Showing 120001 words to 123000 words out of 269010 words

Chapter 41 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13311

tace Safiya haklin ki ne ya ja maki .
In dai baka dauki kan ka da fadi ba Allah yana taimakon bawan sa ta ida bai zata ba Allah ne ya kawo ta cikin rayuwan ki don ta taimaka maki.
Gashi tun yanzu muga haske badon Allah ya kawo ki ba wanan alamarin yaya zamuyi kena da haka zamuyi ta kallon shi a gida babu mai taimaka muna.
Shiyasa nake ganin haukan innar ku da bata da kalamin alheri sai na tsiya akan yayan mutane duk da wanan abin da ya cika dasu kuwa.
Murmushi nayi nace banga ranan da inna zata daina halinta ba ita haka Allah ya halicce ta da hassada don bata bar kowa ba a gidan.
Tace bata fa dainawa don dubi abinda tayi jiya Sani ne kawai mai taka mata burki don badon shi ba jiya ba karamin tashin hankali za a yi ba.
Nace niko ban ga Saadatu ba ma tace tana nan daki bata jin dadin jikin ne don duk da malam ya hana a zubar da cikin jikin ta amma bai hana uwan bata abubuwa a boye ba.
Nace na shiga uku mama karfa ta kashe ta tace in ma ta kashe ta ai ita ta sani waya ci baya ina mahaifiyar ki data rungumi kaddara ba ga abin yazo mata da sauki ba.
Mu dai fatan mu ubangiji ya baki miji ki aure ki huta da zargin cewa zaman banza kike yi a can na ce ai Allah yagani mama.
Ban yi ba da sai yanzu da lalura a jikina zanyi in cutawa mutane ko mai tace ai bata gane hakan ita don idon ta ya rufe ko.
Motsawan da baba yayi yana fadin a bashi ruwa yasa mu tashi muka ce yayi hakkuri an daura mai ruwa nace barin fita in nemo likita a fada mai.
Naje gun nurse din ward din mu na fada mashi sai yazo ya duba baban ya fita kiran likita sai gasu sun dawo tare da likitan yadan duba baba din tare da zare mai ruwan da suke kara mashi din.
Yace a barshi ya dan huta zai daina jin kishin da yake ji nan dai suka kara taruwa a kasa suna mashi gwaje gwaje irin nasu na likitoci.
Yaya Nura suka iso shi da su ummi da mama da rana nan suka samu yana barci bayan gaisawan da mukayi dasu ne mama take masu bayanin halin da baba din ke ciki yanzu.
Nan dai muka wuni dasu sai zuwa yamma sukace zasu tafi drive nan dan arziki yace in bari ya mayar dasu sukace ya bari zasu shiga motar kasuwa inna sai baza ido takeyi wirin kalle kalle a asibitin.
Ya kwashe ya wuce dasu hankalin gida zai kwanta yanzu da suka zo suka gan shi dan da basu zo ba duk wayan da muke yi dasu basu yarda a yadda muka fito dashi gida wai ya samu lafiya yanzu.
Baba yana samun kulan da ya dace sosai dashi sannu a hankali yake samun sauki na shigan shi yana dan dada murmurewa .
A kwana na uku ne driver da ya kawo ni yace zai koma gida na bashi kudi yaki karba amma sai naba yaya Sani ya bashi idan sun fita.
Ban wasa da shan maganina don dama ina dashi anty tana kaini ansa a sace bada sanin kowa ba a can lagos din don haka ban da matsala wurin amsan maganin .
A kwana na shida aka sallamay mu nan muka samu motar muka dauka ta dawo damu gida kowa na ta farin ciki yadda suka ga baba ya samu sauki.
Sai dai an bashi dokoki na ya rage tunane da abincin da ya kamata yaci don ya samu lafiya muka sayo magani wadatacce muka dawo gida dashi.
Dakin mu na shiga na cire kayan dake jikina don duk warin asibiti duke yi wanka naje nayi na shirya sai na fito zuwa dakin inna.
Saadatu na kwance duk ta kumbure nace subbahanallahi Saadatu may ke faruwa haka kina zuwa asibiti kuwa maimakon tai magana sai kuka ne yazo mata.
Zama nayi a kusa da ita nace bari kuka saadatu haka Allah ya nufa damu sai dai istigifar ga bawa nace kin je asibiti tace wa zai kaini Safiya dan jike jike dai inna ke bani ina sha.
