Showing 147001 words to 150000 words out of 269010 words

Chapter 50 - Bahagon Rayuwa By Makawa

04 Dec 2025

13339

cikin tunane fiye da musali saboda bai taba tunanen haka ba da tun farko in yasan za a samu wanan matsalan ba zai tsaya har muyi nisa haka ba
Amma a fili cewa yayi dani come on ba nace ki manta da komai ba kiyi kamar bakiji komai dake gudana ba, idan na zo zan maki bayani yadda zaki fahinci abin
Ko kinfi son ki tadda min da hankali anan har in kasa yin aiki aiwatar da ayyukan dake gaba anan.
Shiru nayi ina sauraren maganan shi karshe na kashe waya ina mai bin lafiyan gado na tunane kuma yazo ya lulube a wirin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , ,


🧕🏿5️⃣0️⃣🧕🏿


NOVEL DINA NA KUDI NE NA FADA MAKI TUN FARKO INDAN KIN FITAR BAN YAFE MAKI BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA ALLAH YA ISAR MIN.


Yanzu ni yar uwa may zace dake tunda tun farko na fada maki kada ki fitar min ai kadan kika gani ga wanda bai tsoran Allah .
Nace tun farko kada ki fitar min da novel kin dauka kalman Allah ya isa wasa ne sai da abu ya cika dake zaki dawo kina na yafe maki.
Baki san ni ba baki kuma san inda na fito ba ina dai novel kina karantawa nace ga yadda nake son abina baji ba yanzu kizo min da wani magana ban damu ba tunda tun farko na fitar maku da hakkina na fada maku ban son a fitar min ke da sauran kadan kuka gani muje zuwa indai nice kullun ya diga bibiyar ki ke nan ai tunda kin zabi kalman Allah ya isa to ya isar min din sai may kuma ni na gama magana na ai tun shekaran jiya ku kaka rage da raddin ubangiji kuma.
Tun safe ban tashi ba ina kwance kamar mara lafiya nake jin kaina ko abinci bam iya fita na nemo ba din ban majin cin komai a raina.
Dawowan su anty da yara danaji hayaniyar su yasa ni mikewa na shiga ban daki wanka nayi na fito na shirya don ina fashin sallah a lokacin.
Bayan na gama shiri ne na nufi part din anty don in mata sannu da zuwa a hankali nake hawa steps din na kawo daidai window din ta dake bude naji ta ambaci suna na har zan wuce sai na tsamaci ita da wani ne a dakin sai daga baya na gane waya takeyi ashe.
Naji ta sake fadin anty uwa na fada maki na Safiya mai sauki ne nasan abinda zan fada mata gamay da sulaiman din ta fahince ni.
Shidai sulaiman din ne yanzu shawo kanshi abune mawuyaci da sauki don ban taba zaton zai mutu ga son yarinyar ba haka.
Shiru tayi tana sauraren maganan anty uwa din sai naji tace gaskiya anty ni safiya bata taba yi min komai ba harda zan mata korar kare a gidana.
Don yarinya nada hali mai kyau wallahi don duk tafi min wayan nan kattan bazan dana tara Fati da Faiza.
Ke dai ki bari mubi abin sannu dan Allah a samu a rabu lafiya da ita ba tare da ta fahinci komai ba.
Anty uwan ke magana ta tsaya tana sauraren ta sai naji tace ba haka bane Anty uwa wallahi wallahi sam ban kawo Nafisa a raina in ba don kinyi magana ba yanzu ai mai sauki ne tunda ba aure aka daura masu ba dashi.
Anty uwa din ke magana sai naji anty tace gaskiya ne zaman ta haka a gida kan baida amfana gaskiya zan san duk yadda zan yi ya koma ga Nafisan batare da an samu matsala ba.
Shiru tayi anty uwana magana sai naji anty din tace Safiya bata da matsala zan san yadda na raba ta da son shi ai don ba wani wayewa tayi ba sosai.
Naji tace to sai kin shigo din next week ina expecting din zuwan ku din ai kafin nan ma tun yanzu na fara aiwatar da shirina a kan su ko may tace mata naji tace ba hakana bane Allah anty yarinya ta bani tausayi ne don wahalan da tasha tun farko a gidan mijin ta.
