Showing 240001 words to 243000 words out of 269010 words
hutu ya kare sai a dawo dasu.
Dan jimm yayi sai yace Safiya maigidan ki bazai ga rashin hankali mu ba kuwa nace ko daya baba babu ruwan shi ai shi bamai zama gida bane ko yaushe.
Sai yayi kwana nawa ma bai gansu a gidan ba idan ba ya kama ba yace nasan halin yaran nan basu jin magana kada kina zaman ki da mijin ki lafiya su je su tayar maki da hankali can.
Nace baba babu komai wallahi ai khadija ma baiso ta dawo ba itace ma ta matsa zata dawo din yace dayake tasawa kanta shiriritan son wanan yaron ba.
Niko da raina da lafiya na wanan abin ba zai yuyu ba muddin ina raye shirmay ta dai takeyi kawai.
Mun dan taba hira dashi yana ta min nasiha akan zaman aure da zaman takewa a cikin mutanen da ban saba dasu ba har magariba ya gabato muna wurin.
Haka ya mike yaje yayi alwala ni kuma na koma cikin gida ina shiga mama ta biyo ni dakin tana fadin kai Safiya ke kika iya da halin mahaifin ku.
Nace mama nasan halin baba don haka ban fito mai kai tsaye da daukan su zanyi ba sai na laba ga hutu ba sai ya gansu ba kuma ko yayi magana nasan abinda zan fada mashi gaba.
Yaran da sukaji za a tafi dasu suka fara murna mace kada su dauki wani kaya mai yawa kada baba ya gane tafiya zasu yi kayan sallah ku kawai zaku dauka.
Tun da safe ana ta fita muna da kaya waje duk sai naji raina ba dadi a lokacin ina kuryan dakin ummi ina shiri ta shigo dakin nace ummi amna dai ya kamata kizo kiga gida na idan na koma gaskiya.
Tace ba iyayyen ki sunje sun gani ba zuwan may zanyi kuma ni nace haba ummi kamar wace bata da gata ai dai dake da baba ku dan leka watarana ko ?
Tace ba dai yanzu ba sai maigidana zaiyi aure ko nace haba ummi khadija dake zaune gefe na tace kyale ta ninan zan rakota har Abuja idan kin koma.
Gwago dasu mama jimmai sun shigo sallama na dasu Saadatu har da mijin ta da kishiryar tan nan na fito tsab dani na shiga wurin baba na rusun na tare dasu maimu nace baba zamu tafi asa muna albarka.
Yace kullun cikin sa maku muke safiya nan yayi wa su maimu fada sosai na su natsu har su dawo lafiya na shiga wirin inna mukayi sallama nayi mata Allah ya sauwaka.
Na fito kofan gidan namu ya cika da jamma a ina tayiwa mutane ban kwana na shiga mota Adamu ya zo mukayi magana dashi ba wanda yaji may nake fada mashi.
Sai dariyan da yayi yana daga muna hannu nan muka barsu tsatsaye suna bin motar da kallo idona na lumshi ina jin wani iri a zuciya na gida a kwai dadi wallahi indai kazo da zuwan bakunta nace a raina.
Suka yaran sai farin ciki sukeyi yau zasu birni duk sun sallami abokai da yan uwa sai washe baki sukeyi cikin murna.
Sai karfe biyu da rabi muka shigo garin Abuja inda muka wuce gidan mu direct daga shigowan mu kanne na da suke ta surutu sai suka koma kallon gari.
Mun iso gidan duk zuciya ba dadi har lokacin a hankali na furta Alhamdullahi a fili tare da yunkurawa ina shirin fita daga motan ji nayi sunce anty mun iso ne eh kawai na iya ce masu.
Security din ne ya fito ya bude muna mota tare da fadin sannu madam sannu ismail na iya fada mai nace nagode.
Fita nayi daga motan tare da amsan Abba dake jikin maimu yana barci saida na karbeshi suka fito daga motan tare da daukar min jakkan hannu na muka nufi kofan shiga gidan.
A rufe gidan yake na dan danna bell ajima kadan sai aka bude Nura ce ta fito tana ganin mu tace ah wellcome madam.
Thanks nace mata ta matsa muka shiga tare da kanne na dake bina a baya tsakiyan falon na nufa na shimfede yaron saman kujerun falon da suka sha gyara.
