Showing 54001 words to 57000 words out of 269010 words

Chapter 19 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13355

zan zauna sai ko naji ya sa hannuwan shi masu kama da na karfe ya hankado ni saman gadon sai na kai kwance.
Tun takwas da wani abu nake dakin bani na fito ba sai daya da wani abu na dare ya koro ni koshi nasan giya zai hada dashi.
Ina fita ruwan zafi na samu nai wanka tare da gassa jikina dashi san nan na samu barci sai dai barcin sama sama nake yin sa.
Da safe na tashi duk jikina yana min ciwo amma don rashi imani sai da yasa na dafa mai ruwa tea ya zauna yasha ya sha ya koshi bai ko kalli gefen da nake ba.
Nima sai harkan gaba make yi ban kula abinda yake sha ba a lokacin har ya gama ya fice na sauke ajiyan zuciya.
Golden morn na hada na karya dashi na mayar maboya na boye sauran inda bai gani na sama yan kitso sun zo min don haka nake busy da jamma, a wata mata ce ta gwada min inda ake sayar da wake da bread a area namu.
Shi na sayo na ci abanicin rana na sai shan ruwa ya biyu bayan har na gama ma mutun biyar kitso bai dawo gida ba na lissafe in kudina na na soke na gyara wurin kamar banyi ba.
Bai ma dawo gidan ba sai dare koda zai shigo a buge ya shigo gidan ranan ko matsin haukan shi baiyi ba.
Washe gari sai karfe goma saura ya tashi sai ya hauni da fada wai yaya akayi ban tashe shi ba har yakai rana.
Badon na gudu ba da ya dake ni son ranshi da naga yana da niyar bugu na bude gida na gudu sai da ya fita na dawo gidan.
Na samu yai baja naja da kaya na yana neman kudi a ciki bai samu komai ba sai dari biyar da na aje canji ya gani ya dauke .
Nagyara kayana tare da mayar da komai inda yake ma dafa abinci naci na koshi na dan kwanta falo in huta sai barci masu kitso suka tayar dani kai biyu na kama ranan kawai.