Nace zuwa zamuyi gidan mau ta dubaki mu gani tace uhumm Safiya ai da na dauka halin innan mu yasa kin fita batuna ne dan da kika zo baki nemay ba harda kuka nayi gashi ban iya fita ko ina.
Nace haba saadatu may zai sa inyi fushi dake ke fa yar uwata ce ta jini halin inna kuma inda sabi ai na saba yanzu sai dai addua kawai.
Da taimako na ta samu ta shirya don inna na dakin baba sai fitowan mu suka gani kawai take cewa ina kuma zaku haka ?
Nace wiri mau ta duba lafiyan jikin ta don ba a barta haka ba tana wahala tace ai ita taja wa kanta ina ruwan wani saaden tace dani mutafi kin ji safiya.
Nan muka fice muka barta mashin na tare ta hau nima na hau mukaje gidan an dubata take muna bayani bata samun kulawa ne sosai an mata allurai don tace akwai maleria masu ciki a jikin ta do haka tabar bari sauro na cizon ta ta bamu magani tare da fada mata abinda ya kamata taci kuma ta dinga zuwa ana dubata akaiakai.
Bamu dawo gida ba sai da na sayo mata abin bukatun ta harda gidan sauro muka dawo gida yamma tayi a lokacin nan ina ta ke cewa .
Yanzu dai anyi kudin da bamu san asalin shi ba anzo ana muna facali a gida indai tai wari ai maji komai daren dadewa .
Ba wanda ya kulata sai dare muka samu kebewa da ummina nan muka shiga hiran yaushile rabo da ita nake fada mata duk yadda nake can.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,

🧕🏿4️⃣1️⃣🧕🏿


Ummi ta nisa bayan ta gama sauraren magana na tana cewa dani anya yar nan baki iya tsaga fadi ba wanan mutumin bai fi karfin mu ba.
Na ce ummi nima abinda nake tunane kenan amma ita anty bata son ina fadin haka din tace yanzun dai ki dan kara nazari kafin ki kai ga gabatar dashi nan din.
Fadan inna da mukaji shiya dakatar damu daga maganan da mukeyi din da muka saurara muka fahinci da saadatu ne take fadan akan daura gidan sauron da muka sayo.
Fada sosai suke yi a tsakanin su nice na fito nayi wa saadatu magana sai take cewa wai inna tace bata yarda ta daura gidan sauron ba a dakin ta.
Nace haba inna tana da wani daki yanzu a gidan nan bayan naki don Allah ki yi hakkuri kibarta ta daura daidai inda take kwanci.
Nayi dana sanin fitowa raba fadan nan tsakanin inna da diyar ta don abin karshe a kaina ya dawo babu irin kazafin da inna bataimun ba ranan kowa najin ta a gari.
Dole naja kafana na koma dakin mu bisa umurnin mama har lokacin bata daina fadan da take yi ba ta hade mu ta zage tas tana cewa sai dai yawon banza amma badai aure ba gare ni.
Naje nayi fasikanci na nadawo ina wa mutane sallo sai inyi wa wa yanda basu san abinda nake yi ba .
Ummi tace da na hanaki fita zakiga kamar ban son zaman lafiya ne ai gashi kin jawo wa kanki kwana da bakin ciki a ran ki.
Nidai shirin kwanciya nake yi ina kara jimamay maganan Inna datake yawan fada min a koda yau she magana ya hada ta damu.
Ya zama min dole in yarda da bukatar Sulaiman akaina kamar yadda yace bai son abin ya dauki lokaci don shi yanzu bai ga abinda zamu tsaya jira ba .
Magana ummi keyi dani amma banji ba nayi nisa sai da ta kara daga murya na ji ta nai saurin cewa ummi kanin mijin anty na ne.
Kuma su suka hada ni dashi don shima irin matsalar mu guda dashi aure yayi matar ta rufe mai tana da lalura sai da akayi abin ya bayana mata.
Bacin rai yasa ya rabu da ita duka duka watan su shidda da aure suka rabu da ita tace amma ko bai kamata ya sake ta ba tunda ya dai riga da ya kamu da ciwon.
Nace ai nima abinda nagani ke nan amma sai anty tace dani dama ba sonta yakeyi ba itace ta like mashi.
