Showing 51001 words to 54000 words out of 269010 words
magana kice wai ke ta Allah ce ina sanin Allah yake a nan.
Cike da tsoro nace dashi Allah ya baka hakkuri, ya buga min tsawa da fadin rufe mun baki mara kunya kawai.
Ya harare ni sama da kasa a karo na biyu kamar zai kara buguna sai dai na samu ya hakada ni gefe har ina gwauruwa da bango.
Ban sake magana ba na dadafa bango na shige kitchen ina jin shi yana dura min zagi yana fadin duk rana da ya dawo ya samay ni ina shegen kitson nan a gidan nan sai ya balbalani har da mai kitson
Ya gaji da fadan shi ya suri key din motar shi ya fita waje tare da banko min kofan gidan a fusace.
Na nisa a hankali dana ji fitar shi gidan naceai hali baya barin halin sa kwana biyu bai dake ni ba hannusa na masa kai kayi dana tanka ya samay ni yai ta jigga kamar an turo shi.
Na kamala aiki na cikin baci rai kaina namin ciwa kamar zai tsage ina ji ranan ya dawo a buge yana hauka shi ban fito ba karya hada dani.
Kwana ki muka dauka a haka a gidan yana faman daukan fushi dani a gidan da zaran ya shigo gidan zai kuna kida na tashi sama kamar kune na zai tsage.
Da zara na shigo falon idan yana ciki yanzu zai dauko taba ya kunna yana busa hayakin sama yana tashi ya gauraye falon.
Da sauri zan bar abin da nake yi na shige don jin warin nake kamar zan amaye hanjin ciki na kaina ya dinga sarawa.
Yauma bai fita ba tun safe yana gida kuma a falo yake zaune bai shiga ciki ba dole na fito hakana ina aiki na.
Na gama hada abinci na aje mashi nai wuf zan koma daki na yace ka dakata naja na tsaya.
Yana zaune yana ya mutsan fuska yana kallon abincin da na aje a gaban shi kaikace mugun abu na kawo mashi.
Ya wani harde kafa yayi kutun kutun da rai yana busa hayaki sama a zuciya ta nace dan isaka ka fada ma Allah ai.
Ina tsaye har wani lokaci a wurin amma hakan baisa ya dago ya kalle ni ba duk da cewa ni gyara tsayuwa don ya san dani a wurin tsaye.
Dole na gaji na dan yi mai magana dacewa gani yaya gani kamar bada shi nake yi ba shiru yayi yana kallon tv da ke aiki wasu fitsararu na rawa.
Na kara cewa yaya gani don Allah kafada min abinda zan wanka nake som naje nayi nai sallah don lokaci yayi.
Yayi wuf ya mike tsaye yana nunani tare da daka min tsawa ya sake nuni da hunnu yace ke yarinya baki fini sanin Allah ba don ba ke kadai bace yar musulmai.
Idan baki san abinda kike yiba nina san abinda nakeyi kada ki cika min kunnuwa da surutun ki na bashi na dakar dake inji ba.
Shiru nayi ina mamakin wanan mulkin malkan da yake min kamar ya sai boya a gidan zuwa ca na nisa nace a hankali yi hakkuri yaya.
Ya koma ya zauna yana kokarin bude abincin dake gaban shi , can ya dago yana cewa uban wa zai ci maki faten doya da rana.
Tsaye nayi kawai ina kallon shi da mamaki zuciyana yana tafarfasa zangan min uba da yake yi ba gaira ba dalili.
Yace a fusace ba tambayan ki nake ba kinyi shiru kin kyale ni, nace nafada maka bamu da koma a gidan ya kare tun kwana biyu da ya wuce..
Wani kallon sama da kasa yai min ya watsar yana cewa wanda na kawo maki kikai barna yanzu ki barnatar da wanda kika gani.
Bazan sake sayen koma a gidan nan ba sai wata ya kare don bake nake yiwa aiki ba da zaki ta cinye min kudi a banza.
Ikon Allah nace a raina amma a fili cewa nayi dashi yaya ban barnan abinci don ma karya kare ban yin dahuwar rana sai da dare nake dafawa.
Yace ke kika sani ni ba ruwa na kin dai ji abinda na fadi kuma ba zan fasa ba don haka ki bace min da gani.
