Showing 60001 words to 63000 words out of 269010 words
gida in an yi magana kice babu komai.
Ban mussaba na yunkura na tashi daki na shiga na dauko hijjab dina na fito ya kulle gidan muka wuce chemist din da yace.
Sai daya bata lokaci sosai yana dudubani don har fitsari yasa nayi ya auna ni ga dan karen tambayoyi da yake min har na gaji da amsawa daga karshe dai ya bashi tabbacin ina da ciki wata hudu da kwanaki.
Ya bani magunguna da zanyi amfani dasu don taimaka min wurin rage aman da nakeyi don acewa mai chemist din yawan kakarin da nakeyi yasa cikina kullewa .
Amma ba ciwo bane mai tsanani don haka mu kwantar da hankali mu tunda ya fara magana yake gum baiyi magana ba sai mur din da yasha.
Hakan da yayi yasa nasan akwai magana fan a zuciyar shi dama kuma abinda nake gudu ke nan ban yi saurin fada mashi ba.
Ya sallami mai shagon muka kamo hanyan gida har lokacin yana gum da bakin shi sai da muka shiga gida na yi hanyan daki na sai kawai naji ya shakoni ta baya.
Idanuwa suka firfito waje kamar zan shude yace a hasale uban wa yai maki cikin da kike dauke dashi nace .
A lokacin da yasan bakin cikin da nake ciki nafi bukatan ya kashe ni in huta da wanna rayuwan wahala da na samu kaina a cikin sa.
Jin kaifin shakan yai yawa nace uban da yake matseni duk dare yai min dole ka taba kwana dani a cikin yarda nane a gidan nan.
Ya kara shako ni yana fadin yar iska sai ki san yadda zakiyi da cikin nan inba haka ba na lahira sai ya fiki jin dadi.
Nace cikin karfin hali amma kadai san ba yar iska ka samay ni ba ko bantaba kwana da wani namiji ba bayan kai a rayuwa na da zakai min wanan tambayan yan iska.
Yace good sai ki san yarda zakiyi da cikin nan a gidan nan don ni ban shirya haihuwa ba yanzu
yara su hanani shakat a rayuwa na.
Ras naji gabana ya fadi nace wata sabuwa kenan kuma inji yan caca wani sabon fitina kuma zai kawo min yanzu.
Hakana mukai ta jidali a gidab dagani sai shi daga karshe dai ya kaini kara wurin ma haifiyar shi akan lalelale sai na zubar da cikin nan in ina son a zauna lafiya.
Babu kunya ta kirani nazo gidan ta ta tare ni da maganan cikin har tana cewa nafison in cika gida da yara miji baida wadata.
Nace Allah daya bani shi zai dubeni da abinda ke cikin cikin nawa don haka na san zunubin da ke ga wanda yai kashin kai ni ba zan zubar ba.
Tace tunda haka kiks zaba duk abinda yai maki ke kika jiyo baruwa na karma kice kin sanni.
Ranan ban kwana ba sai da yai min dan karen dukan tsiya har ya barni kwace da kyat na lalaba naja jikina zuwa dakina.
Washe gari jikin yai min tsami na lalaba nai wanka na lalubo sauran magani na hade na koma na dun kule.
Waya naji yana yi da wani likita akan zubar da cikin koda ya leko dakina na lafe kamar mai barci sai ya fice gidan.
Ina nan ina sake zuci sai sallaman maman biyu naji gidan don tun ranan da suka samu matsala akan lilliya bata dawo gidan ba.
Yau tazo taji yadda mukayi dashi ne akan zancen cikin na tare da murna na abinka da wanda ta rigaka kwana sai ya rigaka tashi.
A take ta gane yanayin da nake ciki na bugun da yai min a daren jiya kan naki yarda a zubar da cikin cikin sauki.
Tace dani kunyi halin naku ko, ?
Kin sha dukan ko badai duk akan cikin bane wannan dukan haka ?
Idana sun ciko da hawayen na dama nace anty cewa yayi wai a zubar da cikin shi bai shirya haihuwa yanzu ba.
Tace a cikin mama what ?
Na hade wasu yawun bakin ciki nace har da maman shi abinda tace dani kenan wai idan ban zubar ba duk abinda ya samay ni ba ruwan ta.
