Showing 3001 words to 6000 words out of 244445 words

Chapter 2 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16416

nuna mata duk d’aya suke a wajen ka sanann ka nuna mata mahimmancin su da mu kanmu
a wajen ka hakan shine dai dai,kuma kamar yadda Yassira ta fad’a hakan ne zai sa ba zata samu damar shiga tsakanin kuba’’

Kamar Yashjub zai yi kuka dan takaici cikin b’ata fuska yace
‘’Haba Daddy you sound exactly like them, yanzu ta Ina Manubiya…’’


Cikin katseshi yace
‘’Bana son musu’’

A hankali Yahanasu ma tace
‘’Yashjub ka yi abunda sukeso a samu a zauna lafiya’’

Cikin jin dad’in abunda tace Daddy yace’’yauwwa y’ar albarka,rivalry a tsakanin y’an uwa bashida dad’i sam kuma ba zan lamuntaba,karka
sha mamaki hakan da kayi ya sanya wa ita Yahanasun bak’in jini.meyasa ka ji ana cewa iyaye kar su ke nuna wanda suka fi so a tsakanin y’ay’an su?’’Bai jira jin amsar su ba
ya cigaba da cewa ‘’saboda irin haka!.
Kuma aure ya zo a k’urarren lokaci mahaifiyar ka kanta bata sani ba ni kaina ina tunanin ta yadda za su d’auki abun ba tare da sun ji wani iri ba
sannan kuma kwatsam ka zo da wannan al’amari
dole a ji haushi mana Yashjub.
Umarni nake baka daga yau bana so in sake jin komai,kana ji Ummi har ta fara cewa kun fi shak’uwa kaida Yahanasu
Ita da ta zo jiya jiya har ta fahimta,dan haka kamar yadda suka buk’ata ka gyara tun kafin itama ta zo ta fahimci wani abun azo ana samun matsala.
Sannan whatever it is
da yake going on tsakaninka Kai da Mahaifiyarka
inaso ka gyara shi da wur wuri ku shirya in dai kanason albarka kuma kanaso nima mu shirya nida kai,uwa ba abar wasa bace
sabuwar rayuwa zaka shiga
kaje ku shirya ka nemi albarkar ta’’


Ahanakali Yashjub yace
‘’InshaaAllah Daddy’’

Shiruu d’akin ya kuma yi kafin chan Daddy ya furzar da numfashi yace’’sai maganar Yassir,his company…wallahi har bana so in yi tunanin abun,ban san Ina yakai kud’in ba komai ya tsaya chak
sannan contract d’in ma da ya d’an samu shima abun yak’i ya yiu kuma laifin sa ne dan sam bai d’auki abun serious ba.

Da farko da nace zan zuba masa ido ne kawai in kyale sa amma no matter how hard I tried ba zan iya ba he is still my son’’
Daddy ya k’arashe maganar tasa ahankali yana mai fesar da iska kafin ya cigaba da cewa’’ni dai na riga na gama sakawa araina ba zan sake basa jari ba tunda bai san ciwon kanshi ba,amman kai zaka iya if you wishi ba wai tilasss nakeyi maka ba sai
In kaga dama.’’

Ajiyar zuciya Yashjub ya sauk’e kafin yace’’akwai abunda nake shirya mishi,aikin da nake yi d’azu da safe ma kenan sMANNUBIYA
(Book 2)
Page 02

Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.

Shiruu yayi kafin chan ya fesar da iska yace’’sabon company ne na bud’e masa na riga na gama registerring da CAC tun tuni na biya komai na karb’a har certificate,dama wani d’an information suka bid’a kuma shima na tura a d’azun.Na bud’e masa company d’in ne dan ya samu ya dinga shigo da k’ofofi windows bulbs da duk wasu kayan gine gine dai nake ganin dacewar ya fara k’arbar kwangilar su,naga abun it’s easier kuma in a fancy way tunda za’a dinga yawan travelling abunda ya fi so kenan gashi ba wahala,inshaaAllah ni da uncle d’in Najeeb zamu harhad’a shi da mutane da zarar ya fara,zai samu alkairi a ciki sosai inshaaAllah kuma kaga yanada ilimin architect so in yanada wayo he can make use of that,tunda wannan aikin dai will not take much of his time and strength tunda na san wahalar ce dama baya so.