Har na juya naji yace dauko min ruwa mai sanyi wanan yayi zafi ya fara cin abincin wayan shi yai kara ya dauka tare da fadin kin dawo kenan don naga nomban nigeria.
Ban san may wada yake wayan da ita ta fadi ba naga ya kalli a gogon hannun shi sai yace yau dai duk yadda za ayi zamu hadu.
Yana sauraren ta yana murmushi a fuskan shi abin da ban taba ganin yayin ba a matsayina na matar shi.
Can yace alrigt sai nazo din amma fa kada in samu baki nan ya aje wayan yana ci gaba da cin abincin sa daya gama kushewa.
Ya dago yana kallona nai kicin kicin da rai saurin dauke fuskanshi yayi ya dauki ruwan ya kora ya aje ya mike ya dauke key din shi ya fice daga gidan.
Shiru nayi ina mamaki wanan hali na shi na rashin tsoron Allah a gadarance komai yake sam bai tunawa a akwai Allah.
Kusan karfe daya dare ina kwance har nayi barci na falka naji dawowan shi gidan ya shigo yana may sai dai bai bugu sosai ba.
Don baji yana min haukashi na zagi ba ina jin yana buruntu a falo can naji ya bari nasan ya kwanta ne.
Barci bai kara dauka na ba na shiga tunanen wanan halin nashi shine giya shine taba uwa uba neman mata.
May zai je ya gayawa Allah tsiyan abin kuma baida mafadi da zai tsaya yai mashi fada da nasiha yaji.
Duk iyayyen sun watsar dasu suma suna nasu sharholiyan da muamula da yan iska ta yaya zasu gyara tarbiyan diyan su.
Gaba daya ba na gari dan dama dama yaya saadu koshi ban tabatar da halin shi ba tunda bana shedar shi.
Ina kwance naji hawaye nabin kuncina zuciya na cike da tausayin kaina ga wanan rayuwan da mahaifina ya zabar min yi .
Na tabbatar da i zuwa yanzu baba yana da labarin halin da nake ciki sai dai karfin hali ne kawai irin nasa na jajircewa.
Na nisa tare da gyara kwanciya na tsoro da fargabane ta sauka min a zuciya ta anya ko nima bazan kwashi zunibi a wanan zaman ba.
Washe gari ba abin da zan dafa mu na a gidan don komai ya kare har wurin sha daya rana can naji motsin shi yafito daga dakin shi.
Fita yayi daga gidan na dauke ya shiga gari ne zuwa wani lokaci sai gashi ya dawo da ledan take away a hannun shi.
Lokacin ina folo ina tsaka da gyaran gidan babu kunya ya samu wuri ya zauna tare da cewa in miko mashi goran ruwa.
Nabar abinda nake yi na shiga na dauko kofi tare da goran ruwan na kawo mashi daidai ya bude take away din nasa.
Tozali nayi da rabin kaza sai dan shinkafa a ciki na friderice da aka zuba yasha hadi launin kore shar.
Nan ya zauna babu tsoron Allah ta cinye tas ya wurga min roban a kasa yai zaune yana sakatan hakori da tsike yagama ya jawo taba ya aza.
Sai da na gama abinda nake yi har sha biyu ya gwauta lokacin ana neman karfe daya na rana.
Na fito saye da hijjab dina ina saka takalmi na ya juya a fusace yana fadin ina zaki ?
Ban ko numfasa ba nace neman abinda zanci tunda safe banci komai a ciki na ba yayi saurin cewa to wa ya hanaki kice barnan ki ya kaiki ga karar da abincin da na kawo maki ai.
Nace abincin da ka kawo min yaushe nake barnan shi gidan nan dudu fa kwano biyu ne na shinkafa kuma ko kazon shi baka taba gani a kasa ba.
Kwano biyun ai nayi kokari daso kikeyi na kawo maki buhu komay ai a gida ku ko kwano biyun ana cine na shinkafa.
Daya ke nan kon samu banza shine kike barnatar wa ko ta yanzu kici kuma wallahi in kika kuskura kika fita yau sai na balbala ki a gidan nan.
Alokaci guda jikina yai sanyi nace kayi ma Allah yaya kayi hakkuri in nemi abinda naci kar yunwa ya illanta ni.
