Showing 246001 words to 249000 words out of 269010 words
yake mata tambayoyi tana bashi amsa duk muna sauraron su yace ke ma kina da laifi wallahi.
May yasa dayace ki bashi kudi shi baki mayar mashi ba tun abin baiyi maku nisa haka ba tace sjerin shedan ne kawai ya kawo haka.
Yace ga tanan tun lokacin da muka ji zancen take bina akan in sa baki tace ban son shiga tsakanin miji da mata ne ban kula mata ba da tun tuni nayi magana akai.
Juyawa tayi ta dan kalle ni sai ta sadda kanta kasa tace nasan nayi kuskure babba a kanki safiya sherin shedan ne dana hajiya uwa da take zugani a kan ki.
To yanzu bari in kirashi inji ta bakin ki uncle yace yana lalubo wayan shi a cikin aljihu yake fadin wani yasan kin zo nan ne da zaki zo tace ba wanda na fadawa zanzo nan din.
Neman layin shi yayi kira biyu a na uku ya dauka yana fadin kadawo kenan tunda naga nomban Nigeria yace two weeks kenan da dawowa na ai na yi rashin lafiya ne dashi na dawo shiyasa baka jini ba.
Yayi mai jajen jikin yace ai bansan cewa kana kasan ba wallahi yace yana na sai dai wani magana nakeji mara dadi yana faru ?
Dariya yayi kamar a fili yake kusa damu yace may kaji kuma yace maganan ku da madam gaskiya brother banji dadin hakan ba sosai .
Daddy yace to yaya za a daurowa ne abin maimuna ta ishe ni dan uwa uncle yace dakata yaya aure ba a cewa haka abune da akeyi da fatan har mutuwa amma ba daga dan magana kadan ace rabuwa ba.
Yace na sani Sulaiman amma yanzu banjin zan iya mayar da ita gida na doni aure zanyi very soon taje ita ma ta samu wani a a dan uwa hakkuri dai zaka yi zan cen maganan auren nan don Allah kabar shi.
Sai daddy yayi murmushi wanda har muke iya jin shi yace ai magana har yai nisa yace to ni nace ka fasa tace har yanzu baka san wace zaka auro wa kan ka ba ne da bakayi ba.
Don nayi bincike a kanta bada da record mai kyau sam wallahi yace uwa fa ta sama min ita kuma ta yarda da natsuwan ta anty ta daga hannu alaman kinji ko nima da baki nayi magana irin ta kuramay nace ah tare da rike habana da mamaki.
Uncle yace kasan ba zan cuce ka ba don Allah ka janye maganan nan kayi hakuri madam ta koma dakin ta kuyi hakkuri da juna please ?
Yace to shike nan don kasa baki ne amma ka ganta ka ja mata kunne idan zata ji maganan ka don yanzu ban daukan iri halayen nan nata.
Yace insha Allahu nan dai ya gaya mashi irin halaiyan su hajiya uwa da abinda suke aikatawa a gari yace shine take son rabaka da matar ka ta hada ka da balai ko ?
Sun dan jima suna magana uncle ya kashe wayan bayan sunyi sallama da junan su ya juya wurinta yana fadin uwa yar iskan matace na sani ba yau ba shiya kika ga sam ban dauki maganan ta ko kadan da muhin manci ba don nasan kowaye uwa.
Tana share hawaye tace ni kaina nakan yi mamakin yadda tazo daga baya ta shige min jiki duk da yana fada akan in rabu da ita amma banji ba.
Ya mike yana fsdin shi zai koma sai gobe ne zaki tafi ko tace wai da yau nace zan koma yace yau kan ai dare yayi yaushe zaki isa bauchi a wanan lokacin ki bari gobe sai ki koma.
Ya fita nace ta taso ta shiga daki wani dakin na bude yana a gyara dama don baki irin haka muka gyara shi nan na sauke ta na fita na kawo mata abin bukata a dakin .
Sallah tayi na kawo mata wani dogon riga da nake ganin zai mata nace ta canza kayan jikin ta na juya zan fita daga dakin tace safiya sai na juyo da sauri.
Ganin taba da magana yasani dawo wa inda take na samu bakin gado na zauna ina sauraren abinda zata fadi a lokacin.
