tayi dakin ta don sauke gajiya a jikinta lokacin ne fati ra samu daman shigowa dakina.
Ni sai da naji tsoro lokacin dana ganta tace ke matsoraciya nice na sauke ajiyan zuciya .
Nace may ke faruwa ne Fati na ganki da daren nan haka, ta dai ce uhumm kawai ba tare da tai magana ba takai zaune a wurin .
Tace aike dai baki sani ba yau naje wurin wani mai magani ne a wani kauye wani irin kallo nai mata na dafe kirjina nace maigani kuma ?
May kika tafi nema gun mai magani ko baki da lafiya ne ban sani ba sai naga ta girgiza kai tana cewa haba dai kamar ba mace kike ba .
Zuwa nayi a samo min kan madam din gida da kuma mutumin nawa gaba nane ya fadi ras taci gaba da yi min bayanin abinda ya kaita .
Ban iya karasa sauraren ta ba sakamakon fadawa tunanen danayi mai zurfi a raina nace tabas inda akwai abinda na tsana shine inga mace tana biyan bokaye da malamai a rayuwanta.
Balle fati da ko aure batayi ba ta fada wanan akidar sanan babu kunya babu tsoron Allah ko nauyi bata ji har tana fada min inda ta tafi da yadda akayi.
Wanan abin ba karamin tashin hankali bane musanman ma da tace takai har da anty gun mai magani to aima yar uwar nata may can.
Ida babu kuya babu tsoron Allah take fada muna yadda suka kwashe da boka a take na suma jin hawaye masu dumi na bin kuncina bata farga da hankan ba sai daga baya.
Maganan da tai min ne ya dawo dani hayaci na kallona take yi da wani irin mamaki baiyyane a fuskan ta ta ce dani Safiya may ke faruwa ne naga kina kuka daga ina baki labari.
Girgiza kai nayi cikin takaici nace Fati waya baki wanan shawaran na zuwa wurin boka at dis age da kike har kin san hanya bin bokaye.
Abin haushi da takaici kuma kirasa wacce zaki kai sai yar uwar haihuwar ki wace