Anty uwa din ke magana ta tsaya sauraren ta alokacin na yo baya baya tare da dafe bakina dake shirin sake kuka asirina ya tuno gaida ita da banyi ba ke nan na dawo daki na.
Sai ranan naga amfanin rashin zaman da su fati basuyi a falo don ko yau yai min rana sosai inba don haka ba da wani yana iya ganina a cikin su.
Ina shiga daki na rufe tare da fadawa kan gado na sake kuka mai tsuma zuciyan mai saurare na ina kiran sunan Allah da karfi nace ni Safiya wanan irin bahagon rayuwa da nake gani damay yai kama haka duka duka shekarana 21 amma gashi ina ta haduwa da kaddarorin rayuwan duniya.
Yanzu idan sulaiman ya kubbace min ina zan sa kaina ko sherin inna ya isheni a gidan mu ai da mutanen garin.
Zuciyana taban amsa da fadin ki rike Allah don yana sane dake mai hakkuri baya tabewa a duniya.
Haka yasa naji wani kwarin gwaiwa yazo min sai na dakatar da kukan da nake yi ina neman wa kaina mafita zancen tunane na ya tsaya akan in bar gida kawai shi mafita gare ni.
Ban tsaya yin wani shawara ba na mike na fara hada kayana a cikin trolleys dina sai da na shake su da kayan da anty da sulaiman sukai min guda biyu na saka sauran komatse na a baccon da na dawo dashi daga kalaba.
Komawa nayi na zauna a bakin gado ina tunanen abinda zan fadawa anty idan zan tafi don na fasa gudun da nayi niyar yi kada su dora min sata banji ban gani ba tunda mafita suke nema a kaina dama.
Ina nan zaune har yamma yayi min sai na fito falo don dama ina jin motsin su a falon ta kalloni fuska sake tana cewa dani ina kika shiga tun dazun muka dawo.
Nace wallahi barci ya kwashe ni daga dan kwantawa in huta sai na dauki lokaci ina barci Faiza dake gefen ta zaune tace ai da banji motsin ki ba nayi tunanen haka.
Tambayan da anty ta jefomin ya hana ni magana tace kun ko yi waya da Sulaiman yau Safiya ?
Sai na samu kaina da yi mata karya da cewa bai kirani ba anty tace nima haka kwanan nan akwai tsiyan da yake ji wata kila yaji wani magana ne yake son ya ja baya kuma.
Murmushi nayi nace in haka yafi alheri a gare mu Allah ya kawo muna saukin rabuwa tace nima shina gani dama can ba son aure yake yi ba da ayi yazo ya kawo muna wani matsala gara tun wuri dai a watse.
Nuna mata nayi maganan bai damay ni ba naci gaba da harkana tai shiru ta shiga dogon tunane sai can security din su ya shigo yace tana da baki a waje.
Ganin ta tashi yasa muka watse wurin kowa ya shige dakin shi kofana na rufo don magariba yayi a lokacin gashi kuma ina fashin sallah don haka sai na jawo tasbahana ina ja kwai.
Kiranshi ne ya shigo min na dauka a sanyaye da sallama na yayi saurin cewa dani yaya kuma naji muryan ki kamar baki da lafiya ne ?
Kodai zancen jiya kika sa a ranki yake damun ki kuka ne ya zo min shiru yayi yana saurare na tun yana fadin subbahanallahi har ya kyale ni ina tayin kukan.
Sai naji ya kashe wayan bai fi minti talatin ba ya kara kirana na dauka yace look ki tsaya ki saurare ni ban son wanan kukan da kike yi kamar ance za a kwace maki ni.
Murmushin dole yasani yi nace uncle ba haka na bane yace to yaya ne kin bi duk kin tayar min da hankali har jirgi nace a bincika min da daren nan saboda rudani da kikayi ba a samu ba.
Nace cikin dan kuka Uncle gida nake son wuce wa gobe in Allah ya kaimu da sauri naji yace saboda may zaki koma gida gobe shiru nayi kawai ina sauraren shi.
Sai da ya gama cikin kuka na fara fada mai abinda naji anty da yar uwar mijinta suna tataunawa a kaina.
Yace oho dama nufin su ke nan shiyasa tace min ba sona kikeyi ba don dan uwan tsohonijin ki dake kalaba ke kike so.