Kai ta dafe tai shiru na wani lokaci can tace wai wa yan nan mutane kuwa musulmai ne kuwa ?
Na murmusa nace wai musulmai ne kuwa anty babu dai tauhidi a zukatan su ne kawai.
Ta mike ta fice gidan kai tsaye ashe wurin aikin su ta tafi don ta bincika tasan komai akan shi.
Can ta samay shi tace su hadu gidan shi yanzu sanin halin shi da tayi yasa baiyi gardama ba ta riga shi isa gidan ya samu tana jiran shi.
Yana shigowa tace zauna shagon mata don ka zama shagon mata baka da aiki sai dukan mace macen ma karamar alhaki irin wannan.
Dadin may kake ji cikin dukan da kake mata ne wai, kai bama wanan ba cikin dake jikin ta waye mata shi ?
Ya dago ya kalle ta don jin abinda ta fada tace eh ina son inji ko ba naka bane don musan abin yi.
Yace kin gane madam nasan ciki nawa ne to amma ni gaskiya ban shirya, , , ,
Sai yai shuru tace, go on, baka shirya may ba dama ka auro tane kawai don ka more rayuwan ka da ita ko may ?
Tace tirr da hali irin naka tirr da rayuwan kafiran farko kai acikin su ma kana kasa da fir,auna.
Ashe kai ba abin farin ciki ne ya samay ka ba maimakon ka godewa Allah da baiwan da yai maka sai kawai kai halin ku na yan duniya.
Ba a haihuwa kai aka haife ka, dama kenan ka auro tane don kawai kaji dadin rayuwa da ita ko may tun wuri ka gyara halin ka tun duniya nayi dakai.
Tai mashi kaca kaca yana saurare ta kamar wani salihi can dashi ni nasan jin ta kawai yake yi badon nasihan ta shige shi ba.
Ta nisa tace dashi haba dai kamar wanda baida tausayi katuna fa kaima kana da kanai kuma haihuwa zakayi indan anyiwa taka haka yaya zakaji.
Sannan ina son ka sani idan wani abu ya samay ta, ko cikin dake jiki ta sai nasa an daure kowa naka a duk inda suke a garin nan sai antona man su.
Kuma ka tabbatar da kana bata abincin daya dace mace mai ciki taci dan lafiyan jikin ta dana baby dake cikin ta.
Duk ta baibaye shi ta ko ina baida halin motsawa ta mike tana gyara gyalen jikin ta, ta wuce ko kallona batayi ba ina kuka da mahaifina da ya jefani wanan halin.
Ya dinga sintiri a cikin falo yaje ya dawo har na wani lokaci ya dawo inda nake rakube yace ke ki fada min may ye hadin ki da wanan matar.
Nai shiru ya kara daka min tsawa yace ba zaki fada min ba, nace yar uwan mahaifiyata ce na fada maka tun farko sai ya ja tsuki ya fice gidan.
Tun wanan lokacin bai ce min ban ce mai zaman doya da manja muke yi dashi a gidan sai ya kwashe kwanaki bai gidan sai yaga dama zai dawo bai dadewa kuma ya fice.
Nima haka ya fiye min dadi don ba matsi ba tsagwama ba warin taba da giya sai in yini falo gidan hankalina kwance.
Abinci dai da maman biyu tasa mai doka ina samu sai dai bamai dadi ba amma ina ci in koshi ko ba dadi yafi babu.
Ranan ina zaune a falo ina kallo sai gashi da liliya yana gaba tana binshi a baya da katon akwatin ta, suna kokarin shigowa dashi.
Wai ashe auren bariki sukayi, yan giya yan uwan su suka daura masu aure acan mashaya su.
Ko kallona basuyi ba suna kokarin shigewa da kayan nata, ina zaune ina kallon ikon Allah, suka shige dakin shi da kayan can sai gata ta fito ta bude munafukin gyalen da ta rufe fuskan ta dashi tace.
Ke wa kike da suna ina son fada maki ban son ganin ki a falon nan indan maigidan na gida in ba kiran ki akayi ba.
Nace ke kuma a suwa dan wake a hotel, tace ni a su matar gidan, inda ance min karuwa yanzu na zama matar gidan sai
a nemi wani suna a canza min.
Ya wuce a kiraki da kilaki ko mai dadiro don sunan da ya dace dake kena don kin fi cancan ta dashi.