Tace nasan nayi maki ba daidai ba a cikin zaman mu amma duk da haka ke kina bina da alheri har yanzu banta dana sanin rabuwa dake a rayuwana ba sai yanzu da na shiga wanan halin.
Uwa ta cuce ni safiya ta cuci rayuwana wanda nasan ba banza ta barni ba a yanzu da nake tuna irin yaudara na da taitayi ita da diya ta da sunan zasu taimaka min.
Ashe ha,inta na sukeyi ban sani ba ni na dauka so ne ance ka samu dangin miji ka rike mutum guda a ciki shine na riketa ashe ita bada zuciya daya take zaune dani ba.
Ni dai hakkuri nake bata kawai don ban ma san may zance da ita ba a wanan lokacin sai bata hakkuri nake kawai dakin su mummy na shiga don in duba su.
Yaran suna kallo nace mummy kuna ciki ne tace eh ai dazun zan fito naga kuna da bakuwa bakuwa kukayi ne a gidan nace eh mummy anty ce tazo.
Wata anty ta tambaya cikin son sani ko wanake nufi nace anty na da nayi zama a wurinta lagos itace tazo dazun .
Allah sarki ashe da rabin zan santa bata taba zuwa ba nake gani ai nace ko yanzu ma ba zuwan lafiya tayi ba na zauna ina bata labarin abinda ke faruwa.
Sai dana gama fada mata tace ikon Allah haka abin Allah yake fa gashi tun ba a je ko ina ba Allah ya fitar maki da hakkin ki baki da Alhakin ta ke nan.
Ai wanan zamanin ana abu wallahi da karfi da yaji akeson tubbuke ka a gidan auren ka don kawai wani ta shiga ko idan shi yashiga alhaki zai barshi ya zauna ne shi ?
Mata kyashi da hassada yayi muna yawa yanzu sai kiga ko da yan uwa na jini da nine yanzu suna kyashin junan tun dai idan an ga daya ya dara daya sai hassada yazo ya shiga tsakani.
Ke dai fita batun yan duniya ki rungumi mijin ki tunda bai raga ki da komai ba na bukata kuyi zaman ku lafiya ba fita kike yi balle ki ga wani abun a kan shi.
Shine amfanin zama guri daya yau idan baka kula mutane ka huta ma rayuwan ka sai zuciyar ka ta zauna lafiya da kowa ba abinda ya damay ka.
Amma kinga yawan kwashe kwashen na babu abinda bai haifarwa shi nake guje wa mutumiyar ki ai kullun ina kan bakina da ita samira bata san ciwo kan ta ba wallahi.
Nace mummy may tayi kuma tace waya san iyaka yar nan gashi yanzu yar uwanta ke fadin dawowan nan danayi tace wai sabbin abaikai tayi ko yaushe idan su basu zo ba ta taje wirin su.
Kinga ai irin haka mutum ke gudu wa rayuwanshi don ba a gane mugu a goshi tunda ba zuciyar mutane ake gani ba wanan abin na yarinyar nan yana damu na wallahi.
Nace ni mummy sai yanzu nake ganun fa,idar barina in fita da uncle bai yawan yi koma wani wuri zan tafi in ba wurin Aisha ko samira zan tafi sai dai mu fita tare sai kuma idan wani abu zan fita in sawo mai muhinmanci a gare ni.
Mun dauki lokaci muna hira da ita nafito daga dakin don magariba ya kawo jiki a lokacin don haka na fito don zuwa sallah.
Ko da uncle ya dawo da dare tafito sun dan taba hira dashi ta koma daki ni dai sai haba haba nakeyi da ita a gidan in samu mu rabu lafiya ina mai kara bata hakkuri.
Washe gari ta wuce da safe tana matukar bani tausayi tace don Allah in kara yiwa uncle magana akan zancen nace insha Allahu anty zanyi bayan tafiyan ta muka zauna nan da mummy a falo muna hira.
Duk jikina yayi sanyi wai yau anty ne take kumsan bakin cikin da na miji a kanta matar da suke gwanin ban sha,awa agidan su ita da mijin ta da yayan ta a gida har damu da mu kaje cin arziki a gidan.
Yau sai gashi wai sun samu sabanin mai muni a tsakanin su dole mata mu rika taka tsamtsam da maje komai dadewan mu a gidan miji.