Watau gani mutumin banza zasu gara ni yadda suke so ki saurare ni kiji ni zan tsara yadda zakiyi tafiyan gobe zan kiraki in sanar dake yadda mukayi da ita kafin goben kada ki kashe wayan ki kinji ko na amsa da eh.
Naci gaba da tunanen zancen nace a raina watau anty uwa ita keson anty ta hada diyarta da Sulaiman shine suke son raba mu.
Nasan anty uwa tun zuwan mu Abuja bude company sulaiman din da mukaje yi wata yar bariki ne don idon ta ya bude sosai don ko shigan da tayi a wurin sai da nayi tir da ita da diya ta wai ita wayewa ke nan.
Yaran ta mata uku tazo dasu wajen biyu sun yi aure amma sun fito ita kuma babban ko auren batayi ba zata kai shekara talatin kila .
Itace ke nan ake son a hada ta da sulaiman nace to ke nan itama din victims ce na HIV komay don naji sunce a huta da ita.
Ban yi barci ba zuwa goma da rabi naji ya kirani yace gobe zaki kibi jirgin safe karfe bakwai za a kaiki airport na fada mata jikin baban ku ne ya tashi aka kirani kuma ina son ki koma gida har yadda hali yayi.
Ta amice don naji tace abin ma yazo da sauki don haka idan ta tambaye ki ki fada mata yadda na fada maki din nayi mashi godiya mukai sallama na kashe wayan.
Muna gama waya dashi na bi gado na lafe kamar ina barci sai gashi an turo kofan ddakin naji tana cewa kin yi barci ne Safiya ?
Na dago da sauri ina fadin yanzu na falka tun tara barci ya dauke ni daga karatu a waya na yanzu fitsari ya taddani ta samu wuri ta zauna tana cewa mutumin ya kiraki ne nace bai kirani ba anty.
Tace yanzu na samu wayan shi wai an bugo mai daga gidan ku mahaifin ki jikin shi ya tashi don haka gobe ki shirya kije gida.
Rudewa nayi ina salati tace ki kwantar da hankalin ki nace shine basu kirani ba anty tace ai sun kiraki wai basu samay ki bane tace ai nima nayi mashi wanan tambayan.
Ta mike tana cewa sai ki shirya goben karfe bakwai jirgi zai tashi yace a sayo maki ticket yau da daren nan za a kawo muna.
Ta fara tafiya sai ta juyo tace dani ina ganin zaki dauki lokaci a can don haka ki debi kaya masu yawa da zasu isheki zama nace cikin rudewa tau anty.
Tana fita na daga hannu sama inayiwa Allah godiya da ya bani mafita da saurin tun ban wulakanta ba a gare su.
Karfe shida na gama komai ban bar komai na wa ba a gidan don nasan ko na bari ba a amfani dashi katshen ta yarwa zasuyi ko su kona.
Security ya gama samin kaya a mota Faiza ce da tayo min rakiya take fadin wanan uban kaya da kika kwasa haka safiya kamar wacce bata dawo wa.
Nace zan rage kayan ne shiyasa na kwasa don in bawa mutane can a gida tace haka na da kyau kuma.
Anty dake bayan mu saye da hijjabi tace Allah dai ya kaddara saduwan mu da alheri ki gaishe sai munyi waya inji saukar ki da lafiyan baban tana magana da gani tana cikin bacin rai.
Na tako gaban ta nace anty na gode Allah ya saka da alheri ki yafe min zaman da mukayi tare idan na saba maki ki gafarce ni anty nace wa Faiza ma haka tare da yi masu sallama na shiga mota ta rufe.
Motar na fita na lumshe idona hawaye na zuba min ji nake kamar ba zamu sake haduwa ba daga nan.
Ita ko anty tun barina gidan sai maganana ya tsaya mata a rai hartayi wanka tana tunanen zancen mu da nace duk abinda nayi mata ta yafe mun.
Tana shirya wa dakina tayo bude ta shiga kallon gadon tayi dana gyara kafin in wuce tace badai tsabta ba safiya tawuce wurin wardrobe dina ta bude sai wayam babu komai a ciki sai zanin gado dana bari nasu.
