Showing 153001 words to 156000 words out of 269010 words
tuni.
Daki na koma van iya tsayawa na saurari sauran maganan ba sai dai na sa a raina cewa ba zan sake shiga dakin inna ba komai ya faru kuwa.
Har yamma naji anty bata kirani ba don haka na dauki waya na kirata amma har wayan ya katse bata dauka ba.
Ban kara kiranta ba da dare muna zaune a dakin mu sai ga baba ya aiko a kira masa ummi ta dan dade wurin sa ta dawo muna hira da kanne na sai tambayan ta kauna tayi tace halan baba yaji zancen maganan dazu ne ummi ?
Tace ina ruwan ki sai kin san abinda naje yi gunsa nace kai kedai baki da kunya Aisha may zai kara ki idan kin ji ni ban ma son baba yaji zancen tace sai dai kada a kara don Nura ya tare shi da zancen a waje.
Ina ga ki je gun su kawun ki kafin bakin ki su iso kin dawo zaifi nace to ummi zan tafi amma ba don naso a raina ba don dai ta ce in je ne kawai ba yarda zanyi.
Kwana biyu da zuwa na na shirya dani da kani na sai kyauyen su ummi na ida mahaifanta suke da zama.
Tafiyan safe mukayi don haka muka isa da wuri mun samu karbuwa na mutunci a wurin su aka kai muna kayan mu dakin kakan mu mace .
Bayan muci mun sha daga abincin su da suka fi karfi suka gabatar muna dashi muka zauna a na gaigaisawa da yan uwa.
Sai yamma mazajen suka dawo daga gonakin su wanda dashi suka dogora suna ci suna sha daga gare shi sai kiwo da suke hadawa dashi.
Kakan mu ne na karshen shigowa gida sai da ya huta mukaje gaida shi bayan mun gaisa ya tambaye mu mutanen gida.
Yake tambayana zancen aure nace insha Allahu malam ba za a dauki lokaci ba zanyi yace ko dai anzo sallaman mu ne gaba daya nayi dariya ina ce mai a a na dai zone in duba ku.
Shekaran jiya na zo shine ummi tace in iso nan in gaida ku yace ai ta kyauta tun bayan abinda ya faru dake bamu sake ganin ki ba sai nake ji wai kin samu mane mi a can birni har yai masu abin arziki a gida.
Na soke kaina kasa din kuya yace yanzu dai ciwo ya wuce ko nace malam yadai lafa dai amma ai ciwon ba mai barin jiki bane kwata kwata.
Yace ummh ummh kar ki yarda da wanan ki sa a ranki Allah zai baki lafiya ko yana nan baya tashi har a manta cewa kina dashi a jikin ki nace Allah yasa malam.
Yace ai kin ga rakumi nace eh malam yace to komai na jikin shi magani ne bani na fada ba in ji fiyayyen halita SAW ya fadi.
Yace da zaki samo fitsarin nan nasa koyaushe ya zama maki kamar ruwan shan ki to da kan ki zaki dawo nan ki bani labari bance zaki warke ba atake amma akwai faida a gare shi.
Nace shi fitsarin rakumin yace kwarai kuwa sannan namar shi ya zama maki abin ci ko yaushe akalla a sati ki kici shi ko sau biyu.
Sai kuma nonon shi ki dinga sha akai akai shima yana da faida sosai a jikin bawa ya dan kurkure baki da ruwan butan dake gefen shi yace sannab kin ga kashin rakumi nace eh malam yace ki samu kashin ki gone shi zai ya kono sosai sai ki daka ki dinga sha da albarkan annabi zaki neme ni indan muna raye.
Ba fa wai matsalan ciwon da ke damun ki ba kawai a a koda jikin ka ne baka gane kansa ba ne mi daya daga cikin sassan jikin rakumi ka riki sahihi da yardan ubangiji zaka ga faidan shi.
Nace ikin Allah yace shiko kashin nan nasa da kika gani nace eh malam mutane ne basu gane mai ba ai da zaki samay shi.
Ki busar dashi ki samu kanufari ki hada dashi kina yin hayakin shi a jikin kin ki sai yayi murmushi yace aiko maza dake samun matsalar rashin karfin gaba gane wa ne ba sayi amma da mutum zai samay shi yayi yadda nace maki sai ya dinga hayaki a gaban shi dashi ai ba katamin taimako yake yi ba za ka iya kuma dafa gaban shi sai dai ba a faye samun shi ba don tun wurin soke shi ake sayewa.