Already yanada building d’in shi,so sai ya fara anan dan adress d’in ma na saka tunda yanzu ya fara wajen zai ishe sa kafin muga abunda gaba za ta haifar.
Amman Daddy ka yi hak’uri ka yi mishi magana ka ja mishi kunne,kaga dai yadda ya maida wanchan campany d’in zane zanen nasa,na san wannan babu wani wahala kowa ma zai iya
But it’s Yassir that we are talking about here
sai an ja masa kunne akan ya maida hankali.’’

Ahankali Daddy yana jin tsananin k’aunar Yash d’in tana sake ratsa sa yace‘’inshaaAllah Yash,zan ja masa kunne sosai’’ kasa hak’ura yayi sai da yace ‘’na ji dad’i sosai da ka damu da d’an uwanka har haka
Allah ya maka albarka Allah ya sake had’a min kanku.
Amman naga kamar har yanzu bakwa shiri har tun incidence din da ya faru ranar a gida’’

Murmushi Yashjub yayi kafin yace’’yeah!baya min magana he’s still mad at me shiyasa dama na bari sai na gama komai sai in had’a a lokaci guda in basa takardun tare da sabuwar motar da na siya masa ta neman sulhu.

Murmushi Daddy yayi kafin yace’’Allah ya muku albarka’’

A tare duk suka had’a baki
suka ce ‘’Ameen’’
Daganan suka shiga tattaunawa akan yadda auren Yashjub d’in zai kasance…da farko Daddy cewa yayi ko za a d’an k’ara lokaci tunda bashida lafiya amma kalar zaburar da Yash d’in ya yi saida ya sakasu dariya
shikuma ya sa kanshi a kunya
dan haka ya ja bakinshi yayi gum bai sake cewa komai ba a ransa yana mamakin yadda Manubiya ta maida shi.

Daddy dama ya san maganar gida ba shi zai yi ba tunda abun na masu yi ne,aikuwa ilai yana yin maganar Yashjub yace ya yi covering wannan ma.

Sun tattauna sosai tukunna
Daddy ya tafi bayan Yashjub yayi mishi alk’awarin shiryawa da Mommy da zarar ya koma gida InshaaAllah dan dama already ya ji ya d’an fara hucewa akan abunda ta yi masa,ga kuma maganar da suka yi da Manubiya kuma yanzu kam tunda har Daddy ma ya sa baki inshaaAllah zai je su shiraya ya bata hak’uri dukda kuwa itace mai laifi.

Sai da Daddy ya fita tukunna Yashjub ya sanar da Yahanasu cewa’’kunce masa tayoyin mota akayi’’
Dan sam baya so kowa ya sani ba tare da ya gama sanin abun yi ba.
Hankalin Yahanasu ba k’aramin tashi ya yi ba ga shi ya ce mata ‘’ta yi shiru ta tsaya tukunna kar a fara investigation sai ya gama deciding akan ‘zai d’au mataki ko ba zai d’auka ba’ tukunna ’’.
Sai da yayi da gaske tukunna ya kawar da batun yana daya sanin gaya mata dan in da ace ya san haka zata d’aga hankalinta to da shiru zai yi.
Cikin son kawar mata da tunanin ya sake sako maganar auren nasa,ta fahimci abun da yake son yi shiyasa kawai itama ta d’an sake ta biyemasa ba wai don fargaba tashin hankali tare da tunanin abun sun barta ba.’’

Ahankali Yashjub ya fesar da numfashi ya shiga tunani’’abu ya kankama sai shirye shirye akeyi amma shi matsalarsa d’aya
bai san ya za su kaya da shi da amaryar tashi ba dan a cikin kwana biyun nan ya lura gaba d’aya a k’ule take da shi
jiya kamar za ta yi masa kuka wai kaff su ya Musbah da inna gani akeyi kmr auren takeso da wuri shiyasa ta bada number Ya Musbah da wurwuri
ita dai gaskiya in b….!.

‘’Inaga gara mu ci gaba da had’a kayan ni da su Ummi ko?’’
Muryar Yahanasu ta katsewa Yashjub tunani.