Haka rayuwa ke guda yau dadi gobe madaci ga bawa watarana kuma a dara uncle yayi kokari ya mayar da anty dakin ta tare da basu hakkuri daga ita har daddy din.
Haka yasa anty uwa da kawar ta suga shiga tashin hankali don komai sunyi na shirin buki a lokaci da bincike da komai suka gano uncle ne yayi sanadin komawan anty gidan daddy din.
Haka yasa suka niko gari zuwa gidan namu uncle ya shawo kan daddy ya yarda a tsayar da zancen auren su da sahura.
Muna zaune a falo duk da safiya ne amma hakan baisa sun shigo sun samay muda shirin mu a gidan bamu da wani makusa sai kanshi ke tashi yana kwance saman dogon kujera don ranan babu aiki.
Abba yana saman jikin shi yana mai wasa sai ni dasu maimu dake zaune muna mashi hiran shirmay su don yace zai saka su islamiya shine suke biya inda suke.
Sallaman su mukaji daga sama shigowa falon gidan kai tsaye da mamaki nake kallon su don shi yana kwance a lokacin.
Baiga fuskokin su ba sai dai yana kokarin mikewa zaune a lokacin gane su da yayi yasa ya daure fuskan shi yana cewa uwa kune tafe ?
Tace eh gamu mun shigo yau ziyara sannu ku dazuwa kawai nace dasu ban kara bita kan su ba kuma ban bar wurin ba sai cewa dani dasu hindu su shige ciki.
Ban kuma mike zuwa dauko masu abinsha ba na zauna tare da harde hannuwana wuri guda jikina yana gugan na shi a yanayin zaman da muka dashi.
Bayan su gaisa dashi anty uwa ta dan dube ni tace don Allah bamu wuri magana mukazo yi dashi kallon ta nayi na cewa ni tare da nuna kai na ?
Tace eh magana ya kawo mu wirin shi mukazo kafin ince wani abu don yau nayi niyar mata rashin mutunci sosai sai naji uncle yace da ita.
A, a bakizo ganina bakan duk abinda zaki fada min idan baki iya fada a gaban matana ai ba alheri ya kawo ki ba ke nan.
So idan kinyi niyar gani na ba idan zata tafi don gidan ta kika shigo kinga ko baki da right din cewa ta baki wuri ki fadi maganan ki kai tsaye kawai naji.
Don ni mata itace abokiyar rayuwa abokiyar shawarana gaba daya don ko kin fada a bayan ta ma fada mata zanyi tsab.
Nisawa tayi tace dama bawani abu ya kawo mu ba sai zancen yayana da kawana sahura gata har an saka lokacin aure yanzu kuma yace wai ya fasa komawar wanan macuciyar matar tashi da ta shiga ta fi, , , ,
Dakata uwa don Allah ban son sha shanci kin sani ke har zaki iya dauko kafa kizo min gida da wanan zancen naku na banza .
Yanzu don baku da kunya kuke kokari shiga tsakanin mijin da matan da suka shafe sheru goma sha wani abu da aure kina kokarin cusa mashi wata bare can.
To bari kiji ban cikin wanan magana naki na hauka kuma aure yaya ba zai taba kara aure ba muddin maimuna na gidan nan.
Tashi tayi da fushi tana fadin don munzo wurin ka neman taimakon bawai yana nufin munzo roko ko maula ba balle kayi kokarin fada min magana haka ?
Dole yasa ka ga mun zo wurin ka don kawai ka dafa muna ba wai wani abu ba yace oho gani mahaukacin daure kun kwaso kafan ku kunzo a hada kai ayi cuta to ban iya ba ku bace min da ga tun raina bai baci ba na kira maki yan sanda yanzu.
Sai da ta watsa min hara nima na mayar mata daga inda nake zaune ta fita fuuuuu sauran suna biye da ita a baya.
Yaci gaba da fada a falon yana fadin wanan matar tana da hankali kuwa ko abin nata ya zama hauka ne wai ?
Naji dadi sosai har cikin raina yadda uncle bai raga masu ba ya kore su ya kira wayan daddy yana fada mashi abinda ke faruwa a gidan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/21/20, 9:58 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , , , ,
🧕🏿8️⃣3️⃣🧕
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Haka rayuwan mu yaci gaba da tafiya a gidan muna samun kula yadda ya dace daga wurin uncle har yasa yan kanne na wani school mai tsada a nan cikin Abuja.