********* ********* *********
Ina sauri in shirya in tafi gidan su gaida gwago na dake fama da kafa kwana biyu bata ko iya tashi.
Tsaida ni yayi wai sai na dafa mashi ruwan zafi a gurguje na dafa mashi don an dauke wuta na zube mai ya kewa ya na fito kada ya hana ni in yi laifi gun ta.
Yau basu sana a duk yan matan gidan su nan kowa da abinda take yi sai dai masu hira da maza cikin su sunfi yawa.
Na shiga duk suka bini da idoban kula su ba na shiga dakin gwago din na bada baya naji sun kwashe da dariya.
Na shiga naga gwagon nai mata sannu da jiki tana amsa min da kyat inda ciwo har da hali kamar bata son ansa min.
Muka dan zauna tsawon wani lokaci a dakin shiru itace ta kawar da shirun da fadin shi yana gida ne ko ya fita aiki ?
Nace yana gida na barshi zai fita yanzu kaita kada min can ta sake cewa ke har yanzu babu ko batar wata sai aukin akawo maki ki juye a masai.
Shiru nayi ina wasa da yatsun kafana ta sake cewa idan har kin san wani abu kike yin don karki samu ciki idan na gane ki bazaki sha da dadi ba gare ni.
Teema tashigo dakin wanan yarinyar da muka taba haduwa da ita a gidan farin zuwa na tana gani na sai ta washe baki tana min dariya.
Duk naje gidan mukan dan kebe da ita muyi hira wani lokaci takan ziyarce ni ko taje nai mata kitso a sace.
Yau ma mun samu mun killance take cewa dani ashe kin zo nace eh kwana biyu ban ganki ba tace kin san mutanen namu sai a hankali.
Kwana ki hajiya taji natafi wurin ki taita sababi dani ta kar na sake zuwa gidan ku idan na koma duk abinda tai min nina ja wa kaina.
Nace o o zuwan kuma da kike yi an maishe shi tsegumi tace ai basa so na je ba don suna ganin zan fada maki abubuwa gamay da mijin ki.
Tsaki nayi nace in dai wanan mijin nawa ne mai zaki fada mi wanda ban sani ba tai saurin jiyowa gareni tace akwai shi amarya kedai baki sani ba kawai.
Wata sabuwar fuska naga ta fito daga wani daki tana wani shan kamshi tana wani yamutse fuska ta dube mu a wulkance tafita daga gidan.
Da ganin ta goggace takwarai yar barikin gaske ce don basai an fada maka ba tafiya ma tana wani girgiza jiki goggagan karuwa da ita.
Sai naga teema tayi dariya tace dani kinga ta nan nace da ita eh sai kuma tace bari dai zanzo har gida in fada maki magana baiyi a nan an saka muna ido da yawa.
Ban damu da naji komay zata fada min ba muka dauki wani zancen zuwa can naji gaba na yana faduwa da farko na zo da suna yini ne a gidan sai kuma naji bazan iya ba.
Nace zan koma gida na leka gwago tana barci don haka na tafi ban sallamay ta ba Sadiya kawai na sama a gidan
mukai sallama na tafi.
Na murda kofan gidan najishi a bude nai mamaki da har lokacin bai fita ba zuwa aiki ba na tura kofa a sannu na shiga gidan.
Gaba daya baka jin komai sai nishin su a falon basu masan na shigo ba sai ihun da suka ji na kurma don gigicewa.
Da sauri ya tashi yana fadin ke ke ke may ye haka maynene zaki tara muna mutane akai kamar kin ga wani mugun abu.
Ban tsaya saurare shi ba sai na shiga kitchen na dauko yuka na nufo su dashi suna kokarin shigewa daki na nufosu da yuka gadan gadan nai kan yarinyar da yuka sai ya tare ni.
Nai cikin su gaba daya suka shige dakin sai da ya kimtsa yafito yaso ya jibge ni nai tsaye nace wallahi yau idan ka dake ni akan wata mace a gida nan sai nayi karan ka wajen yan sanda.
Fadin da nayi bai yarda ba sai da taji nace dama maman biyu tace ko harara na ka sake yi na fada mata ai karan ka.
Jin na ambaci maman biyu yasa ya dakata dako har yana nade belt zai shirin jibgana dashi yaga banza.
Amma duk da haka sai da ya tureni na fadi gefe na shiga bakina ni kaina naji mamakin kaina da na dake nai masu yankar kauna a gidan.
Ta fita tana wani taunan chewagun sai lokacin ma na gane ashe wanan yarinyar mai sallon da na gani gidan su ne wurin gwago.
Ta kalle ni a wullakance tace kin dauki bashi in dai wanan ne a tare kika samay mu tare kuma zaki barmu.
Ta wuce gaba yaba binta baya suka fice a gidan nasa hannu a kai nace ba shiga uku nikan nawa ya samay ni.
Dama abinda teema tai niyar fadamin kenan ta fasa naji dai tsna cewa ki tafi gida yanzu kada ki wuni a nan .
Naso na tambaye ta sai na share kuma don ban gane manufanta ba don tace magana baiyi a gidan sai dai tazo.
