Showing 249001 words to 252000 words out of 269010 words
shaye maganin na koma na kwanta fita yayi ya samu Nura mai aiki yace ta hado min tea takai min dakina.
Ina kwance sai ga Nura ta shigo dakin dauke da dan karamin tire a hannun ta da kayan tea ta kawo min tana min sannu.
Ban tashi ba sai ga uncle ya shigo dakin na lura sallah yayi yana fadin kinsha tea din kuwa yana kai idon shi inda kayan suke aje kai kawai na girgiza mai alaman ban sha ba.
Zama yayi ya hada min tea din yana tashi kisha cikin commad yayi maganan shi bawai alaman lalashi ba dole na tashi na sha tea din rabin kofi na koma na kwanta ya mike yana fadin zai dan fita ba dadewa zaiyi ba zai dawo.
Har yakai kofa wani irin amai ya taso min da sauri na yunkura zuwa ban daki kafin in isa na sake amai mai karfi a tsakiyan daki na.
Wani irin kallo ya bini dashi tare da yi min sannu cikin tausayawa a gare ni na karasa zuwa ban daki amai nayi sosai duk da ba komai a cikina.
Fita yayi ya fadawa mummy nayi amai na bata dakina dashi da sauri ta taso da Abba goye a bayan ta ta nufi dakin nawa.
Mummy ta gashe ni ta sauke yaron ta fara gyaran wurin dana bata din da amai sai sannu nake mata ina fadin ai da ta barshi zan gyara wurin ko ta turo su maimu su gyara don suna gida yau ba islamiya.
Tace haba wanan ai ba komai bane aikina ne barin yi ta gama gyara wurin ta dawo tadan zauna sai ga maimu tashi tana saye da wandon tie baki iya gwiwa da yellow din dan riga sannu take min cikin tausayawa.
Nace jeki kitchen ki dauko min lemo guda biyu ki wade min su ki kawo min da sauri ta fita ta dan dauki lokaci ta kawo min na yunkura na tashi dakyat na iya shaye guda na koma na kwanta don sam banjin dadin jiki na.
Ban dade da kwanciya sai barci yau ni dake hana wasu barcin bayan laasar sai gashi ni ina yi fita mummy tayi da yara don kada su ta dani tare da jawo min kofan dakin.
Uncle ya dawo gida kafin magariba ya wuce dakina kai tsaye ya tura kofan ya samu ina barci ga lemon da aka wade min a gefe na aje yadan dade tsaye kaina ban san ya shigo ba.
Ya dan taba ni kadan sai na bude idona yace tashi magariba ya gabato da kyat na samu na tashi zaune yayi min sannu da kara tambaya ko na sake yin aman bayan fitar shi nace banyi Allah ya sauwa yayi min.
Bayan fitan shi daga dakin na daure na tashi na shiga bayi wanka nayi da ruwa masu dumi sosai na dan gasa jikina tare da dauro alwala na fito.
Sai da na zauna na dan huta na mike na gabatar da sallah a inda na idar na sake dunkulewa a cikin hijabi na banyi barci ba ina jiran inyi ishai a wurin mummy ne tashigo duba na.
Ta samu nayi sallah ta yi min yaya jikin nace da sauki mummy murya can kasa kasa na amsa mata tace har yanzu bai fada maki ba ?
Nace na rage jin sanyi yanzu kaina ke ciwo kamar ya tsage nake jin shi sannu tayi min ta dan jima zaune a wuri duk da ba hira muke yi ba a lokacin sallah ya tayar da ita tana idar wa suka dawo tare dasu hindatu suka zauna a dakin.
Uncle ya dawo dauke da ledoji a hannun shi dakin ya nufa dasu su Mommy na ganin shi suka shiga gayar dashi hindatu da maimu suna rige rigen amsan ledojin dake hannun shi din.
Mika masu yayi tare da fadin su aje karamin su tafi da babban suci ya juya wurin mommy data mike tsaye ko tana shirin fita dakin .
Yana tambayan ta bata kara amai ba ko mummy tace bata sakeyi ba sai dai kanta tace yana mata ciwo sosai kamar zai tsage.
Yace kuma again ban san may yasa zata boye min bata da lafiya haka ba har saida abin yayi nisa sosai yanzu ai ba a wasa da ciwo.
