Showing 36001 words to 39000 words out of 269010 words

Chapter 13 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13358

wai ina ruwan shi da matana ne wai
May yasa yake son shiga harkan gidana ne matar shi ko mata na don haka babu ruwan shi ko kashe ta nayi.
Yana tsaye yana huci ya ansa a fusace da haka kace to wallahi jira kaga matakin da zan dauka a kanka ai akwai hukuma a kasan ko sai ya fita a fusace uwar na kwala mashi kira amma bai dawo ba.
Mike tayi a firgice tana fada tana shiryawa tabi bayan shi tare da kiran habiba ta raka ta.
Ina kwance bayan na samu taimakon daga maman biyu tadan bani dan ruwan tea na sha nakoma na kwanta sai dai hannu na ba dama na daga da kafa.
Tana tsaye a kaina suka shigo gidan tun daga kofa take kwala min kira a gigice tana cewa fito muna fukar banza da wufi kawai ganin ban fito ba yasa suka nufi hanyan dakin.
Sai sukai kocibis da maman biyu a kofan dakin kallon kallon sukai wa juna sai gwago din tai karfin halin fadin ina ita Safiyan take ne.
Dan jan jikinta tayi a kofan shiga dakin sai suka samu wurin shiga dakin a kwance suka samay ni sharkaf jiki ba dadi gaba daya na sundule saboda bugu.
Sai ta sasauta fadan da takeyi ta fara cewa uhmm uhmmm aishe abin yayi muni ne haka ban sani ba.
Maman biyu da bata san ko su waye suba sai tace wanan tsinanen mijin nata mara mutunci da tarbiya an baka diya amana don rashin mutunci kai mata wanan dukan kamar zaka kashe ta.
Sai habiba tadan juyo tace mata ai mijin ta ne sai dai itama tabar mai shigan tsagal ga alamarin shi.
Matar tace haba yar uwa ko ke ce ai ba zaki dauki hakan ba mace banza har cikin gidan ki don rashin tarbiya da tsoron Allah.
Tana kokarin cewa na tashi na zauna ta gani sai maman biyun tace ina ga kamar fa ta gwauce ne ko tayi tarmashe.
Don bata iya daga wa sai an kamata maman biyu din ke magana cikin tsigar tausaya wa.
Sai gwagon take cewa na daga ta gani mana.
Habiba tace in ko don taji ana karawa abin gishiri bazata daga ba yanzu.
Aiko maman biyu tai kanta da sabon fitina tana cewa amma dai ke baki da tausayi idan da yar uwar ki ce aikaiwa haka abinda zaki fada ke nan.
Wanan ai rashin tausayawa ne ke fa mace ce kin san zafin wanan abin mutum kobaida tausayi dole ya tausaya mata.
Ta neme fada mata maganan banza tace kama kanki kin kuwa san ko ni wace ce yan zan saka dake da mijin nata a kulle min ku baki daya don kashin kai ya so yi anan.
Sai da taga da gaske maman biyu keyi kuma ta kalleta taga ba raini a jikin ta da gani watace ko matar wani a garin hakan yasa taja bakin ta tai shiru, gwago sai fadi take .
Kaddarane ai ya kawo hakan fada tsakanin mata da miji ba a shiga sai mutun yayi kunya idan ya shiga.
Maman biyu tace amma dai irin wannan abin dole a tausaya wa mutum bari ai ya dawo zan tsawa ta mashi.
Tace yanzu a taimaka akaita asibiti kada yarinyar mutane ta halaka ga banza don shi na mijin kawai na ta yaya kai kaiwa yarinya sanadin haka.
Amma kana ganin ta cikin wani hali ace koda dan paracitamal wanan bazaka iya saya mata ba don tsaban iskanci wallahi ni sai nasaka a adana mun shi bawani abu bane.
Gwago tace a dai yi hakkuri a dan sawo mata dan magani tasha ko zata samu sauki.
Tace What da karfi wanan case din fa ba avin a zauna da ita gida bane.
Sai ga yaya Saadu ya shigo yana fadin a fito da ita mu tafi asibiti fa mota nan na samo a waje gwago tace har asibiti za aika bari a bata magani kawai.
Don kar aje suce sai an kira mijin nata maganan ta zama babban case kuma .