Shine ya fito yana cewa baby na fada maki bani son kina shiga tsabgan yarinyar nan, da ita da babu duk daya a gare ni tana zaman cikin ta ne da tace taji ta gani dashi.
Kema kin san wanan ba ajina bace kawai dai matsala aka samu aka aura min ita amma wanan abar ai da gidan aiki ya kamata ta a danganta ta.
Nace andai ji kunya wallahi tunda dadiro aka fake aiko anci baya wallahi ya balla min harara da jajayen idon shi.
Yaja ta suka shige ina jin suna dariya dariyen su a dakin ga kida na tashi ina daga dakina bakin ciki ya cika ni.
Haka dai muke zaune a gidan ba ruwan shi dani ina kallo zasu sayo abu su zauna a falo su baje suci inya rage a zubar ga abin shara.
Ko ta dafa da kanta a gidan kanshi yana tashi gidan haka zanta juye da cikina su gama su cinye su hana min ina kallon su ko kallo ban ishe su ba.
Ranan suna zaune suna ta shakiyancin su a falo na samay shi a falon suna gani na, ta wani shige mai jiki .
Shi kuma sai ya daure fuska murtuk nace dashi yaya abincin da ka saya min ya kare tun kwana biyu da ya wuce.
Sai cewa yayi kije gidan ku a baki don ni ba dole bane sai na baki tunda baki jin magana na.
Ita kuma ta dago kai ta wani harareni tace ke bana fada maki kada ki kara kula min miji in yana nan ba shine don maita irin naki kikai mai magana yanzu wai manyar ina ce halan.
Nace ke tsohuwar kilaki rufe min bakin ki da ke nakeyi balle ki samun baki ga zance na.
Tsawa ya daka min yace duk ranan da na sake jin kin kira min mata da kilaki sai na halaka ki a gidan nan.
Kallon mamaki nabi shi dashi ina cewa ai akwai Allah yana sane da komai da ka ke yi shi zai saka min.
Ban karasa ba ya buge min baki gau da mari sai da wani wuta ya gittamin gaba na.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,
🧕🏿2️⃣1️⃣🧕🏿
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,
Tun muna jiyo maganan su sannu sannu har suka fara daga murya mudai har barci ya kwashe mu bamu san lokacin da suka kwanta ba.
Shiko yaya saadu gida ya tafi ya samu mahaifiyar da yanzu jikin sai a hankali sun kammala cinikin dare habiba na kirga kudi da sukai ciniki.
Dinban habiba yaya yace munafukan banza da wofi kizo ki zauna da yar uwar ki kikace baki da lafiya ne.
Yanzu may kike yi anan zatai magana ya dago kamar zai make ta yana cewa duk dai abinda kawa wani kasani sai an rama mashi.
Mahaifiyar su tace kai kada kazo fa kace zaka samin yara gaba da hitina kan safiya.
Idanuwan shi sukai jawur ya kalleta yace mummy halinda yariyan nan ke ciki ba wanda ya ja mata sai ke saboda son kai,
Kin san danki yafi karfin ki kema da kika haifeshi baki iya shi rayuwan mu ba daya ba da tashin arewa amma kika rufe ido kika nace sai anyi.
Mummy ansan mukadari ne ba wanda ya isa ya goge shi amma kuma sai ki saka ido a kanshi aike kika haifi abin ki.
Ajiyan zuciya tayi wani bakin ciki ya tokare mata zuciya, tace Saadu, nayi kuskure da na dauka Safiya idan ta auri yayan ku zata gyara rayuwansa na jefa rayuwan yarinya cikin kunci da wahala.
Ni kaina nasan ba aiwa yarinyan nan adalci ba amma ba yadda na iya dashi sai ya ce zai dauki mata akan magana na.
Gashi mahaifinta dan uwa na gari ya dauki amana ya damka a hannu na don ba da halin zuwa gidan su gun mahaifanta takai kara uba yace bai yafe mata ba.
Yaya saadu ya katse ta da cewa safiya tana cikin kunci da bakin ciki wanda duk wanda ya ganta yana da imani dole ya tausaya mata ace ana horon mutum yunwa saboda Allah fa.
Sannan mummy keda kanki kika bashi goyon bayan a fitar da cikin da jikinta keda kanki mummy mu mai yasa baki fitar da cikin mu ba da kika samu.