Tace kila bata dauka sosai bane haka ko irin dan zazzabin da kan zo ya wuce ma mutum ne shaaa .
Fitan mummy ya dan kwanto yana tambayana yadda nake ji nace da sauki yace kan fa ya lafa yanzu nace eh kawai badon ya lafa min ba din.
Ya ce in tashi inci wani abu ga nama na da fresh milk in sha kai na girgiza alaman a a yace to a hado maki tea ki sake sha nacs uncle ko nasha ba zai zauna min ba ne .
Ya mike yana bakuma zaki kwanta da yunwa ba kin sani dole ne kici wani abu sai cewa nayi koko zan sha ka fada wa mommy.
Koko kuma a ina za a samay shu yanzu da daren nan nace muna da abindama shi a fridge mommy ta san inda yake na bashi amsa.
Uhmmm yace kawai ya mike tsaye ya nufi wurin mommy din ya fada mata abinda nace ta tashi da sauri ta shiga kitchen din don Nura ta tafi gida ko dare yayi.
Ta damo min kunun ta kawo min shi na dan samu na sha ya zauna min a cikina har na samu barci ya dauke ni sosai ban farko ba sai cikin dare fitsari ya tayar dani.
Nan dakina naga uncle kwace a kusa dani yana barci jin motsina bayan na fito banda yasa shi falkawa yace yaya ne kuma ?
Nace ban daki na fito da sauri yace haras wan ne kuma nacs fitsari nayi yaya jikin yanzu nace da sauki cikin gundura da magana na haye gadon na kwanta a bayan shi.
Haka barci ya kara daukan mu sallah asuba ya fita yi don jin jikina yadda ya gashe kuma ina rawan sanyi yasa shi fita bai tayar dani ba.
Har yaje massalaci ya dawo ina kwance sai kaduwa jikina keyi ina wani irin sam bato hakorana suna kadawa da yan uwan su na kasa.
Hawowa yayi saman gadon tare da dan tallabo ni yana fadin tashi muje asibiti hakana .
Kasa tashi nayi dakyat ya samu na tashi nace kuma zanyi sallah kina iyawa yace dani kai kawai na gyada mai na shiga ban dakin ya biyoni ciki har nayi alwala na gama na fito ya miko min hijjab dina.
Da kyat na sallamay bai saya jiran komai ba ya dagani muka fita daga dakin da kanshi ya toka motar muka fice a gidan bayan ya buga ma mommy zamu tafi asibiti tace jikin ne har yanzu ?
Eh kawai yace ya fice bamu dawo gida ba sai da suka bani gado suka kwantar dani likitan shi ne a kaina sai wasu dakan dan shigo sun debi fitsarina da jini zasu auna su gani.
Alluran da akai min yasa ni barci sosai fita yayi ya kira yaya Saadu ya fada mai anbani gado ya kashe ya kira Aisha tace gata nan zuwa da ta sauke yara makaranta.
Gida ya kira mommy ya fada mata don hankalin ta ya kwanta shigowan yaya Saadune da samira na dan falka ban dade ba na koma barcin don karfin alluran da akai min din.
Zuwan su samira yasa shi komawa gida don anan suka barsu a tare dani sai barci nakeyi hankali kwance ga ruwa daure a hannu na .
Aisha ta zo nan suka hade wurin suna dan hira mummy da zai dawo bayan yara sun tafi makarantane yazo da ita don ance sai sha biyu result zai fito na test din da akayi.
Bai shigo dakin ba amso result din yayi suka hade da likita bayan ya karba yafita sai ya dawo dakin da nake kwance din sun gaisa dashi ya nufi wurin gadon yana tambaya ban falka ba har yanzu ?
Samira tace na dan falka dazu ban dade ba kuma na koma barci ya dade tsaye a kaina ya juya ya fita sai suka hade da likitan.
Hannu likitan ya mika mai yana fadin congratulation sir madam.cikine gare ta har five week shine ya jawo mata ciwo haka kuma kasan yanayin jikin nata gashi kuma bata dade da haihuwa ba strees yayi mata yawa ne.
Wani irin lumshe ido uncle yayi tare da dan rike hannun likitan yana fadin ya gode kamar shi ya bani cikin.