Yace ya zama mana waje ya zama don may zai duketa kuma ya kawo ido yana kallon ta haka kwance a gida.
Maman biyu dake tsaye a kaina tace asibiti kan sai an kaita don wanan bana zama gida bane mutafi tare zan san abinda na fada masu.
An kama ni an fito waje sai maman biyu taga motar hayace suke nufin a shiga tace dasu sallami mai motar ga motar na nan mutafi.
Da motar ta muka tafi ta kaimu wani asibiti na kudi da farko sunce idan duka ne sai anzo da yan sanda sai maman biyu ta dauko id card din ta ta nuna masu sai suka yarda zasu dubani.
Nan aka dubani ni ansamu nayi tarmashe da kuma raune a hakarkarina suka ce dole sai sun bani gado.
Duk maganin da aka rubuta da awo da sauran su itace ta bayar da komai aka bani gado a wani daki ni kadai a ciki.
Nan yaya saadu ya daga wayan shi ya kirashi yake sheda mai yazo an bani gado a asibiti ya fada mai sunan wurin.
Nan ya iso yana mazurai da ido yana kamay kamay sai fadi yake waya kawota asibiti nan na kudi kun san dai bazan kashe kudina ga wanan mara mutuncin ba ga banza.
Maman biyu da take gefe tana kokarin hada min maganin da aka bani insha tun shigowan shi take hararan shi.
Ta dago kai ta harare shi tace amma dai kai ka kai mara mutuncin gaske wallahi ma jin dadin naka yayi yawa da har zaka kashe yar mutane so ba a hukunta ka ba zaka zo kana muna maganan banza a nan.
Ya bita da kallon kallamin ta zuwa gare shi daidai lokacin da take dago ni daga kwance tana bani magani,
Sai faman murde murde nake yi saboda zafin da ciwo da nake ji a jikina ya tsura min ido yana kallon yadda na koma ga ciwo a fuka da hannu duk na goge wurin bugu.
Likita ma ya shigo yana dudubani sai da ya dan bata lokacin shi sosai a kaina ga dan karen tambayoyi da suke min duk yabi ya tsargu sai dai na boye wanda yai min haka don cewa nayi a duhu ne ban san su ba.
Nan nadama yazo mashi gwago ce taja shi zuwa waje ta fara yi mai fada akan ya rage wanan zafin rai don kar yaje ya kashe yar mutane yajawo masu magana.
Idan ma tai maka laifi ne ai basai kai mata mugun duka ba haka har yakai taji rauni maganar yaya Saadu ne suka ji a bayan su yana fadin.
Amma mummy bai kamata ki na haka ba fada ya kamata ki masa kin san fa girman abinda yayi badon wanan matar yau ba abinda zai hana ba adaure shi ba.
Idan ba a daure ni ba sai kai kaje kasa a daure ni mana wai may ye dalilin ka na min shishigi a gidana irin haka matar ka ce ko mata na.
Yaya Saadu yace kauna tace kaga ashe ina da right din da zanga ana cutan ta in saka baki na akai.
Ya zaburo mai shima ya zabura mashi kamar zasu buga gwago taga suna batun tara mata mutane sai ga maman biyu ta fito tace wanan wani rashin mutunci ne haka.
Wallahi in bakai hankali ba sai na sa an daure mun kai yau don baka da tausayi mutumin da ya cece matar ka har zaka zo kana son mai rashi mutunci.
Ta harare shi ta wuce zuwa wurin motar ta sai da ta dan gwauta ya juya yake tambayan su wacece wanan matar ne.
Gwago tace a tare muka samay ta da Safiya a gidan ku ya bita da kallon mamaki har ta dauko abinda zata dauka ta koma ciki koda ta dawo ta sallamay ni nayi barci.
Don haka tafito tana gyara gyalen dake jikin ta tana cewa waye zai zauna da ita a nan don ni zan tafi gida sai suka fara gardama tsakanin gwago da Habiba din.
Taja tsaki ta wuce tana mai jin haushi da Allah waddai da rayuwan su gasunan da ganin su marasa tarbiya dasu kawai ta dan tsaya tana cewa gwago kizo na maidake gida ita yarinyar sai ta zauna.
Ya zama dole subi umurnin ta don sun hango ita din wata ce shiyasa suke kyale ta suna binta a sannu.