Namiji in dai yana amfani dashi ai masa romon shi da bakin iri ban san yaya kuke kiran bakin iri ba ku.
Nace ko habbatussaudat yace sunan sa ke nan ko nace eh yace sai a hada da kanumfari da citta da masoro da tafarnuwa yace ai bashi ba gazawa ga iyalin shi don karfi ne zai taso mashi sosai yaji shi gyagyan kamar dan shekara a shirin a duniya.
Yace kaiyya ai abar gado tun baya an dauki aladun wasu mun dora wa kan mu amma kin ga mu na kauye ai bamu bar gado ba, kin ga ko mun fiku karfi da lafiya don mu ciwon nan da ake fadi duk bamu sanshi ba.
Nace hakane malam amma ai inda mutum zai samu rakumi ne aiki malam har ya tara fitsarin shi da yawa haka.
Yace kuke nan dake birni amma munan ai shi yafi komai sauki ko yanzu kafin ki tashi zan iya sa a tara maki jarka kuma samo maki sauran sassan jikin ki jeraba ki gani.
Godiya na fara yi masa yace may ye abin godiya a ciki lafiyar ki ai namu ne duka yanzu barin fita idan na dawo maci gaba don lokacin sallah yayi yanzu.
A Zuciya na fara tunabe nayi yadda mutum zai sha waban abin da ya fada min amma dai ko yaya ne zan nema un jeraba in gani nma mikewa na yi zuwa rumfar kakata inda dakin ta yake na zauna rubuta duk abinda yace min nayi a wayana.
Bayan munyi sallah aka gabatar muna da tuwon surfafen dawa da miyar danyen kuka an lema man shanu a saman shi.
Kanina yace bazai ci ba shi zai fita yasamu bread da shayi ya sha azuciya ta nace ikon Allah ashe akwai abincin da dan gidan mu zai kyamaci ci a yanzu.
Nikan naci shi sosai nayi kat tare da hamdala na wanke hannu na sai naji kawo habu ya shigo yana cewa ina bakuwar tamu ga dan tsaraban kauye nasan ba iya cin abincin namu zakiyi ba ya miko min leda na karba hannu bubiyu ina cewa ai ko naci kawu sai da na koshi.
Ledan na aje a gefe na shima ya samu wuri ya zauna muna hira kakan mu tana sa muna baki jefi jefi.
Nan dai har ya gan garo kan zancen aure na nake fada mai halinda ake ciki yanzu ga zancen nawa ban boye mai komai ba ya murmusa yace abinku ne na yan birni.
Baku neman gida sai abu ya kure maku gani kuke yi kamar mu kauyawa ne komai bamu sani ba banda noma da kiwo amma ai aiki sai kauye.
Nace kawu ba hakana bane nayi nisa ne daku ko gida sau biyu ke nan nazo tun tafiya na yace to kin ga tunda kinzo yanzu ai ba a barki haka ki koma ba ai wani dan abu ba.
Kin ga ki samu kaucin gwandan daji da kan tunkiya ki daka ai maki miya dashi kaucin zaki iya dafawa kuci har da yara in Allah ya kawo su amma fa banda mai gida wanan mallakane sahihi.
Sai na neman farin jini ga dukkan dangin miji da ma mijin kan shi zaki samu farar dawa da farin goro farin kudi kurma farar kaza sayen tunfafiya na gabas din shi ki hade ya bushe kiyi wanka dashi da hayaki bayan kin dake su wuri daya, sai naga yayi murmushi.
Don watse makircin makiya kuma zaki karanta Lah illah hailala muhammadun rasulallah, hasbunal lahu wani imal wakil kafa dari duk safe zaki ga yadda zasu kwashe da yardan Allah.
Domin tsarin jikin ki kuma zaki samu ganyen hankuwa da ganyen sabulun dawaki da ganyen geza wanda suka fadi kasa da kansu a dake ki sha.
Wanan ma na tsari ne zaki samu gero wanda ya fidda kai ya baci yayi geza da suren fatake a dake asha da kunu .