Takardan magani ya mika mai yace asamo wanan maganin idan ta tashi zata samu sauki sai tasha don jikin nata ya samu dan karfi don yanayin ta.
Bai dawo dakin ba don mata sunyi yawa a ciki yake gani wurin sayen magani ya tafi daga can ya wuce office ya duba wasu bakin da yayi sai bayan la,asar sosai ya shigo asibitin.
Lokacin ina zaune ina tauna Apple din da nace yaya Saadu yazo min dashi idan zai zo gaishe sukayi ya amsa a duduke ba tare da ya kalle su ba.
Bakin gadon ya karaso yana tambayana yaya jiki da sauki kawai na iya bashi amsa ya kalle ni duk na ramay na fada a lokaci guda kamar na dade ina ciwo .
Fita suka fariyi a dakin kamar wa yan da ya kora bansan may sa suke shakkan shi idan yana wuri har samira bata sakewa takan ce dani mijin nan naki kamar ustazu yake baya kallon mutane ko kana gaida shi sai ya dinga yi kamar yana tsoron mata.
Muryan shi naji yana ce min cin fruits din ya tashi ko da sauri na kalle shi sai kuma na sadda kaina nayi kasa .
Sai kuma na dago nace dashi ciwo yasani ci idan bashi na dan ci ba banjin dadin baki na yace aifa yanzu banda sauran wasa da saye fruits .
Haba uncle daga ciwo kuma sai in buge da shan fruits ko yaushe murmishi yayi yana gyara zama da kyau yace yanzu yaya kike ji naji sauki na fadi a hankali kamar banson magana.
Ga magani likita ya rubuta yace a sayo dazun sai kin ci wani abu zaki sha don haka barin fita in kira Aisha ta zuba maki kici sai ki sha ido na lumshe a hankali tare da fadin bazan ci abinci ba zan dai sha koko da mummy ta damo min.
Yace ok kisha din sai ki sha maganin ya mike ya fita ya kira Aisha tazo ta zuba min ya dawo ya zauna inda ya tashi yana zaune har na gama sha ya bare maganin ya bani na hadiye na koma na kwanta.
Kwana daya nayi aka sallamay muka koma gida ba laifi don na samu lafiya sosai sai dai jikin nawa ba karfi har lokacin su Maimu da hindatu keyi wa Abba wasa ina zaune na kura masu ido kawai banjin dadin hayaniyar nasu amma kuma ban iya tsawata masu su bari.
Mummy ne ta fito tana masu fada daga dakin ta lokacin uncle ya shigo gidan zama yayi nan falo inda muke mommy ta gaida da dawowa.
Bayan ya tambayeni jikin yana yi ma abba dan wasa ya leke mai wai ya dauke shi yace tafi wurin uwar ka maimu zan dan watsa ruwane a jikina.
Ya mike ya shiga dakin shi ya jima a ciki na tashi na bishi dakin nashi don ban iya jure hayaniyan da yaran ke yi haka kawai nake jin haushi komai ba gaira ba dalili.
Shiga nayi na kwanta saman gado har ya fito ya samay ni a nan nan kika dawo kuma nace haniyan yaran nake jin shi har cikin raina wallahi.
Sai da ya gama shirin shi yasa jallabiya ya fesa turare a jikin shi haka yasa nasan bazai fita ba ke nan yau kuma don baya fita hakana.
Takowa yayi inda nake din yazo ya zauna safiya naji ya kira sunana a hankali na dan bude idona da suke lumshe na sauke akan shi tare da dan kakaro murmushi a fuskana kadan.
Kin san kina dauke da ciki a jikin ki na wata daya da kwanaki da sauri na daga daga kwanciyan da nake ina fadin na shiga uku.
Kin sha uku akan may safiya ban taba zaton jin wanan furucin daga bakin ki ba domin ko abin farin cikine ya samay mu bana shiga uku ba.
Uncle abi fari ciki fa kace yaro na yana da wata bakwai uncle zakace wai abin farin ciki ya samay mu ?
Kallon da yake min ne yasani natsuwa na farga da katobaran da nake shirin yi a gaban shi a yadda na san shi da son haihuwa yanzu.
Yana yawan fada min shi haihuwa yake so yayi yanzu yana son ganin yara sun cika mai gida kamar sauran gidajen yan uwan shi da abokai.