A hanya su da gwago take dan binciken ta tana jin wani abu a gamay dani sai take lurar da gwago din nauyin amanan dake kanta na tare da fada mata cewa idan ya kara min irin dukan nan zata sa a daure mata shi.
Gwago ta tsora ta tace insha Allahu ba za a sake ba wanan ma akasi aka samu ayi hakkuri dai zata sauka takawo kudi taba ta tana ta godiya.
Yaya Saadu yace zai tafi wani wuri ya dawo sai ya bar yaya Ahmed da habiba zata fara mashi tsegumi ya katse ta da cewa ke raba ni dan Allah da anyi an ce.
Sai taja bakin ta tai shiru ta tsargu ta koma gefe daya ta rakube wuri daya tana harare harare wa mutanen dake sintiri a haraban asibitin.
Ya fita ya dawo dauke da leda da lemo da ayaba a ciki ya nufo dakin ya shigo ya samu na farka.
Ina zaune ina dan matsa kafana a hankali don haka likita yace dani nayi sai gashi ya shigo dakin babu kunya babu alamunta ya samu wuri ya aje ledan dake a hannun shi.
Yazo ya zauna a kusa dani ga mamakina sai naga ya fara wade ayaba a hankali ya miko min sai na girza kaina alaman a a yace likita yace abaki abin gina jiki saboda haka kici wanan nan.
Yayi niyar wai bani har a baki don yaudara sai na ki karba sai dai ya wade min na karba nakai a baki da kyat.
Naci kamar kwaya uku da kyat don bakina bai da dadi nace ya ishe ni sai ya mayar da ledan ya aje gefe daya ina zaune na langabe kaina a karfen gadon da nake kwance.
Sai naji ya kamo hannun da yafi mun ciwo na dan matsawa a hankali sai da nai kara, yana fadin ai sannu zai warke ya bar ciwo da yake na zugi.
Ban kai ga bashi amsa ba sai ga matar da nake cewa maman biyu mutumiyar kirki ta dawo niki niki da su flask da ledoji da wata yar budurwa bayan ta.
Suka samu wuri gefen gado na suna aje kayan da suka shigo dashi din tana cewa a she kin falka sannu yaya jikin ina sauri karki falka babu abinda zaki ci anan.
Yana zaune ya dukar da kanshi kamar maijin nauyi da kunyan ta sai can tace wanan ne mijin naki ko sai lokacin ya dago yake cewa da ita sannu da zuwa.
Yana kokarin mikewa tsaye ya fita tace dashi No zauna abinka ai tafiya zanyi don ba dadewa zanyi ba dama wanan kayan na kawo sai yarinya da zata dan zauna da ita don naga kaunar bata son zama da ita.
Ya dai mike yana cewa zan dan tafi nan bakin get ne na sayo abu sai ya fice tabishi da harara tana cewa mara mutunci kawai sai ta ja tsuki nasan haushin sa take ji har cikin ranta.
Tace wa yarinya Nafisa dan zauna anan bakin gadon barin zuba mata abincin nan kadan ta danci.
A sanyaye nace nakoshi maman biyu tace da sauri may kika ci da kyat na bude baki nace ayaba naci sai ta kalli wurin ledan ayaban da ya aje tace ina wanan bawan da nagani shi kika ci.
Na kada mata kai alaman eh,
Sai take cewa idan kika biyewa wanan mijin naki mara mutunci kina tunane sai ranki yai ta baci ga banza.
Nan ta zuba min ta jawo kujera a gabana ta zauna ta debo min zanyi gardama tai min jan ido dole na karba.
Ina ci ta jefo min tabaya akan auren mu ina bata amsa a hankali har na dan ci abincin kamar spoon biyar zata karo nace na koshi.
Bata ce dani uffan ba ta aje plate din tare da mikewa tana gyara gyalen kan ta tana cewa barin koma yara suna gida na barsu.
Sallama tai muna ina mata godiya ina share hawayen dake zuba a idanuwa don tun tana tambaya nake kuka.
Ta fice tare da jawa yarinyan kuna akan ta kula sosai idan da matsala ta kirata a waya.
Tai muna sai da safe ta fice daga dakin na dade ina kuka bayan fitan ta dakin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , , ,