Na juya naje kuna Ac da fanka a lokaci guda take falin ya fara canza yanayin shi daga zafi zuwa sanyi.
Har yanzu su maimu basu zauna ba nace dasu ku zauna mana gaku kamar masu tsoro da sauri suka zauna a takure saman kujeran duk sun matse juna.
Zama nayi ina kokarin dauko key din daki na a cikin jakka na can kasa naji key din na fito dashi daidai lokacin da Nura ta kawo muna ruwa da juices din kwali gaban mu da kofuna ta aje.
Goran ruwan na dauka na fara tsiyaya a cup tare da masu nuni da su dauki ruwa su sha mana suma da sauri kowa ta dauki cup din zasu zuba ruwa nace bazaku sha lemon bane muna sha maimu tace min da sauri.
Bayan na shanye ruwan na aje cup din na mayar da jikina ga makarin kujeran tare da lumshe idanuwa a hankali na danyi tunane sai kuma nayi ajiyan zuciya.
Wayana yayi kara daga cikin jakka na na jawo jakkan ina duba wayan yaya Saadune yake kira na alokacin na dauka tare da fadin hello yaya .
Yace Safiya yaya hanyan na amsa da Alhamdullahi yaya.
Yace kuna ina yanzu ?
Gamu gida yaya na bashi amsa a takaice.
Yace ashe kun iso ke nan , ?
Eh yaya
Yace OK sannun ku da zuwa gani nan tafe yanzu mu gaisa
Sai kazo yaya kawai nace na kashe wayan ina kara mayar da kaina yadda yake da farko.
Mikewa nayi na bude dakina yayin da su malam musa ke ta shigo muna da kaya cikin gida shi da wanan security din Nura ta tarawa daidai kofan kitchen din mu.
Dakin na shiga sai duhu na kunna wutan dakin tare da jefa jakkana saman gado kaya na fara cirewa a jikina na shiga wanka na dan dade ban fito ba.
Sai can na fito na sauya kayan jikina na samu Abba ya tashi daga barcin da yake yi tv na kunna kafin in zauna na kalli dining naga Nura ta jera muna abinci a wurin.
Makulin da nafito dashi daga daki na bude wani daki a kusa da na mummy nace da su maimu ku taso kuga dakin ku ko.
Da sauri suka taso zuwa inda na kira su wanda sai kayi dan tafiya zuwa wurin nace nan yayi maku ko yanzu dai gaku a cikin gidana.
Fushi ya kare maimu da baba dakin muka shiga dukan mu sai baza ido sukeyi kamar matsorata a raina nace rayuwan kauye baiyi ba gaskiya.
Ji yadda yara ke wani iri kamar wa yanda basu yarda dani ba ko wani saman gadon dakin na zauna nace suma su zauna Abba nake kokarin cire ma kayan jikin shi a lokacin.
Nace kunga ga bayi nan don Allah banda kazanta don shi zai hadani ku ba komai ba a kullun a wake bayin nan sau uku ko sau hudu a rana.
Taso muje in gwada maku yadda zakuyi amfani dashi nan dai na nuna masu komai nace su kwaso kayan su sushigo dashi dakin a tare muka fito ina ce masu suyi wanka muci abinci.
Sun gama sun fito shima Abba wanka nayi mai muka fito muka ci abinci muna kan ci yaya saadu suka iso gidan shi da samira.
Ina ganin su nace chewgun ke nan kina lake ko yaushe masu miji ke nan ina kuma kuka baro min diyata ?
Tana wurin uwarta tace ganin yaran yaya ce ina kuma kika kwaso wayan nan yan kauyen haka hararan shi nayi nace ina kaga yan kauye kuma anan ?
Tace ke ko kin so dawowa ji yadda kika koma kin je kin cinye ma tsofi abinci kin ki dawowa.
Na lumshe idona nace bari samira wallahi gida akwai dadi kamar karna dawo nake ke ji sai naga gidan nan yayi mi wani irin girma wallahi ba hayaniya ba motsin kowa.
Kajiki da wani zance har yaushe kika bar nan din da zakice wai wani gida dadi ai da ki zauna gida in baki dawo kin samu munyiwa uncle din ki aure ba.