Kiran da matar shi ta aiko tana mashi ne yasa ya tashi badon ya gama bani ba sai da ya fita nace ma kakana ni ina zan samu wanan abin daya fada min tace Allah ya kaimu gobe sai in zagaya nan bayan gari in harhado maki su wanda babu in kin koma can gwagon ummin ki sai ta samo maki ban samu ganin kakana ba don ance yana waje da bamin fulani da suka zo wurin shi.
Don haka nayi shirin barci na kwanta da wuri sai barci can cikin barci na naji Shafiu ya dawo kakan mu nace mashi ya dauki ga leda nan da kawun mu ya sayo muna nama ciki.
Ban iya bude idona ba don barcin da yaci karfina a lokacin har ya gama ya fita ban tashi ba tagama abinda take yi ta rufe kofan daki ta sauke min gidan sauron da ta kafa min na gyara kwanciya na asuba ta gari yan uwa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , ,
🧕🏿5️⃣2️⃣🧕🏿
NOVEL DINA NA KUDI NE NA FADA MAKI KADA KI FITAR MIN DA NOVEL AMANA NE GARE KI IDAN KUMA BAKI BIYA BA KIKA KARANTA ALLAH YA BI MIN HAKKINA A KAN KI DON BAN YAFE MAKI BA
Washe gari malam yayi sakon fita zuwa wani kauye da fulani da mano ma suke rikici akan gona don haka ban samu ganin shi ba ranan sai dare sosai mota ya dawo dasu har kofan gidan shi don haka ba halin in ganshi da daren nan.
Gashi washe gari zan koma don shirin taron bakin da zasu zo min anan kauyen su ummi na sayi kwan zabbi mai yawa da kuma zabbin da ransu wanda zamu gyara masu idan sunzo .
Nono har na rasa inda zan sakowa yana kawo min kyautar kwai da nono tsaraba.
Naje sallama da malam yace Allah sarki Safiya sa ar safe gashi ban samu ganin ki ba har zaku wuce nace malam ai zan dawo kafin na tare yanzu ma zan koma ne na tari bakin da zasu zo yace to ga nawa gudun mawa rago nan sai a soya masu idan sun zo Allah ya tabbatar muna da alheri yasa muce gwanma da akayi.
Nace amin a kunyace yace banyi fushi ba duk da an kasani amma in mun hadu da abokin nawa watarana zai bani kudin fansan ki a gareni.
Nayi dariya kawai na mike ina mashi sallama muka fito don mota nasa aka dauko muna shata dagani sai Shafiu kawai sai kayan mu.
Mun iso gida kafin sallah azahar aka fitar muna dakaya zuwa cikin gida na sallami driver tare da yi mashi godiya nace ya ban nombashi idan muna da sako yakai muna.
Don tunda muka kama hanya yake muna hiran yanayin kasar da sauran su shafiu ne ke bashi amsa ni sai jefi jefi nake saka masu baki ga hiran nasu.
Mun shiga gida sai bin mu akeyi da kallo Aisha ke fadin ga mutanen kauye sun dawo munko ga alama don ga tsaraban kauye nan hardasu zabbi da kwai.
Ummi ce ta buge mata baki tace kai surutu muka shiga daki na huta mama tazo ta tare mu ta tambaye mu yaya muka barsu nace lafiya suna gaida ku.
Zata juya nace mama ga nono nan da kwai da zabbi nazo dashi don bakin da zasu zo jibi sai a gyara masu.
Taji dadi tace a a baki muke dasu tafe ashe sai ta karasa shigowa dakin tana cewa yanzu yaya za ayi masu dashi don mu fara saboda akwai aiki sosai.
Nace mama yadda ya dace zakuyi dashi mana tace to yanzu bari in aika ma mamakin suzo asan abinyi kafin gobe a makara.
Ta aika kiran su mama zuwa karfe biyu sai gasu sun iso nan ta gabatar masu da komai don haka suka fara tsara abinda zasu yi na kawo kudi na basu wanda za a sai kayan aiki.
Da farko an yanka ragon da malam ya bani nan suka shiga gyara saadatu ne kawai ta fito inna cewa tayi wai ba a sata a maganan ba.
Kowa ya share ta a gidan yaya Sani yayi fada har ya gaji baba yace a kyale ta ranan asabar mi salin karfe dayan rana sai ga su kawu abu sun shigo wai babane ya aika su zo nace kai baba ho tambayan aure shine harda taso su kawu su zo kuma.