Yace bazaki fita ba nace a hankali na matsa wajen shi nadan fara magana a sanyaye cikin kamala nace yaya nasan ka isa ka hana ni fita amma ka tausaya min in samo abinda naci tun da ranan jita wallahi banci komai ba a gidan nan.
Yace ke na fada maki don ba zan yarda ki rika zubar min da kima a waje ba a ganki kinje sayen abu ga hannu.
Da mamaki na dago ina kallon shi bakunya ya fadi haka kamar ince kaida ka sayo abinda kaci fa yanzu.
Nace ya kamata ka tauna maganan ka kafin ka fadi indan ban sayo naci ba may zanci a gidan nan kenan.
Yace ke kika sani gobe in na kawo abinci zaki koyi tatalin shi dakyau ya tashi ya shige dakin shi ya barni tsaye a wurin na bishi da kallon mamaki.
Ina cikin daki na idar da sallah azahar naji fitan shi daga gidan nan na fito falo na zauna sai ga makwaciyana ta shigo wurina bahausa ce akwai dan nisa a tsakanin mu.
Bayan mun gaisa take cewa dani ai tun dazu naso shigowa nasan wanan miskilin mijin naki na gida don naga motar shi a waje .
Nace yanzu ya fita bai dade da fits ba ta na bude hijjib din tace ga dan wake nayi damai da yaji nasan zaki so don nan ba arewa bane na kawo maki na karba ina godiya.
A zuciya na sai kabbara nakewa Allah da yai min mafitan abinci ts ida ban zata ba bata dade ba ta fice tare da min sallama tace tana da aiki gida.
Nai mata godiya na dan raka ta bakin kofa ts fita na koma a sukwa ne daki na hauci hannu baka hannu akushi naci sai da na cinye shi tas na kora da ruwa mai sanyi.
Nai hamdala gs Allah da ya bani abin da zanci shi mugun baiga karshe na ba na bude window dakin da sake fanka kamshin ya fita.
Bai dawo ba sai bayan karfe tara na dare yazo da ledan shi na abinci da na dan wani bussashe burodi ya wuga min daki na ya zauna nan yaci abincin shi ya koshi ya fice gidan tare kulle ni ta baya.
Bai dawo ba sai safe lis koshi don ranan aiki ne nasan zai tafi wurin aiki ya dawo da wuri don kada ya makara.
Ya fice baiko bi ta kaina ba na sauke ajiyan zuciya na mike da sauri na shirya zuwa gidan maman biyu don na samay ta gida kada ta fita office.
Nayi arziki tana shirin fita na iso gidan tana ganina ta aa Safiya yau da safe haka kika bugo sammako.
Maimakon in bata amsa sai kuka bata hanani ba ta zauna tana tare da harde hanneyen ta saman kirjin ta.
Sai da nayi mai isata ta miko min ruwa tace jeki ban daki ki wanke idon ki dashi mikewa nayi ta bini da kallo a ranta tace wake da laifi mahaifina ko mijin koko ni.
Fitowa na ya katse mata tunanen tace zauna a kawo maki abinci kici nasan baki karya ba wanan sammakon da kika bugo haka.
Mai aikin ta ta kwala wa kira tazo tace akawo min abin karyawa aka cika min gaba na da abinci fal na kasa cin komai duk da ina so din amma kincin zuciya ba zai barni naci komai a lokacin.
Ta mike zuwa ciki can ta fito ta samu ban taba komai ba daga cikin abin da aka aje min din.
Tace aa anty yan biyu bakici bama na lafiya dai zan fara kuka tace dani dakata banson yawan kukan nan ki fada min binda ke faruwa.
Dama nasan wanan mijin naka dan iska tuban mazuru yayi ba tuban Allah da annabi yayi ba.
Nace wallahi anty dama kin fada ai nace wallahi anty da yunwa yake horoa na yanzu nan na kwashe komai na fada mata .
Tace dan iska wai ashe bazan sa a kama min dan iskam mijin nan naki ba aimin maganin sa matsalan kawai mahaifin ki da idan yaji zai tsitsine ki a banza.
Anya safiya wana mijin naki kuwa yana cika sallah shi don bai abinda masu imani keyi a rayuwan su.
Nace ina fa yake cika sallah anty ibandam dai gashinan ne daga jumma, a sai jumma,a ake yinta .