Yanzu ke baki ganin akwai matsala idan kika bashi baki akan ya fito nifa ina tsoron masu kudin nan don da wuya suke rikon aure.
Nace ummi duk wanan tunanen nayi shi kuma na fada ma anty amma sai cewa tayi nasan dai ba zata kaini inda za a cuce ni ba kin ga banda ta cewa don darajan ta a gare ni.
Amma dai ni sanin da nai mai baida wani matsala rayuwa sai dai ba a san abinda ke boye ba kwai ne.
Tace yanzu dai kafin ki koma sai ki shirya kije can gida ki ga baba da yaya Adamu ki fada masu in ma mallam ya yarda sai mu tafi tare dake mu gan su.
Nace to ummi hakan ya kamata ayi nima dai hankali na bai gama kwatawa ba dashi amma babu yadda zanyi ne kawai sai ya zama kamar na watsa ma anty kasa a ido bisa kokarin da takeyi dani.
Haka na muka kwanta kowa da tunanen da yake yi a zuciyar shi sai asuba muka tashi bayan nayi sallah na fito na share gidan na tara kwanonin da akai amfani dasu.
Ina cikin wanke wanke ne na kusa gamawa sai ga inna ta fito sai cewa tayi dama ko acan abinda ke yi ke nan anzo nan za ai muna barkadon banza.
Nace inna ina kwana bata amsa min ba ta shiga daki sai gata tafito da kwanoni masu yawa ta zube min su ashe mama na daga kofan ta tana kallon mu.
Inna ta wuce tana maganganun ta sai mama tace kai wanan balain da may yai kama don Allah ba a barin mutane suji da abinda ya damay su sai bakin fitina tun da farin safiya haka.
Wa na hana yadda yake so a gidan nan idan kuma kin saka kan ki ne sai a sayar maki ba abune mai wuya ba ehhy.
Mama tace in ma zaki iya nan da shekara sai ki tayi bama sayar ba ko kwasa ne sai ki yi gaki ga wuri ai.
Wanan abu damay yai kama kin kwana fitina kin tashi dashi duk yarinyar nan bata kula ki ba ba sai kiba kanki lafiya ba wanan ai zubar da mutunci ne gare ki.
Nan dai sukai dan cacan baki tsakanin su ba wanda ya kula ta ni dai na gama na shige dakina na barsu nan.
Wanka na fito nayi ina cikin gyara jikina sai ga Saadatu ta shigo dakin ummi din ta samay ni muka gaisa.
Nake tambayan ta yaya jikin ta sai tai murmushi tace jiya na samu barci sosai wallahi Safiya na gode kwarai wallahi banda abinda zan fada maki sai dai kuma kiyi hakkuri da halin inna don Allah.
Na yi murmushi nace ai inna uwane fadan su gare mu taki wata rana zai muna amfani a gare mu dariya ta dan yi tace kayya ke dai kiyi hakkuri kawai.
Muna nan muna dan hira sai jin muryan inna mukayi tana kwala ma saadatu kira share uwar tayi kamar bata jita ba.
Sai da ta kara kiranta tace tana zuwa ta ci gaba da maganan ta sai da nace taje taji kiran da inna ke mata ta dawo.
Bayan fitan ta ne na ci gaba da shiri na nace ma ummi gidan gwagon ta zan tafi in gaida ita tace dani aiko kin kyauta.
Nace a debi tsaraba abawa kowa har da makwabta tace kidai diba sai ki ba mutanen gidan abasu sai na makwabtan duk ki diban masu.
Dole na tsaya nayi kamar yadda tace inyi din tace haka yayi bayan na raba na dauki na fanin su gwago aka fita min dashi waje inda zan samu mashin din da zai kai mu gidan gwago din.
Mu kafito ni da kauna na da zata rakani gidajen uwayen mu muka hau mashin sai gidan gwago anan muka shiririce da ita har lokaci yayi mun fito.
Mun tashi muna batun zuwa gida maman mu bayan muyi sallah azahar ta dafa muna taliyan hausa da manja munci mun fito sai ga kani na saman keke ya biyo mu.
Nace lafiya ka biyo mu haka yace anty wai kizo wasu mutane suka zo wurin ki a wata irin katuwar mota.
Anty baki gansu ba kamar bature dayan mutumin suna nan sun shiga gida gaida baba shine ummi tace in zo in kiraki.