🧕🏿1️⃣2️⃣🧕🏿


INA MAI GODIYA GARE KU YAN UWA NA GODE DA KAUNAR KU A GARENI ALLAH YABA HAKKURIN ZAMA DA JUNA NAGODE.

YAR UWA NOVEL DAI NA KUDI NE BA YARDA KI KARANTA BA INDAN BAKI BIYA BA DON BA A YAFE BA, , , ,


Tsaye yake ya jingina jikin shi da motan shi yana busa cigari sai busar da hayaki yake sama da alaman tunane yake yi a lokacin.
Har ta tako zuwa inda yake tsaye yana shagalin shi bai farga da zuwan ta ba sai da tai magana ya dawo cikin hankalin sa.
Tace dashi wanan abinda kake yi ba dabian diyan hausawa bane komai na ba haushe ansa shi ne a cikin kawaici da alkunya.
Murmushi yayi ya jefar da taban dake hannun shi kasa yana takewa a cikin kasa.
Yace hajiya har kin fito kenan tace eh dama na kawo abinci ne da yarinya da zata zauna min da ita don na lura yan uwan nata basu san zama anan gashi tana bukatan mai taimaka mata wani fannin.
Angode yace da ita har ta juya zata fara tafiya sai kuma ta juyu tace dashi a gaskiya wanan dukan yayi muni kwarai da an kai ka ga hukuma ba abin da zai hana su kulle ka wurin su .
Ya kamata ace ka godewa Allah da yabaka mace irin wanan yarinyar dan babu macen da zaka doka a yanzu irin wanan batai karan ka ba.
Yace sherin shedan ne akasi akasamu haka bazai sake faruwa ba in Allah ya yarda.
Taima shi sallama ta yafi bayan ta bashi dan shawarwarin da ya dace na zaman takewa a tsakanin zama ta tafi sai sauke ajiyan zuciya yayi kawai koba komai dai ta rufa mai asiri.
Don irin wanan wayyayun mata ba a shansu a banza amma ita gashi ta rufa mai asiri.
Sai wani tunane yazo mashi a rai a ina safiya tasan wanan mace ne haka da har take mata irin wanan taimakon dole ya sani don gaba.
Sai da na kwashe kwaki sati a sibitin san nan suka sallamay ni kudi dai ya sha kashi sosai na dawo gida har lokacin dari dari nake dashi don nasan mai hali baya fasa halin shi.
Zaune muke a falon da Maman biyu ta wade min lemon da zan sha sai ta tambaya labarin auren mu dashi
Ban boye mata komai daga ciki ba na labarta mata sai tace barin fada maki idan sun tambaye ki ko yaya nake dake ki fada masu cewa ni yar uwan mahaifiyan ki ce tun a gida akace ki nemay ni idan kinzo nan don zan kula da almarinki kamar yar uwata ta jini kike a guri na don muna garin da dan uwa ke bukatan taimako juna.
Tace idan Allah ya hada ki zama da miji dan iska sai hakkuri don gaskiya mijin nan naki yayi nisa da harkan bariki duk na miji da zai iya dauko macen banza zuwa gidan shi tantiri ne.
Don gaskiya sai kin kwantar da hankalinki sosai kin bi halin shi a sannu ki guji duk wani abinda kika san zai jawo maku matsala a tsaka don shi zai iya yi bai zama komai ba amma idan ke kin yi zai iya komawa fitina.
Ki bishi sau da kafa ki guji saka ma alamarisa ido koda yaushe kina jina ko sai na gyada mata kai alaman eh.
Nace cikin murya mai rauni tare da hade miyau bakin cikina a wuyana nace ina iya kokarina don ganin na kyautata mashi.
Amma da yake shi wani irin mutum ne mai hali na daban duk abinda nayi baya gode min.
Sannan abun bakin ciki shine yadda yan uwanshi suka tsane ni sun sani a gaba kamar ba yar uwan su nake ba sam babu kauna a tsakani na da su .
Sanan shi ya kasa fahintar makircinsu na san ba wani abu yasa suke min haka ba sai don sun dauki iyayyena tallaka ni ban kai sa,an auren shi ba ga rayuwan da suke yi a nan don ya banbanta da namu.
Ta katse ni da cewa duk ki manta da wanan yanzu ki kama Allah Allah yana tare da mai hakkuri ko yaushe.
Za a zo ya wayi gari

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login