Wanan karon na turza na kafa mashi cin mutunci banji tsoron shi ba yace ke ki rufe min baki Liliya ta fiki komai ke inba kaddaraba may zai kaini aure ki.
Nace kamar yadda ka zamu min mijin kaddara a rayuwana in badon darajan iyayye ba mai zanyi da dan giya mazinaci a rayuw, , , ,
Marin da ya kwashe ni dashi yahanani karasa abinda zan fadi ya samay ni ya mamara awurin yakuma ce.
Auren Liliya zaiyi ko da ita taki shiyasa uwarshi ta aura mashi ni don ya manta da Liliya.
Nace auren ku bai damay ni ba zina daine bazan yarda ashigo har cikin gida ai min ba yace tunda gidan ki ne sai ki hanani abinda nake so yi.
Ranan dai munyi shi ba dadi yafice yabar min gidan bai kwana a gida ba washe gari na shirya zuwa gidan maman biyu.
Na samayta a gida bata fita aiki ranan na bata labarin tace ni wanan mijin naki na rasa wani iri dan iska ne safiya ai mashaya giya wasun su basu damu da mata ba.
Nace anty shi fa tatirin dan iska ne na gaske tace aiko ba irin ki ya kamata ya aura ba daidai dashi ya kamata ya samu yar iska irin shi su saje.
Amma ke ai cutar ki zai ta yi a banza don baki saba da abin yan bariki ba ni fa ina jin tsoron kar ya kwaso maki karuwa su halaka ki.
Nace nima anty abinda nakewa gudu kenan wallahi yau wanan tazo gobe ma wata zai kwaso duk a mutum daya.
Tace Allah dai ya kyauta ban dawo gida ba sai yamma lis koda na dawo gidan yana nan kamar yadda na samay shi alamu sun nuna bai dawo ba har lokacin.
Na kule gidan na shige dakina bayan na gama abinda nakeyi ne na kwanta can cikin dare naji dawowan shi na fito na bude kofan ya shiga ciki.
Fuska a daure babu walwala nima haka na daure fuska na ina budewa na wuce zuwa ciki abina na kwanta.
Da safe kafin na fito yayi sakkon barin gidan duk da yake weekend ne a lokacin amma sai da ya fita gidan .
Can yan iska irin shi fada ya hada su sukai mashi dukan tsiya akan Liliyan Allah ya rama min ya dawo gida jina jina dashi.
Nan ya zube min a falo yana kwala min kira na fito da sauri yace taimaka min da ruwan zafi na gasa kafa na.
Nai kamar kada insa sai na tuna da hadisin da kecewa Aljanan ku na karkashin kafan majajen ku.
Da taimakona ya samu ya gagasa jikin shi da kyan ya samu barci koshi sama sama da safe jikin yai masa tsami sosai.
Kwana biyu bai iya ko dagawa nan yan iska suka shiga shigowa gida maza da matan su wai sun zo gaida shi.
Naga mutane iri iri a gidan wurin dubiya sai na kara tsunke ma alamarin shi a raina nasan ba karamin dan duniya bane ashe nake zaune dashi .
Harda maza masu kitso mata masu dan buje iya cinya da sauran su inaji harda shugaban yan giyan lagos yazo gaida shi wasu in sun zo su bani alheri in sun tarar dani a falon wurin shi don boyewa yake cewa nayi kada su ganni wai yana jin kunya ace nice matar shi.
Gashi ina jinya shi amma sai zagina yake ba kakautawa ranan sai ga mahaifiyar shi tazo ankawo ta ta gaida shi nan na dan ji abinda ya faru da kyau wurin ta.
Sun sha sun bugu ne sai wani yazo yaja liliya sai ya hana su kuma suka tarar mashi sukai mai dukan tsiya sai da aka kwace su.
Abinda yasa bai je asibiti ba yan sanda zasu cisu kudi sosai ne shine akai rufa rufa yake jinya a gida.
Bayan su gwago sun tafi daki na shige naki fitowa yai kira kamar may naki fitowa waje da ya matsa min sai na leko nace kira karuwan ka tai jinyar ka mana .
Ita da kaje fada don ta da ya dauka baza iya ba sai yaga na koma daki na rufo kofana nabarshi zaune a falon.
Zagi kan na sha shi a wurin shi amma baisa na fito ba sai da safe na fito yana zaune yana gyan gyadi saman kujera yana jin motsina ya bude idon shi da sukai ja yace don Allah taimaka min nai brushe kafan nan ya matsamin da ciwo.
Nace karuwan da kai fada a kanta bazata tai maka ma bane ai ita ya kamata tai jinyar ka ba ni ba.
Ya marairaice yana cewa don Allah taimaka min asibiti zan koma a duba min kafar kamar zan share shi sai dai na taimaka mashi yai wanka.
Ranan harda sallah akayi amma saidai a zaune ya ban kudi wai a sayo abin karyawa na safe na hada yace na taimaka mashi yaci sai wani cika nake da batsewa.
Yadawa asibiti da rana sai ga yar iskan ta shigo muna gida da kawayen ta nan suka zube falo ana ta tafka iskanci da iya shege a folon namu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,