Samira ke da kanki ke fada min haka lallai wata shigowan kishirya ki ya tsaya don wanan watan zamu kawo maki wanan karfen kafan da ta leke wa yayana.
Don Allah Safiya ki daina zancen wanan gajan matar da ta tashi aiki don wulkanci ta rasa wanda zata lekewa sai mijina yar iska.
Yace ai shike nan tunda kin san takon ta kuma da tayi maki tsiya bani go ahead kawai safiya na shigo da hafsat kai tsaye
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/15/20, 7:06 AM - Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , , ,
🧕🏿8️⃣1️⃣🧕
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Bayan tafiyan su samira da basu dade ba na shige daki nayi laasar na fito muka fara gyara kaya da Nura su maimu suna taya mu.
Kafin wani lokaci muyi ma komai muhalin shi mu aje a inda ya dace kuma na nuna masu wanda zasu ci inda suna bukatan ci din.
Falo na dawo inda kanne na suke suna kallon na zauna sai dai ni ba kallon nake yiba waya nake amsawa daga mutanen gidan mu suna tambaya na mun sauka lafiya .
Abincin dare suka ci ina zaune a kasa idan na sallamay sallah ishai wayana yayi kara uncle ne ya kirana a lokacin na dauka da sallama tare da karawa a kunne na.
Uncle ina wuni na fara fadi ya sauke a jiyan zuciya kadan yace madam kun dawo ko kuna can har yanzu nace uncle gani daki na muna ta kewan ka, gidan ya koma ba dadi da baka nan.
Murmushi yayi tare da fadin I miss you to my wife ina Abba dasu mummy nace ga Abban nan hannun maimu mummy kuma bata dawo ba.
Maimu ya maimaita sunan da na fada nace eh tare da su nazo ita da hindatu sin zo muna hutun kwana biyu ne .
Yace bana ce ki samu yarinya kizo da ita ba idan zaki dawo don ki samu abokiyar hira a gida nace ko yanzu ga su suna debe min kewa a gidan.
Bai kara yin magana sai cewan da yayi kara ma Abba waya inji muryan shi sai na manna ma yaron waya a kunnen shi nan ya fara yin gwalanci kamar ya san abinda ake nufi mika ma maimu wayan nayi tace ina wuni yaya yace a a ke yar kauye ashe kun shigo gari sai yarinyar tace eh.
Amshe wayan nayi ina fadin kin yarda ke nan ke yar kauye ce ko na kara ma hindatu tace cikin muryan ta mai sanyi ina wuni yaya ya amsa mata tare da tambayan da wa nake magana tace hindu ce.
Sun jima yana masu tambayoyi wani su bashi amsa daidai wani kuma su fada mashi ba daidai ba
Mukai sallama dashi yana fada min kada in rufe gida yanzu zaa kawo min sako in kar ba godiya nayi mai tare da tambayan shi yaushe zai dawo ?
Yace kin damu in dawo ne ko wani abin kike so madam nace babu komai sai dai kewan ka da mukeyi na rashinka a kusa damu.
Kararawa kofa yayi kara ni da kaina na tashi na bude gidan malam musa driver ne da ledoji da kwalaye ya shigo dasu ya koma ya dauko sauran sai leda daya miko min hannu da hannu na karba .
Bayan na karba na fahinci maye a cikin ledan don jin zafi danayi daga cikin ledan yana tashi da kamshi.
Yayi muna sallama nace ya tsaya ina zuwa yace a a hajiya nima maigida ya saya min nawa na gode wallahi sai da safen ku yana dan dukar da kai kasa alaman girmamawa gare ni .
Yana fita na koma wurin kayan daya shigo dasu ina duba inda naga kayan tea ne mayan gwangoni madara biyu sai na milo da nescafe da ovoltin sai katon din sugar na kwali.
Dayan kuma fruit ne a ciki iri iri masu kyau fresh one murmushi nayi don akwai wanan abin daduk aka sayo muna a gidan.
Ledan da kamshi ke tashi a cikin sa wanda tun ban bude ba na fahinci may ye a cikin wanan ledan kaji ne gassasu guda uku kosassu sun gasu dakyau irin gasuwan resturant din nan da albasa da kabeji da sauran tarkace wanda yakan sawo muci a gidan.
Yaran dake satan kallo nace hindatu ta dauko plate a kitchen guda uku kowa ya dauki kazan daya yaci maimu tace anty duka nace eh duka maimu.
