Showing 156001 words to 159000 words out of 269010 words

Chapter 53 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13320

ba gani nan kamar aiki zai kashe ni yan iskan yara kawai komai basa iya yiwa kansu sai dai ai masu.
Amma kamar naji ana maganan Sulaiman da suka ganin sai sukayi shiru basu san naji abinda suke fadi ba sai dai banji ba sosai kamar suna cewa inba shi ba mai zaiyi da yar kauye ga mata birjit a birni.
Nace nice yar kauyen ke nan ko tace wa yasanar masu yan bakin ciki kawai.
Mun dauki lokaci da ita muna hira ta kashe tana cewa wai ana kiranta don haka mukai sallama tace idan taji wani abu zata kirani.
Ta barni da tunane nace a raina ashe sunzo din Allah ya taimakeni dani ce zan zama masu jakar aiki harda gaiya zasu hada min ga korar karen da sukayi niyar yi min a gidan.
Da dare na yi shirin kwanciya sai ga wayan sulaiman ya shigo min ina dauka naji ya kwashe da dariya yana fadin Allah dai ya sakawa baba da alheri.
Wanan irin halarcin haka aiba kowane zai iya ba zankadedeyar kyauta haka abin yazo min da sauki da na dawo yanzu sai kawai nazo na dauki matata mu tafi.
Nace sai kace amaryan dako yace ai itace don ko baba ya hutar dani ga komai yayi yadda sunna yace ayi saura may kuma ba in daukeki ki tare a gidana ba.
Nace kana fara yi min haka aiko dan walima ka bari muyi don Allah yace kai Safiya bansan baki da tausayi ba .
Allah ya kawo min sauki kina son kuma ki kirkiro wani abu na daban kisa ai walima ko a dakin ki kaso sai ai maki.
Kara marairaicewa nayi nace don Allah uncle kada muyi haka dakai yace kedai zancewa kada muyi haka dake shekarana nawa ina zama gwauro yanzu kuma da aure na zaki mayar dani gwauro da karfi da yaji.
Kunyan zancen nake ji don haka nayi kokarin kawar da zancen da tambayan shi ka fada ma anty kuwa ?
Yace bari nayi sai taji ta kirani zamuyi maganan da ita don yanzu ban shirya abinda zan fada mata ba.
Ajiyan zuciya na sauke nace ashe su anty uwa sun tafi lagos din yau Faiza ke fada min yace itace info dinki a gidan ke nan nace a a magana ne ya kawo ta fada min.
Bayan muyi waya dashi ya sheda min a sati biyu yake son in tare gidan shi don haka na fara shirina da wuri zai dawo next week in Allah ya kaimu.
Bayan na kashe wayan ne na sauke ajiyan zuciya sai yaya Saadu ya fado min a rai don haka na kirashi don in sheda mashi.
Kira biyu ya dauka yana cewa yar halas yanzu muke maganan ki don ga takwaran kinan ta hanamu shakat sai kuka take muna nace subbahanallahi.
Kun bata magani kila cikin ta ke ciwo ina jin yana tambayan Samira ko an bata magani tace bata bata ba.
Ya juyo gareni yace yaya garin kina lafiya yaya logos nace ni ina gida yaya yace kina gida tun yaushe ?
Nace sati daya ke nan lafiya kika je gida yanzun Safiya kodai auren ya tashi ne ban sani ba ?
Nace aure sai dai ayi fatan dacewa da zaman lafiya yanzu yace may kike nufi tukun nace abinda na fada yanzu yaya.
Wai tsaya don Allah da gaske kikeyi ko wasa nace wallahi ko yau baba ya daura min aure daga zuwa tambaya sai daurin aure daya ni.
Yace don Allah ki bari ni ina nan ina cewa ni zan bada ke don asan ba zumuncin wasa ke tsakanin mu ba ashe baba ya rigani.
Nace wallahi yaya ni yanzu duk abin ma ya daure min kai wallahi duk na shiga rudu wallahi ban shirya komai ba yaya.
Yace Allah yasa haka yafi zama muna alheri nace amin yace yaushe ne tarewan naki yanzu nace ban sani ba yaya amma dai naji yace in two weeks yake son in tare.
Yace haka yayi yanzu ki bari zamuyi waya zan kiraki ansan abin yi kafin in zo nace yaya kada kace zaka wahal da kan ka don yace baison inje da ko tsintsiya gidan shi mata ya nema mata za a kai mashi.