Sai gashi ina shirin yin baranbarama da albishir din da yake min na dan cikin da ke jikina wanda ashe shiyani zazzabin nan da nake yi duk dare.
A hankali na koma na kwanta tare da lumshe idona ina mai jin zafi a raina da samun wanan cikin na jikina a wanan lokacin da ban tsamace shi ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/21/20, 9:58 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , , , ,
🧕🏿8️⃣4️⃣🧕
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Fita yayi daga dakin batare da ya kara magana komai ba nima komawa nayi na kwanta ina jin zuciya na yana min zafi maikon in ji farin ciki a raina.
Ba don komai ba sai irin surutun da mutane zasu dinga yi ga haihuwa na a kai akai da nake yi kowa zai fassara min shi da wata manufa ta daban.
Na dade a wurin kwance ban motsa ba shi kuma bai shigo dakin ba har wanan lokacin barci ne ya dauke ni wanda na dade ina yi sai a zahar na tashi don sallah.
Ko da na fito nasamu bai gidan sun fita da yaran zuwa shan ice cream dakina na nufa ban iya yin wani abuba a dakin sai kwanciya da nayi.
Ina nan kwance sai ga hindatu ta shigo da Abba dauke a hannun ta maimu na bayan ta dauke da ledan tsara da ya sayo masu.
Suna zuwa suka fada min a jiki gaba dayan su na dan lumshe idanuwa a hankali ina jin su a jikina kun dawo nace dasu anty kin ga abubuwan da baba Abba ya sayo muna yakai mu mun ga biri da zaki abubuwa da yawa muka gani inji hindu.
Murmushi nayi nace su bude kayan in gani ba komai bane sai tarkacen kayan lashe lashe na yara dasu yought din robobi nace sai kuje wurin mummy kuyi ta sha ai.
Na samu na iza su suna fita na sauke ajiyan zuciya har wani lokaci banji motsin uncle da banyi ba yasa banji dadin haka ba a raina nasan idan na biye mashi fushin nan nashi ne zai wakana a tsakanin mu kwana biyu.
Haka yasa na dan mike jiki ba kwari na nufi dakin shi don bai falo a lokacin dakin shi na nufa na tura da sallama yana ciki zaune ya tasa laptop din shi a gaba yana aiki dashi.
Jin sallama na da yayi ya dago kai ya dan dube ni kadan ya mayar da kan shi ga abinda yake yi a hankali na karaso inda yake zaune nace.
Uncle sannu da aiki kun dawo yau kasha kiriniya da rawan kai wurin su maimu ya ce na kaisu shan iskane da Abba don kin san farin cikin yara shine nawa a yanzu.
Nasan magana ya fada min a fakaice cikin dakewa nace Allah ya raya muna su ta farkin addinin musulunci yace amin kawai ba tare da ya dube ni ba.
Gyara zama nayi da dakyau a kusa dashi na dan dora kaina saman jikin shi ajiyan zuciya naji ya sauke a raina nace su zuciya manya.
An fara sauka ke nan don naji ya sauke ajiyan zuciya karo na farko shiru ba wanda yayi magana a cikin mu har na wani lokaci sai aiki yake yi wanda nake gani sako yake turawa a lokacin.
Gajiya nayi da kwanci haka na na sai na dan juya ina kokarin jawo filo in kwanta sama muryan shi naji yana fadin kin ci abinci kuwa nasha koko nace mashi.
Koko ba abinci bane kin dai ji likita yace ki dinga cin abinda zai gina maki jiki ko yaushe uncle zan ci nace a takaice.
Rufe laptop din yayi ya mike ya fita sai gashi dauke da abinci yazo ya aje a gabana yana fadin oya tashi ga abinci ki ci na kai duban ga abincin .
Sakwara ne da miyan gaye yaji agushi sai manja da tayi amfani dashi da nama manyan yanka da ta saka sai kamshi ke tashi a gabana.
Take naji warin abincin ya nashe ni har amai na son taso min a lokacin amma don dai kawai in farauta mashi rai haka na daure nayi loma biyar da kyat har nayi kusan rabin plate din dake gaba sai dai ban kai ko ina na ba koda ya dawo mayar da kayan abincin ya samay a bayi ina haraswa sosai.
Na galabaita