Girgiza kai kawai Yashjub yayi
kafin yace ‘’karki damu,suma za su yi wani abun important,had’a lefe is your job ke kad’ai…’’ har ya d’an lumshe idonshi ya sake kishingid’ewa sai kuma ya bud’e ya kalleta yace’’Yaha!a tunanin ki Kausar za ta iya kasheni??’’

Shiruuu tayi ta dad’e tana nazari kafin ta sauk’e ajiyar zuciya tace’’gaskiya a’a!.
what makes u think that?ta basa amsa tare da jeho masa tata tambayar.

Ajiyar a zuciya ya sauk’e kafin yace‘’it’s just…kinsan na fad’a
miki conversation d’in su da na ji itada Mommy that very day
da attitude d’in ta towards me and everything.Da suka had’u da Manubiya kuma naga tashin hankali a idanunta ba kad’an ba…a ganina a nawa tunanin da nake yi shine’ta ga she doesn’t stand a chance against Manubiya shiyasa ta yanke shawarar ta kasheni kenan kowa ya rasa’ ko ya abun yake??
I’m confused…’’


Ajiyar zuciya Yahanasu ta sauk’e kafin tace’’ka tabbatar
tayoyin kunce su akayi ko?’’

Jin jina kai yayi kafin yace’’I’m certain’’

‘’To ka bari ayi investigation mana Yash’’

Ya jima yana nazari kafin ya sauk’e ajiyar zuciya ya d’an furzar da iska tukunna a hankali yace’’i don’t want to dig up more dirt,as u heard
just now
Daddy yana buk’atar zaman lafiya a tsakanina da Mommy A ganina indai har Mommy za ta iya rufe ido ta goyawa Kausar baya su yi betraying Yassir sannan kuma ta so ta k’ulla aurenta da ni
to I don’t think akwai abunda ba za ta iya goya mata baya blindly akai ba.’’

Dasauri Yahansu tace’’no no no no Yash! Mommy ba za ta tab’a supporting Kausar ta kashe ka ba’’

Cikin tarar numfashi ta yace’’Yeah I know that,
but idan aka fara bincike na san za ta rufe ido ne ta bi bayan Kausar kuma na san ba zata tab’a bari ayi interrogating d’in ta ba.
Ni kuma in dai haka ta faru to daga ranar ni da Mommy mun raba gari kenan har abada
saboda I can’t bear inga tana sopporting wanda yaso ya kasheni!.Kinga kuwa babu zaman lafiya kenan kuma ni
kaina nasan na janyowa kaina bala’i ne saboda fushin uwa ma kad’ai fitina ne ballantana kuma ince zan raba gari da ita.’’
Wata zazzaafar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya ci gaba da cewa’’like I said’i don’t want to dig up more dirt’.
I’ll just have to be more careful from now onwards,sannan inshaaAllah zan zauna da ita lafiya,I think i’m just gonna have to live with the fact that ‘mahaifiyar da ta haifeni bata wani damu da ni ba!’,sam ban yi sa’a ta wannan fannin ba.’’

Ahankali Yahanasu ta sunkuyar da kanta k’asa muryar ta na d’an rawa cikin
son kwantar mishi da hankali da kawar mishi da tunanin tace
‘’Komai zai yi daidai komai zai gyaru,it will be okay,we all will be okay.’’

‘‘InshaaAllah’’yace
Daganan duk sukayi shiru

Sunanan zaune family d’in driver suka zo,dan haka ya mik’e ya fita…shi bai samu zuwa har k’auyen ba Daddy da wasu dribobine suka zo asibitin suka bi mutanen har chan kauyen da baifi tafiyar mintuna talatin ba inda za’a yi masa sutura achan a binne sa.

Bai dad’e da dawowa d’akin ba likita ya shigo ya sake duba sa,daga nan yayi masa allurar bacci.

Ba shi ya tashi ba sai da su Ummi suka dawo itada Munirat
da abinci nik’i nik’i.

Yaji zafin rashin ganin su Ya’isha
amman kamar yadda su Daddy suka ce dukda ya san ba su fi sa gaskiya ba amma shima kawai sai ya bar abun akan sun ji haushin fifita Yahanasu da yayi akan su ne shiyasa suka yi fushi da shi if not wallahi wannan attitude d’in da suka bashi da sai ya nuna musu origin d’in attitude tunda basuda kunya.