Ban koma ta kansu ba ina faman dakilan wayana suna ci suna dan magana kasa kasa danaji maganan yayi yawa na dago ina cewa dasu wai may kuke fadi ne kasa kasa.
Wai cewa tayi kada mu cinye duka mu rage gobe muci saura nace akan may zaku rage idan kuna iya ci duka kuci mana.
Basu iya cinyewa dukka ba duk zalaman su anan suka barshi nace suje su saka a fridge ban ci nawa sai fruit din naci kawai bamu dade ba nace suje su kwanta su huta.
Sai da na tabbatar sunyi barci na dauki Abba zuws dakina na kashe wutan falon komai daya kamata in kashe na kashe na shiga na kwanta asuba ta gari.
Da safe muna tashi bayan munyi sallah nace suje suyi wanka kuma kullun da sunyi sallah haka zasu dinga yi suka shige daki don yin wankan dana ce suyi.
Abba nayiwa wanka na shirya shi na dauke shi nakai masu dakin shi na dawo nayi nawa wankan na shirya.
Nura ta iso ta fara aikin hada muna breakfast din safe a lokacin na shiga kitchen din nace kada tayi wani mai yawa don ba a ci sosai.
Bayan mun karya ne muka zauna su kallo ya dauke masu hankali waya na na dauko na kira samira muka dan taba hira da ita nace idan ta samu lokaci ta shigo don Allah ina son tayiwa su maimu sayayya kayan sawa don ni ba dama in fita uncle bai gari.
Tace zata shigo zuwa rana asan abinyi din akai nan muka kashe wayan nima kallon na kama yi don shine aikina kawai tunda ba fita nakeyi ko wani abuba.
Sai idan uncle yana gari ne watarana nakan shiga in muna abincin garagajiya don yana so ita kuma Nura bata iya ba sosai.
Hajiya baaba na kira don mu gaisa tace na dawo ko ina gida har yanzu nace hajiya mun dawo jiya muna Abuja yanzu.
Tace yaya muka baro su nace suna lafiya suna gaida ku baaba tace to yanzun dai kinje gida hankali ya kwanta ko ?
Don Allah safiya ki bi mijiki a yadda yake so ku zauna lafiya don Allah yanzu tunda kin san halin shi kibishi a yadda yake ban son yawan fitin da kuke wayan yi ko yaushe din nan.
Insha Allahu baaba zanyi yadda kikace din tace nasan komai safiya nasan kina hakuri sosai dashi shima din halin shine kawai haka bawai yana yi cikin son ranshi bane.
Godiya nayi mata na kashe wayan ina tunanen maganan da mukayi da hajiya din shigowan samira gidan ya kawar min da tunanen da nakeyi.
Samira ta shigo na bata kudi nace taje dasu don kada a samu akasi tace bata zuwa da kauyawa ko ina nace watarana kina ganin su nan sai sun fiki wayewa.
Tana masu sheri suka fita taja motan yaya tabar gidan tare dasu haka yasa na samu kwaciya nayi barci sosai dani da Abba kadai a gidan.
Zuwa rana suka dawo da kayan da ta sawo masu din kayan sunyi kyau sosai na bata atamfofi a cikin kayana da zata kai masu dinki.
Nace ina son yaran nan suyi clean ne samira su din rabin jikina ne da komai nawa watarana sune wa yanda zasu tallafa min a lokacin da nawa kadfin ya kare.
Tace gaskiya ne Safiya da har ina ganin wautar ki na dauko su sai yanzu na gane hikimar yin hakan da kikayi akan su.
Zasu taimaka maki kwarai a rayuwa ki don naka sai naka haka abin yake wallahi Allah ya taya ki rokon su nace amin samira.
Sannu a hankali nake koya masu komai kuma suna ganewa sosai don sun sauya kamar basu ba don da gani sun saurari fadan da akai masu da zasu zo.
Sai da uncle ya kara sati biyu ranan alhamis ya dawo da dare ni dai ina barci naji wayana yana ruri na dauka muryan shi naji yana fadin bude min gida don Allah.
Da sauri na mike tare da daukan key na fita daga dakin na bude gida da sauri yana tsaye yadan jigina jikin shi a bango suith din shi na sagale a kafadan shi.
Mirmushi na sake