Da sauri gaban ta ya fadi tace kardai yarinyar nan ta fahince ni ne ko may nake plain a kanta da sauri ta dauki wayan ta tana kiran driver ya dauka tace bani Safiya yace ai jirgin su ya daga gani hanya dawowa gida.
Zama tayi saman gadon tana magana ita kadai tace sam bata ji ba sai dai idan yadda tace ne zata rage kayan a gida.
Da wanan tunanen ta mike ta bar dakin zuciyar ta fam da tunane a ranta tana fadin haka ma yafi sauki da sai anty uwa ta zo suyi mata korar kare a gidan gashi ba mutunci je da su ba.
Tun da muka daga babu abin da nake tunane banda zama na da ita tun farkon haduwan mu da tazo tana tamnayan ko nan ake kitso wata yar wajen aikin su ce tai mata kwatance dani nakai kallo na ga ayan tagwayen ta nace nan ne anty gashi kuma yamma yayi tace ko yaran nayiwa don gobe monday nace to su zauna sai na sake kan wace nakewa kitso na shiga na dauko ma yaran abin sha na kawo masu.
Matar dake zaune tace na nuna masu banbanci su da suka dade da zama ko ruwa ban basu ba sai wanan da tazo yanzu.
Nace ai Sister dina ce ita dole in karrama su naga masu kitson harda ita kuma naki karban kudin lokacin ne Ahmed ya dawo tana jin fadan da yake min akan na tsaya kitso har dare .
Da na fito take tambyana mijinane na bata amsa a sanyayye da eh tace shine yake maki fada akan neman kudi tun wanan rana mu ka saba da ita.
Gashi yau wani matsala ya gitta a tsakanin mu har yana son raba mu da ita lumshe idanuwa na nayi ina mai ci gaba da fitar da hawaye.
Bamu dade ba muka iso abuja da sanyin safiya sai ka dauka a nan muka kwana shida kan shi yazo dauka na yana saye cikin suit irin na maza farare kayan sunyi matukar karban jikin shi sosai.
An gama sa min kaya a mota ya bude min na shiga sai lokacin yayi min magana naji yace ta gudu an iso lafiya ?
A jiyan zuciya na sauke na amsa da lafiya lau yace kin sa mun yi wa baba karyan ciwo Allah ya kara mai lafiya nace amin na gode.
Yace ina mamakin mutane yanzu son kai sai yasa mutum yayi abinda ba halin shi ba sam na rasa gane yaya akayi madam ta yarda wanan matar tayi convices din ta haka.
Hauka nakeyi ko matsuwa nayi da yin aure ai ba zan taba auren Nafisa ba a rayuwa na bayan ta gama watsewar ta a titi ace za a dauko a kawo min gida na barin ga iya gudin su ai.
Get din gidan aka bude ya shiga da mota ni dai ban yi magana ba har lokacin yace ki huta driver yana zuwa yanzu zaku tafi.
Muka fito daga cikin motar shi yayi min jagora zuwa cikin gidan a falo nan muka zube dukkan mu yace yanzu dai hankalin ki ya kwata ko kin gudo wurin antyn ki.
Murmushi nayi ina gyara gyalen kaina nace abin ne ba dadi ni tsoro na kada anty uwa su zo su samay ni a gidan don ban san abinda zasuyi min ba.
May zasu yi maki kuwa banda suyi haukan su su wuce ai ita madam tana da hankali nace haka dai yafi mun an rabu lafiya gida zan koma gidan mu ya fiye min komai zan zauna har ranan da Allah zai kawo min dauki.
Dariya yayi yana mikewa yace ko kin zo ke nan sai in bugawa baba a daura muna aure ke kin tare ko da sauri nace hai uncle abin kuma yar zolaya ne ?
Yace Allah ba wani abu bane ai sai kawai a dauro aure ke kin riga kin tare nace ba aikaina za a fara ba ni dai driver bai iso bane mu kama hanya.
Yace amma dai kya bari ki karya ko ga table can an hada muna tashi ki yi breakfast ki huta sai ku wuce.
Nace ban jin cin abinci ne Uncle yace kina wasa ne maza tashi kici abinci ko in hanaki tafiya yau da sauri na mike ban ci wani abin kirki ba sai dai na dan taba kadan sai ga driver ya shigo yana gaida shi.
Nima gaida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login