Yace ayi haka bari dai mu gani zan kiraki da safe in nayi shawara mukayi sallama ya kashe wayan.
Na sauke ajiyan zuciya tare da kifa wayan nawa ina mai sauke numfashi tare da lumshe idona sai na mike zubur na fada ban daki tare da dauro alwala na fito.
Na dade zaune ina kai kukana ga ubangiji da ya tabbatar min da alheri ga wanan auren ya kawar da duk wani abin ki a gare mu.
Na dauki lokaci mai tsawo a zaune itama ummina tana nata a falo sai kanne na ne ke ta kwasan barcin su hankali kwance na shafa tare da mikewa na nade abin sallah.
Sai naji Ummi tace min kin idar na amsa mata tare da fitowa falon na samay ta na zauna anan.
Take cewa dani gashi dai yau Allah yayi ikon shi kina da aure a kan ki a gidan nan abinda kowa bai zata ba akan ki.
Don haka sai dai muyi fatan Allah yasa ma auren albarka Allah dai yanufa shine mijin ki kece matar shi kada kisa kowa a ranki ita ma wace tayi maki wanan dalilin aure kada ki yarda ki yashe ta komai ritse don ita din ba abin yaddawa bane a gare ki.
Ki manta da komai ku zauna lafiya don alaka ya sake hadaku dama duk wa yan da zaki samu a zurian shi ki zauna lafiya da kowa.
Kin daiga shi abin duniya bai rufe mai idon shi ba to kema ki zama haka na ga yan uwanshi da nasa sai a zauna lafiya.
Yanzu sai mu jira dawowan shi muji yaushe yake son ki tare dakin ki nayi saurin cewa ummi waifa a cikin sati biyu yake son in tare.
Sai naji ummi tace to shike nan mana Allah yakai mu lokacin nace ummi may aka shirya da za a biye mashi don yace cikin sati biyu yake son in tare ?
Tace akwai Allah shi zai hore muna abinda zamu kai masu a matsayin gara bashi kenan ba sai ki tare shike nan sai kuma a jira suna idan muna da sauran kwana.
Cike da jin kunya na sauke kaina kasa ina cewa kai ummi sai tayi dariya tace to may za a jira kuma yanzu bayan wanan sai maman ku ta shiga zuwa reno.
Kunya naji nace kai ummi tin yanzu har an fara wani maganar haihuwa can a dai samu a tare din don dazun Faiza ke fada min wai anty uwa tana lagos gidan anty kan maganan.
Sai naji ummi tace ai basuyi kamar Allah ba don aure ya riga ya dauro a tsakanin ku ko ba kuma zasu iya rabawa ba insha Allahu.
Mun dauki lokaci muna magana kafin mu kwanta barci da safe ma da muka ta shi da maganan muka tashi kuma a dakin mu.
Kiran shi ne ya shigo min na dauka da ladabi ina gaida shi bayan mun gama gaisawa yace Safiya a gidan ku wa kike ganin ta samu kebewa da Nafiu kanina da suka zo.
Gaba na ne ya fadi dam nace a gidan mu kuwa gaskiya ban sani ba don ni ina daki har suka wuce yace ki dai bincika din akwai wace ta fada masu wai.
Rufa rufa za ai min kina da cuta a jikin ki abincika kafin ki tare don kar a cuce ni da sauri nace ba kowa zai min haka ba sai inna .
Yace wacece inna nace dashi maman su yaya Sani don itace kadai zata iya yimin haka don tasha fadawa mutane hakan.
Yace subbahanallahi nan na fara bashi labarin zaman ukuban da nakeyi da ita tun tasowa na a gidan har zuwa yanzu.
Yace ok ita din ce na fada ma hajiya baaba da ta tuntube ni da zance nace ba gaskiya bane sai da mukayi gwaji dake kafin mukai ga matsaya nasan kuma ta gamsu da magana na.
Zan kuma kara yi mata bayani yadda zata fahince ni amma dai wanan matar ko bata da hali mai kyau yace zan gaya wa baba da kaina don ya dauki mataki akan ta kada yan uwa na suzo ta bata auren.
Nan dai ya kwantar min da hankalina muna gama waya na kira ummi na ina fada mata ita kuma bata tsaya ba ta kira mama tana sheda mata abinda ke faruwa.