🧕🏿1️⃣8️⃣🧕🏿


YAR UWA NOVEL NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KAR KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


Satin shi guda cur a gidan yana zaune yana jin ya Lilliya takar itake jinyan shi kusan ma a gidan take kwana nai magana ya zundumi ubana tun lokacin ban sake kallon su ba.
Idan dai gari ya waye zan masa ina kwana da yaya jikin idan tana kusa zai amsa min da kyat kamar baya son gaisuwan nawa.
Sai in bata kusa zan samu ya dan amsa min har yasani wani abin in mashi ranan maman biyu tazo duba shi ta samu Lillya mane dashi.
Ya dan ji nauyin hakan amma abin su na yan duniya sai bai nuna a fili ba ya basar ta kasa yin shiru tace wanan fa da take manne dakai haka.
Matar kace ko mai, sai yadan yunkura yana cewa No kawatace take dubani.
Kallon mamaki taimai tace amma kasan hakan ba daidai bane agidan ka wata karuwa zata shigo ga matar ka na sunna da sunan wai tana duban ka ai duk abinda zakuyi ku tsaya iya waje ku yi shi.
Lilliya ta dago kai tai mata wani kallon banza tace ke wacece da zaki zage ni da sunan karuwa ai karuwancin ma isa ne ko.
Tace OK yanzu zaki san ni ko wacece ya dago da sauri yana ce mata will you keep quite.
Take ta har zugo mashi maman biyu batai mata magana ba ta mike zuwa kofa ta sa mashi key ta rike ke din a hannun ta.
Waya ta dauko tai kira dashi aka amsa mata sai lokacin suka kulla da ita Lilliya ta dago tana cewa may zaki yi in bariki ne nafiki iya wa tace bissimillah ina son yau inga iya barikin naki.
Taso taja da ita jacket din dake jikin ta tacire sai uniform din ta ya baiyyana dakatar da abinda tai niyar yi mata tayi tana cewa haka kawai zaki zageni.
Karyan bariki kike yau zan gwada maki akwai wa yanda suka fiki suka riga ki shiga bariki da lasisi.
Mari takai mata naji dadin hakan daga inda nake tsaye a rakube jikin kujera.
Taso turzawa amma karfi ba guda ba take ta murde ta kafin tai wani abu aka fara dukan kofan ta je ta bude sai ga kartan sojojin tsaye a kofa ko wani a cikin shirin shi.
Hakkuri ta fara badawa harda shi munafukin yana cewa madam don Allah ayi hakkuri rashin sanin ke wacece yasa tai maki haka.
Arest her tace da su take ko suka kamata saura shi tace shima a tafi dashi fuskata babu burbushin rahama take maganan.
An fice har dashi a gidan wani dadi ya kamani sai hawaye bata ko tsaya ta kaina ba ta fice gidan itama ta bisu.
Daga inda nake tsaye a cikin fargaba da tsoro na mara masu baya ina tsaye motocin su suka wuce dasu.
Ko ba koma yau maman biyu ta daukan min fansan wullakacin da ake min a gidan don ya gama zagine ke nan a kanta ta shigo gidan ta samay ni daki ina kuka nasan abinda ya kara harzuka ta kenan.
Ina zaune takure a cikin damuwa sai gashi ya dawo duk ya jirkita azotana da yadawo zai hauni da duka da zagi yadda ya saba ne.
Sai gashi naga sabanin hakanan ya dawo ya bukaci ruwa masu zafi zai gasa jikin shi dashi sai kuma dan abinda zaici.
Yana zaune bayan ya fito wanka ga abinci a gaban shi yace Safiya ina daki na amsa masa na fito kujera ya nuna min da hannu alaman wai na zauna.
Sannu a hankali na kai zaune saman kujeran ina fuskantar shi tare da sauraren abinda zai fada min a lokacin.
Yace kin dai ga yanda wanan matar suka yi a gidan nan ko na dago kaina a hankali ns dubeshi ya tsare ni da idawan shi.
Na sake dukar da kaina kasa ba tare da na amsa mashi ba yace yanzu dai ba wanan ba abinda nake so dake shine.
Kiwa ita madam din nan magana a sake Lilliya don ba karamin tsaro sukai mata ba yau kawai duk ta jemay saboda tsaro da horo irin nasu na sojoji.
Ban san cewa girman ta da kimarta yakai haka ba sai yau din nan da na gani ke kaidace zakiyi magana a saki Liliya da sauri inba haka ba abin zai jawo min matsala

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login