Sallah ya fara yi tukunna ya ci abinci kad’an da taimakon d’uren Yahanasu.
Ranar Yashjub ya bawa su Ummi mamaki dan ba su yi
tunanin yana magana har haka ba,abu d’aya da suka fahimta tashi d’aya shine’in dai
kana buk’atar yayi maka hira sosai da fara’a to ka sako maganar Manubiya,
dan haka suka samu abunyi
haka suka dinga hirarta dama suma abunda suke so kenan.
Ya kuwa ji dad’in yadda suke k’aunar Manubiyan tun kafin su ganta
Babban burinshi a yanzu shine
su Mommy ma su k’aunaci Manubiya kamar yadda su Ummi suke k’aunar ta.
Tabbas ya na son y’an uwanshi ko ba komai jininshi ne su,bai san wanne kalar shed’an da sabon iskanci ne ya shiga kwakwalwarsu suka fito da wannan shirmen ba but it definitely has to end,bai
damu da wacce hanya zai bi ba ta lallashi ko ta k’arfi
iyakar abunda ya sani shine ‘it has to end’!.
….
Dakyar Munirat ta rabu da shi ta hak’ura dan da itama cewa ta yi sai an kira Manu ta gaishe ta.Shi kuma Yash baya so ya kira ta sai zuwa gobe gudun kar ta ji muryar sa somehowta fahimci ba shi da lafiya dan baya so ma ta sani balle hankalinta ya tashi.

Yahanasu ta so ta kwana da shi amman ya tubure akan shi ba Yaro bane kuma ai ciwon nashi is not that severe
Ba yadda suka iya haka suka hak’ura suka shirya suka tafi.

Suna zuwa gida
Yahanasu ta turo masa wani a cikin masu gadin su,shi ya zo ya kwana da shi.


A b’angaren su Manubiya kuwa,ganin abun ya fi k’arfinsu kuma ba yadda za suyi ne ya sanya su ya Nafi’u suka samu dattijawan layin akan maganar su Uncle.
Dakyar kuwa aka samu aka shawo kan su Baba habu da Uncle da
kaka mallan wanda yafi kowa zak’ewa akan sai su Baba sun tashi a gidan…..da kyar suka
hak’ura bayan an yanke an kuma ja layi
Akan
‘Babu ruwan kowa da kowa
Kuma ko kallon banza su Manubiya suka sake yiwa wani a cikin yaran gidan
to sai sun fuskanci shariah.’

Gaba d’aya in kaga Baba sai ya baka tausayi,ya zama so silent ko a wajen meeting d’in ma ‘’To’’ kawai ya dinga cewa.
Ko bai fad’a ba tashi d’aya in ka kalle shi zaka fahimce
Abunda su Uncle sukayi masa
ya girgizashi matuk’a……..hiyasa na zauna a doguwar kujerar baya…..’’MANNUBIYA
(Book 2)
Page 03
Na
Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.

Yassir yana fita daga asibitin,direct gida ya nufa dan yana buk’atar ya ganewa idanunsa wanne hali
Kausar take ciki.
It’s either tana chan ta b’oye kanta tanata kuka ko kuma dai bata damu da Yashjub d’in ba shiyasa bai ganta a asibitin ba….

A b’angaren Kausar kuwa sai yanzu ta samu maganin baccin da ta sha ya sake ta.Dan haka ta mik’e ta nufi toilet,tana cikin wanke fuskarta ta fara jiyo muryar Baaba Larai a cikin d’akin nata tana cewa’’Kausar wai baccin uban me kike yi ne haka tun d’azu…’’
Dan haka ta yi maza ta k’arasa wanke fuskar tata ta fito.
‘’Lafiyarki kuwa??’’
Muryar Baba Larai ta katse mata tunanin da ta fito tana yi,ahankali ta d’an sauk’e ajiyar zuciya kafin tace’’na d’an sha maganin bacci over dose ne
shiyasa har yanzu kaina yake juya wa’’

Girgiza kai Baba Larai ta yi kafin tace’’Ni dai ince,na ga ban ga kin fito an tafi da ke ba’’

‘’ina?’’
Kausar tayi mata tambayar cikin katseta.

‘’Yashjub ne yayi hatsari shine aka tafi asibiti tun d…..’’