Zuwa karfe biyu saura suka iso mota biyu akai masu taron mutunci sunci sun sha sai suka gabatar da zancen neman aure da kuma suna son a yanke masu sadaki kafin su wuce.
Baba yace sadaki dubu ashirin zasu bayan ba kuma zasu wuce ba sai an daura aure don ni ba budurwa bace.
Duk yadda suka so baba yaki yarda dole suka amince za a daura kagin su wuce mu dai sai ji mukayi mai shela na sanarwa a na gaiyatan mutane kofan gidan babana.
Nan dai aka sheda daurin auren na da sulaiman akan sadaki dubu ashirin kacal ina daki kwance shafiu yazo min da labari.
Zubur na mike ina cewa yaya uncle zai min haka kuma ai ce min yayi tambaya zasu zo da kuma saka rana.
Mutane sun rage yawa sai ga bakin daya daga cikin su ya shigo na fahinci kannin Sulaiman ne don naji yana cewa ina amaryan nawa take na ganta don ban santa ba.
Nayi saurin boye sai da mama ta shigo tace in fito mu gaisa hijjab kawai na saka na fito yana zaune falin ummi yana gani na yace ba laifi shiya sa bross ya lake sai ke amma kamar na san fuskan nan taki wani wuri.
Gaida shi nayi shiko sai sheri yake min yana fadin yau ban san yadda zai ji ba idan yaji har an daura aure gaba daya akwati biyu na gani anshigo dasu yace ga sakon baaban mu nan tace a kawo maki na mun gani muna so gashi kuma har kin zama namu gaba daya.
Na dago kai da kyat nace aimin godiya wurin baaba kafin inzo yace zata ji ya mike yana fadin zamu tafi do garin naku akwai nisa sosai wallahi ai gara da aka daura gaba daya muka huta.
Mukai sallama ya fita nan aka fara fita masu da kayan da aka hada masu na ganima suka ce harda wani dawai niya haka kuma.
Nan sukai min sallama suka tafi cike da farin cikin irin karramawan da suka samu a wurin mu sun kuma yaba da halin baba da bai yi zari ba da kwadayi ya karbi kudi kadan a sadakina.
Nan aka bude akwatin mama ta fara daga dankara dankaran zannuwan dake ciki da lece har goma sha biyar dayan akwatin sauran tarkace ne a ciki aka zuba.
Baba ya shigo har dakin ummi da kudin sadakina a hannun shi yana cewa ina Safiyan ga sadakin ki nan hakkin kine ba namu ba sai dai nayi karanbanin yake masu mafi saukin sadaki don samun albarkan aure.
Na mika hannu bibiyu na karbi kudin tare da nufan ummi na dake zaune gefe dasu tace a a rike abunki Allah yasa albarka duk wanda ke dakin yace amin.
Ya fita na koma kuryan dakin na haye gado tare da lafewa kamar mai yin barci ina jin suna watsewa da guda guda.
Ya saura sai ni kadai da yan gidan mu kowa ya kama gaban shi daga inda nake kwance na jawo waya na naji ina son kiran anty in fada mata ta ida aka hau tanan ake sauka.
Amma har ya katse bata dauki wayan ba na kara kira yan biyu ta dauka tana fadin tana sallah na kira sunan ta take ta gane ni mukai ta hira dasu har tagama ta dauki wayan.
Muryan ta ba yabo ba fallasa muka gaisa tace abubuwa sukai mata yawa shiyasa bata samu kirana ba amma tasha ganin miscall dina.
Mukai sallama nai mamakin jin bata tambaye ni Sulaiman din ba nima kuma ban mata maganan shiba.
Faiza na kira tace ke yar kasa ai na dauka ki manta danine ina son in kiraki ina jin tsoron kada ki fada ma mutumiyar tamu nace haba don kin kirani sai in fada mata kuma.
Naji ta shake murya tace dama ina son kiranki in sheda maki anty uwa nan tazo ita da yaranta sai faman shuka muna tsiya suke a gida.
Nace don Allah yaushe tazo tace yau kwananta biyu da zuwa wai may ya hadaki dasune Safiya?
Nace ni kuwa ina na san su banda wurin liyafan da muka hadu a abuja.
Tace aike gara da baki gidan don ko ita anty ta gaji da su wai kuma sati daya zasuyi a gidan nace tirkashi .
Tace ke dai ai kin auna arziki da kika tafi basu samay ki