Mama tace a bari baba ya dawo gidan ai ba kyale ta za a yi ba dole ai mata magana wanan karon.
Basu gama magana ba sai ga baba ya shigo a fusace tun daga kofan gida yake kwadawa inna kira mama tace gayacan ma shigo ko yaji ne ma ?
Inna tafito tana cewa malam wanan kira haka kamar makaho ni har gabana ya fadi ai.
Yace gaban ki ya dade bai tarwatse ba munafukan banza muna fukar wofi kawai ta Allah ba taki ba.
Munafincin ki bai ciba sai ki canza wani kafin ma ki canza badai a gida na bakan don safiya bata tarewa kina gidan.
Fadin haka yasa yaya sani dake bayan shi yana sauraren maganan baba din yace saboda may baba ?
Yace sani wanan uwar taku wani irin hali ke gareta yanzu ace duk halarcin da yarinyar nan take muna agidan nan kaf bata debe kowa ba wai amma Rakiya bata gani.
Sai tabi baya ta yi munafinci akan auren Safiya don ta kumsa muna bakinciki kawai duk a taru a lalace uwa zaune diya zaune a gida kamar yadda take da yar ta a daki.
Yaya sani ya sake fadin may ya faru ne baba may kuma innan ta sake yi ne wai ?
Yace sani wai ka diba ashe zuwan mutanen nan garin nan Rakiya ta sillace jiki ta ja daya daga cikin bakin nan ta fada masu wai ba lafiya ke ga Safiya ba ayi bincike kafin ta tare.
Sai gida ya dauki salati dama kowa ja waje cirko cirko a tsaye ana sauraren baba yaya Nura yace an ko yi haka wallahi dama nayi tunanen in ba wani abin zata fada mai ba don naga lokacin da ta fito suna alwala ta kirashi gefe ni kuma muna shagon musa mai tereda zaune wallahi na ganta.
Kai munafuki da ka ganni sai akace abinda na fada mai kenan ko may yace nidai na gan ku tsaye wallahi ba wani ya fada min ba da idona na ganki inna.
Baba yace yanzu yaron nan ya kirani yana fada min sakon da aka kaima uwarshi gida don haka ban zama da macen da bata son diyana da karuwa a gidan ki tafi gidan ku har, , ,
Yaya Sani ne yace don Allah baba kada ka karasa don Allah sai ya fashe da kuka sauran yaran suka dauki kuka gaba daya.
Ummi tace malam kayi hakkuri ko don yaran nan idan ka sallamay ta yanzu ga Saadatu da ciki ina zata yace inko ban sake ta ba yanzu bata zaka min gida sai safiya ta tare.
Nan dai gida ya dauki kuka kowa da abinda yake fada yafice yabar gidan nace gidan mu gidan danger.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON


🧕🏿5️⃣3️⃣🧕🏿


NOVEL DINA NA KUDI IDAN KIN FITAR MIN ALLAH YABI MIN HAKKINA A KAN KI IDAN KI KARATA BAKI BIYA BA BAN YAFE BA NA FADA NA SAKE FADA A KIYAYYE DON ALLAH DON CIN AMANA BALA,I NE, , , , ,


Shigana daki yayi daidai da shigowan wayan Faiza nayi saurin dauka don nasa magana ya samu ke nan ina dauka tace wai safiya may ya faru ne daga jiya zuwa safe dai surfa maki zaki ake a gidan nan babu kakautawa.
Tace bari dai zan kiraki ina zuwa sai ta kashe wayan nata na bi wayan da kallo kamar shine faiza na bashi amsa da cewa sunji zancen auren ke nan.
Shigowan gwagom Ummi na gidan ne ya dawo da kowa a cikin sai tin shi don ta shigo gidan ne da gudan ta tana fadin ayyurriri amarya Allah ya kawo mu lokaci ya kawo mu yan bakin ciki kunji kunya masu hassada kubi bango ku narke don Saifiya da Sulaiman zama daram.
Su yaya Nura ne ke fadin gwagon ummi gudan bai isa ba sai ta kara fadin ayyurriri Amarya.
Yar shagali yar biyan bukata yar galari , makulin mota ke akaba na kofan daki ke akaba sai yaya Sani ya manna mata kudi a goshi nan ta kasa karasa kirarin nata ta saike guda tana fadin Amarya bakya laifi, ina amaryan take ne.