Na ce ni fa kace shafiu yace wallahi anty don Allah kiyi sauri don da ganin su masu kudi ne baki ga motan da suka zo da ita ba fa.
Gwago tace yi maza ki je tunda an aiko kiranki Allah dai yasa muji alheri dariya nayi kawai sai nace bari mu aje maki sakon su mama anan mi tafi.
Juyawa mukayi zuwa gida tun da muka karyo kwana na hango motan take naji gabana ya fadi nace to waye yazo har nan wuri na ?
Haka dai muka shiga gidan da fargaba ko waye yazo a kofan ummi muka hango takalman su ga awakin ina sun zo suna hawan takalmin nasu mama tana korewa muka shigo.
Wurin mama na nufa ina tambayan ta ko su waye tace haba Safiya ashe abin arziki muka samu baki sanar da kowa ba sai yanzu da bakin ki suka shigo gaida mahaifin ku suke sanar damu.
Na danji kunya nace kai mama ho baga shi kun sani ba yanzu ai sai yace cikin shake muryanta ai baki sani ba tun shigowan su mutumiyar ta shige daki bata fito ba nace wake nan mama.
Tace wa kika sani banda innar ku uwar yan hassada kuwa ake dai bari shiga dakin baban ku kiga abin arzikin da suka zo muna dashi.
Yaya sani ne ya shigo da kwalaben abinsha gidan a cikin leda yana sauri ya nufi dakin ummi dashi nace Allah sarki dan uwa ko ina ya samu kudin da ya karma min bakin dashi oho ?
Ya fito dakin ya ganni yace a, a ashema kin dawo ga baki mun samu daga abuja sin zo wurin ki kin kuma zo nan kin tsaya jin na dawo yasa ummi dake zaune a takure dakin fitowa ta bamu wuri.
Nan na shiga da kunya dakin da sallama na suna zaune saman tabarman da aka shimfida masu hankali kwance ga dan wake a gaban su da akayi gidan suna dan cokala suna ci.
Hamza ne ya amsa min sallama na yana dauko dan wake a kwano yace a a amaryan mu ina kika je bamu baki izzini ba haka.
Dan dariya nayi nace gidan kakata naje don tun da nazo ban je na gaida ita ba sai yau sai kuma akace min nayi baki.
Nan na dan dago kai na kalle shi bai ko dago kai ba sai cin dan wanken shi yakeyi kamar bai san ina wurin ba ma.
Yace dama ai ba ita mukazo gani ba mun dai ga wanda muka zo dubawa gashi har ummin mu ta bamu wanan abincin da na dade ban ciba muna ci.
Nace aiko abu yayi kyau amma sai dai kaci kadan kasan a gidan sarakkai kake yace ina nan ai yanzu nima na zama dan gida baki ganina a kuryan dakin uwana zaune.
Kara shiga dakin nayi yayin da na dan rakube a gefen dan gadon katakon ummi sai hamza ke cewa dashi a gara ki fada mai don naga yana batun mubar kwanon kawai.
Nace yaya hanya suka amsa da lafiya nace amma uncle shine da mukai waya dakai dazun baka fada min kuna haya ba a shirya ma zuwan ku.
Sai yace akwai shirin da yafi wanan ne a gare mu munzo munga mai jiki kima mun gabatar da kan mu an kuma ce ambamu abinda muke so gaya min akwai abinda yafi wanan farin ciki .
Sai ya samay hannushi daga kwanon tare da aje fork din da suke cin danwaken dashi yace naji dadin da ummi tace kin fada mata komai a kaina shi kuma baba ya amince dani albarkacin madam.
So ni yanzu banda wani shaku na neman ki don naga inda kika fito dakuma yan uwanki na kuma yaba da abinda idona ya ganan min.
Karya da rashin asalin shine ba a son a cikin zance naga komai kuma na gamsu da hakan yazu idan na koma munyi waya da madam da mijin ta za a zo a nema min auren ki kamar yadda sharia da alada ya tana da don na fada maki ban son wanan abin ya dauki lokaci mai tsawo .
Ina bukatan azumin bana inyi shi da matata a dakin ta don ban son a sakani cikin gwauraye kuma.
Kaina na kasa duk kunya da nauyi sun cika ni suka ce in kira masu ummi suyi sallama da ita don zasu kama hanya saboda nisa.
Na daga tsam zuwa kiran

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login