Wani kallo ta watso mai bai damu ba ganina acikin kunci da bakin ciki yafi komai bata mashi rai yace yanzu gashi tace zubar da cikin zatayi ta huta da wahala.
A razane tace zata zubar kuma da cikin yace eh to ba abinda kuka zaba kenan ba dama itama yanzu shiyafi mata sauki zubar da cikin.
Mummy zan inya hana wani abu mummuna da zai faru nan gaba kema kiyi abinda abin da ya dace akan zaman nan nasu amatsayinki na uwa gare shi.
Don sai karuwan nan ta bar gidan nan wallahi ko ta halin yaya, ya juya zai fita daga dakin a hasale tace saureren nan Saadu kaji.
Ban son kana shiga harkan gidan dan uwanka haka nan kabarshi shike da gidab shi da su.
Ya zamana na karshe kada ka sake zuwa mai gida katayar mashi da hankalin iyalin shi.
Ya juyo ya kalle ta yayi dariyan takaici yace mummy da kun hana ni na yarda nabar zuwa don biyyaya a gare ku.
Amma yanzu na fahince ku bakin ku daya ne akan yar uwata muddin Safiya tana gidan shi bazan taba fasa zuwa gidan nan ba.
A wane dalili zan nisanta kaina da yar uwana saboda karuwa ko may, zanyi haka wanan karon ba zan sake dauke kafana a gidan ba indai safiya tana ciki.
Muddin ina raye ina numfashi ba zan sake bari a kuntatawa rayuwan safiya ba, danki yana danne mata hakkin ta batada matsayi da yancin a gidan shi amma duk baiyi laifi ba
Mummy kin dauki yariya karama kamar safiya kin aura ma mutun irin Ahmed, ya dauko karuwa mata karuwa a gida ya hada tada ita sun taru suna kuntata mata kice wai baki sani ba.
Duk kece sillan lalacewa rayuwan rayuwan mu haka mummy yarinya na zaman ukuba a hannun danki kice wai kada a taimaka mata, duk kece mai kawo matsala a tsakanin mu mama.
Yana gama fadi ya juya ya fita yabar gwago cikin kunan rai ta bishi da kallo har ya kule tace Saadu kao baka san uwa da soyayyan dan ta ba.
Inda zaka bincika kaga yadda nake cikin damuwa da bacin rai akan yaran nan da baka furta hakan ba inda kasan nauyin da maihaifin yarinyar nan ya danka min banda yadda na iya ne.
Baka san nauyi da rikon amana kedashiba da matukar wahala duk abin nan ina sane dasu amma son dana ya rufe mun ido.
Shiko dan waje ya koma yana jigina jikin shi ga mota yana tunane ya dinga kuna wiwi yana zuka yana wa kwakwalwan sa caji tare da neman mafita akan matsalar mu.
Ya nisa yana cewa a ranshi hakika Safiya ke yar uwata ce ta jini kuma mata ga dan uwa na zan tabbatarb kin kasance cikin farin ciki zan fuskaci duk wanda ya nemi ya kawo maki kunci a rayuwan ki.
Burin mahaifinki akan hadin auren ki shine da dan uwana yaga an hada zuria mai dorewa a tsakanin shi da yar uwar shi amma dan uwana yana son yaga rushewan wanan alakan saboda rayuwan duniyanci daya dauka.
Ya Allah ka tabbatar da farinciki da kwanciyan hankali a rayuwan ku kar zumunta ya baci a sanadin auren ku.
Iya sani na mummy bata da gidan zuwa a arewa wanda ya wuce gidan mahaifin Safiya don ko sako ne ta gareshi take turawa a sayo mata abu a aiko dashi nan.
Haka dai ya kwana yana yawan tunane barkatai da samo fita ga matsalar mu .
********* ********* *********
Fitanan sune ya farka damu daga barcin safe da muka samu mukeyi a gidan nida Sadiya.
Fada suke yi sosai shida ita hakan yasa mu fitowa da sauri dakin mu danbe suke yi a tsakanin su.
Suna ta faman fashe fashen kayan falon da suke fadawa da gani har sadiya ba mai iya raba su don sun fimu karfi.
Sun dauki lokaci suna abu guda saida sadiya takira yaya saadu yazo ya raba su ta kwashe kayan ta tana mai zagin kaskanci irin na yan duniya.