Sai mama tace a a gwago karkizo ki sa min yarinya kuka fa munyi arziki tunda aka daura aure bata wani bata rai ba.
Gwagon ummi ta juya ta kalli mama tace kuka kuka fa kikace
Yo kukan may ina so kina so sukayi fa kinji ki da wani zancen badai yaran yanzu kuka kan.
Aiko na munafunci basa yi koda kuwa budurwace sun daina kuka tace yo Allah na tuba wanan din ma ai tayi kawaici da watace da yanzu ta kafa muna DJ a gida ta ruda unguwa da gaiyatan shedanu masu hana auren zaman lafiya.
Ummi ce ta fito fuska a daure tana yiwa gwagon sannu da zuwa ta bi yar dan uwan nata da kallo tana amsa gaisuwa nan tabar mama da sauran yara tsaye ta nufi dakin umin nawa.
Kara gaisawa sukayi ta kasa daurewa tana tambayanta make faruwa ne naga ranan farin ciki a gare ki gashi kuma kin bi fuskan ki duk kin daure ?
Ummi bata iya yin magana ba sai hawayen dake zubo mata sai nice nayi karfin halin fito ina cewa gwago an shigo tace a a kina ciki dama ?
Nace na kwanta ne dama tace may ya samu uwar taki ne haka kuma ranan farin ciki a gare ta gata tana kuka kuma ?
Nace ba wani ubu bane zancen Inna ne dai shine takema bacin rai ,
Innan taku tayi wani abune mara kyau ne kuma nace gwago takan rasa ne ai mai hali baya barin halin shi.
Zuwa tayi ta fadama ma dagin mijin antyn mu wai suyi bincike anty mu na da cuta a jikin ta amai rufarufa ne don acuce shi.
Salati gwagon ta saka tun kafin taji karshen maganan tana fadin amma dai anyi yar banza mata anan .
Da ita nufinta haka za a hada auren bai san halin da take ciki ba to mu bamu da gadon sheri a tare damu.
Yanzu may ake ciki tana sake tambayan Aisha kauna na don ta san ni da ummi ba zata gane komai a wurin mu.
Aishan tayi mata bayanin komai yadda zata fahinta tace hakan da malam din yayi yana da kyau tunda dai Rakiya bata da niyar gyaran halinta.
Nace ni gwago na rasa mai nayi wa inna a duniya tun ina karama bata kauna na haka.
Tace bazata ko kaunace ki ba don indan kika ga mutum da yafaye wanan halin yaje bakar bincike binciken ta an fada mata abinda ya tayar mata da hankali shi ne abin yake wahal da ita haka.
Kin san wasu basu da dogaro gun Allah da zaran kishiyar su ta samu ciki zasu je a bincika masu mai zata haifa da sauri nace kai haba gwago tace Allah sarki ai wanan abin abu ne da ya kewaye birni da kauye don ko ina akwai marasa imani.
To duk yadda akayi irin haka ne ke damun Rakiya taje an mata buncike an fada kata cewa abinda zaki haifa na da arziki sai ta ce a jefo mao kaddara da karshe kuma ba mai iya hana ikon Allah sai kaddaran ya juye Alheri ga bawa.
Shiru mukayi muna sauraren gwago da al,ajabin abinda take fada muna tace don yanzu an daina wasu abu saboda wayewan kai da mutane suka samu.
Amma har gobe a kwai masuyin zagon kasa don su basu bar gida ba don haka yake da kyau mutum ya nema wa kansa rigakafi tun kan rana ya baci.
Don haka kema yanzu ki saurare ni don zaki tafi cikin bakin fuska da baki san su ba baki san halin su ba .
Don haka zan baki makarin kwarce ko wani zai maki ba zai kamaki ba murshi nayi a raina nace kai gwago ho.
Zaki samu kwai na zabo guda ukku sai ki samu kayan aduwa 99 a hada su da kwanzaben nan a dafa sai ki hada bawan kwan da kayan aduwa a dakesu adinga zubawa a kunu anasha.
Maganin walwale turbuda shine turbuda kuma idan kina zargin wani na maki asiri shine,
Zaki samu ruwan tsami ko ruwan tsami da ganyen zogala wanda aka shuka iyankan gona sai ki jika da kai kayi koma kan mashekiya ki hada da ruwan tsamin da zogalan na iyakar gona kiyi wanka ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login