Sa su makaranta yasa yanzu ina fita in kai su in kuma je hudu in dauko su in sun shirya nakaisu islamiya ranan da ban iya fita kuma sai driver ya dauko su daga school din.
Yau haka na kwana ba lafiya a jikina sai karfin halin da nakeyi ban son asan halin da nake ciki a gidan sai dai jikin ya matsa min har ban iya boyewa mutane halin da nake ciki.
Wanda ya saukar min da zazzabi zuwa rana mai karfi har yakaini da rufuwa da bargo da kyat barci ya dauke ni cikin zafin jiki nake barcin a wahale a lokacin.
Jina shiru ban fito ba tun safe da na sauke yara makaranta yasa mummy lekowa dakina ta duba ni ganina kwance na rufe da bargo har kaina yasa ta shigo tana fadin .
Safiya yau lafiya kike kuwa abinda ya falko dani daga barcin dana dan samu ke nan na bude idona dakyat nace.
Mummy ban jin dadin jikina ne yau tun dare zazzabi ya rufeni sai da nasha magani ya lafa yanzun kuma ya kara dawowa.
Ina gyara kwanci nace karfe nawa yanzu mummy tace uku da rabi ya wuce dan yunkurawa nayi ina son in dauko waya amma na kasa.
Sai mummy ta gane abinda nake son yi tazo da sauri ta dauko min wayan ta mika min neman layin uncle nayi don in fada mai a dauko min su maimu daga school .
Jin murya na yasa shi fadin may ya samay ki safiya ?
Banda lafiya na iya fadi kawai sai naji ya kashe wayan da sauri na gyara kwanciya nayi don ko sallah ban iya yiba a lokacin.
Ba afi wasu mintina ba sai gashi gidan yacewa malam musa yaje ya dauko yaran daga school ya dawo yanzu ya juya ya fita daga gidan kamar yadda ya umurce shi dayi din.
Ciki ya shigo bayan ya sallami malam musa din dakina ya nufo don yafi tsamanin ina can din a lokaci ya turo kofan da sauri.
A kwance ya hangoni kwance na dunkule a wuri daya ina makarkyatan dari duk jikina rawa yake a lokacin .
Bargon dana rufe jikina ya kwarai tare da dan taba jikina a hankali zafi yaji radau a jikin nawa jin hannun shi a jikin nawa yasa na bude ido na hanshi zaune a kusa dani yace .
Safiya baki da lafiya ne har haka baki fada min ba kuma baki kirani ba take ya daga waya ya kira likitan shi yace yana wani wuri amma gashi nan zuwa yanzu.
Yana dakin har likitan ya shigo gida fita yayi sai gasu sun shigo tare da likita dakina ya ce madam sannu yaya jikin ?
Nace da sauki ina takurewa a wuri daya yace yaya nake ji ne ?
Nan na fada mai yau kwana hudu da amai amai ya fara min sai kuma daren jiya ya saukar min da zazzabi .
Yayi min yan tambayo na bashi amsa uncle na zaune ya kafeni da idanuwan shi sai yace bari ya fara saukar min da zazzabin gobe zai dawo akwai awon da zai min.
Wani irin ras ras naji gabana ya bada don ambatan awon da yace na dauka akan maysalan ciwon mu zai mun awo din na yaba allura har biyu tare da magani.
Suka fita da uncle daidai lokacin yan makaranta suka dawo dakina suka shigo don tun a hanya malam musa ya fada masu banda lafiya shiyasa banzo daukan su ba.
Don su fison in tafi dauko su don duk abinda suka gani na marmari a hanya sukan ce min insaya masu ko kuma in tambaye su asai maku abu kaza ne ?
Gaishe ni sukeyi kowa tana kokarin ganin fuskana kamar an fada masu a fuska na ciwo dake damu na yake min.
Dan samun saukin da nayi na rarafa naje ban daki na dauro alwala nazo na tayar da sallah don har da azahar banyi ba ina kwance.
Ina sallah naji shigowan uncle dakin bai fita ba don ina sallah zama yayi har lokacin da na idar da sallah din ya miko min maganin da likita ya rubuta mai ashe shine ya fita sawowa.
Nan ya tsaya sai da na