Tace kin ga yanzu aiki zani bari na saka a samo maki abinda zaki ci kiyi ki koma gida don yana iya maki tako yaje ya dawo ya gani ko zaki fita.
Tace ki dai kara hakkuri mu gani indan bai daina ba wallahi ni da kaina zanyi karansa a raba wana kaddararen auren naki.
Komai aka hado min mai yawa babu abunda babu na fannin girki da ba a hada min ba niki niki na dawo gida da kayana.
Taimin alkawarin zata dinga zagayowa akai akai tana dubani nai msta godiya ina kuka tace nayi hakkuri ta kawo kudin ta kara min ta wuce zuwa wurin aikin ta.
Ban bata lokaci ba na shiga kawar da kayan kafin mugun ya dawo gidan ya tar dasu ya samu na min iya shege a kan su.
Komai na adana su tsab ba abin da na bari a fili na dawo falo na zauna can ko kamar ta san zai dawo sai gashi ya shigo gidan ina zaune a falo.
Ko kallo ban ishe shi ba ya shige dakin shi fuskan murtun kamar na yan high killer marasa imani dasu jin kadan ya fito ta sake fice wa na nisa tare da fadin macuci azzalumi kawai ta Allah bataka ba.
Kashi dai karfafa ne gashi da tsayi da saje ya kewaye masa fuska a ido kamar kamili idan ka gashi amma duka halinsa ba na saye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,
🧕🏿1️⃣7️⃣🧕🏿
YAR UWA WANAN NOVEL DIN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,
Gani ina gida ya sa ya juya ya fita nasan ba komai ya dawo yi gidan ba abincin da na dauko tun na safe gidan maman biyu shina yini ci a cikina.
Mugun bai dawo gida ba sai da magariba ya shigo da leda biyu a hannun shi na dauka wani abu ya sayo ashe wai garin kwaki ne.
Dayan ledan kuma kayan break fast din safe da zai karya dashi ne ya sayo ce na dauki garin ni ya sayowa na aje mai kayan tea din shi da safe zai karya dashi.
Na dauka nakai saman fridge na aje ashe yana kula dani ban sha ba yace ke garin bazaki sha bane a dakile nace na koshi a harzuke yace kin koshi may kika ci ?.
Nace komai atakaice.
Kamar zaiyi magana sai ya fasa ya sai ya mike zuwa dakina yana bincike baiga komai ba a dakin ya fito yana kutawa.
Yace idan ma baki sha ba ke kika sani ni dai hakkina zaki bani ba ruwa na da rashin cin ki wanan ke ya shafa.
Banko dago kai na kalle shi ba na kurama tv da ta shigo ya samu ina kallon super story.
Tashi nayi zuwa sallah inshai don lokaci yayi ban fito ba ina gurin da na sallama sallah zaune sai gashi ya shigo daga shi sai gajeren wandon boxes a jikin shi.
Kallo daya nai mashi na kawar da kaina don bani son ganin shi a irin siffan nan yace ke bake nake jira bane.
Nai dabur dabur na rasa abinda zanyi gashi ya tsure ni da idanuwan shi jajaye kamar garwashi wuta.
Yace a dake ki samay ni a dakina ina jiran ki gabana ne ya fadi badai wanan dakin matataran karuwan shi da mashayan giya yau zai ce na samay shi ciki.
Dan jin nayi na dan wanj lokaci tunane ya hana zuciya na shakat a lokacin ta shi nayi na bude kaya na na ciro turaren jiki duk na mulke jikina dashi hijjab dina na sallah na cire na nike a saman gado na canza zanin jikina.
Ina tsaye ina kara kintsawa sai gashi ya dawo kamar maye yaso kurwa yace yana zazzare ido wai ashe bake nake jiraba ne.
Tare da tsura min ido kamar zai cinye ni danya nace gani zuwa ina gyarawa ne yaja tsuki ya fice daga dakin nace kaji dashi dai kazami ko wanka baiyi idan za a kwanta dashi.
Na shiga dakin da sallama na yana kwace dadaya saman gadon dakin ga abin taba nan ko ina sakin birjit warwatse a kasa sai kwalaben dake wani gafe a ajiye.
Ina shiga ya kalle ni sama da kasa yace mallama dallah zo konji ina da abin yi tun dazu kin shanya ni ina jiran ki.
Dan matsawa ni bakin gadon