Da k’arfi Kausar d’in tace’’what!!!’’sai kuma ta tafi luuu za ta fad’i.
Dasauri Baba Larai ta tarota a rikice tace‘’relax,ba abunda ya same sa sai gocewar k’ashi kawai a hannu,amma Baba Iliya kam an amsa kira’’

Ajiyar zuciya Kausar ta sauk’e
da kyar ta k’arasa bakin gadonta ta zauna kafin tana haki da kyar ta samu ta iya cewa ‘’ba shi yake driving d’in ba kenan?’’sai kuma ta sake mik’ewa ganin tana shirin zubewa yasa tace’’Baaaba d’an rik’e ni jiri nakeyi,bari in je asibitin ki zo ki taya ni sauk’a’’.

Matsowa Baba Larai ta yi ta rik’eta sannan tace ‘’ki nutsu su Mommy sun kirani yanzu suma suna hanya,ki nutsu sosai mu jira ta dawo tukunna..’’

Cikin fushi ta hankad’e ta tace’’ Baaba kin san me kike fad’a kuwa ?
In nutsu kmr ya?Yashjub ne fa ba lafiya yana kwance ya yi hatsari shine kike ce min wani in nutsu??’’.

‘’Shikenan.Bismillah’’
Baba larai tace da ita da ga haka ta juya ta fita.

Yassira Kausar d’in ta kira dan ta tambayeta sunan asibitin amma kamar yadda Baba Larai tace mata itama Yasirar haka ta ce ta yi hak’uri ba sai ta je ba suna hanya suma akwai d’an case dan haka in aka ga ita ta je abun zai rinchab’e,and just so she should know yanzunnan suma Yasmeen take ce musu ta ji a bakin likitan yana cewa wa’enda suka kawo
su Yash d’in sun ce wai kamar kunce tayoyin motar tasa akayi.’’

Tashi d’aya hankalinta ya sake tashi ko sallamar da Yassira tayi mata batajiba
ji tayi kawai ta kashe wayar.
Zato zunubi amma tunani da zarginta tashi d’aya akan Yassir ya dira dan in ba shi ba ta san kaf gidan babu wanda zai yi wannan aika aikar tunda dai su babu wanda ya ke shigo musu gida,besides in ba black snake wanda suka tab’a yin fad’a da Yash d’in ba ta san Yash bashida wani abokin fad’a,yo yaushe ma ya dawo k’asar dududu.
To amman mai yasa Yassir zai yi haka
saboda kishi ko me?tabbas dama ta san yana zargin ta bai gama yarda da ita ba amma sam ba ta yi tunanin abun na sa ya kai har haka ba.
Dan haka dole ta tashi ta d’au mataki saboda al’amarin na Yassir ya fara zama wani abun daban…ba ta riga ta tabbatar ba amma muddin ta gama tabbatarwa shi ne to fa ba za ta zauna ta zuba masa ido
tana gani yake wasa da rayuwar Yashjub ba,shirmen na sa ya yi yawa……
A hankali Tana Jin kanta yana wani irin mahaukacin sarawa
ta nemi guri ta kwanta ta lumshe idanunta a take hawaye suka shiga sintiri akan farar fuskarta har ga Allah ba ta san yadda za ta yi da Yassir wanda ya zame mata k’adangaren bakin tulu ba,ga shi ba ta Isa ta yi wani abun ko ta tunkare sa da maganar ba tunda ta lura abunda ya ke expecting daga gareta kenan.

Tashi d’aya ciwon kanta ya sake hauhawa in banda sarawa ba abunda kanta yake yi shiyasa ta yi shiruu ta kwanta ta lumshe idanuwanta ……….
Ba ta dad’e da gama waya da su ba suka dawo gaba d’ayansu,kafin kowa ya shiga inda take Yassir ya shiga shiyasa su Yasira suka wuce d’akunan su kawai.


Yayi mamakin ganinta a kwance hankalinta kwance
amman dai fuskarta ta kumbura tayi jaa which means kuka tayi,k’arasawa yayi inda take ya d’an zauna a gefen gadon a hankali yace ‘’Kausar’’

Dakyar ta samu ta danne zuciyar da ta ke yunk’uro mata..a da da farko ta san tana son Yassir,da Yashjub ya dawo gaba d’aya sai ta ji Yassir ya fita a ranta dan tashi daya k’aunar Yashjub ta ci k’arfin komai a zuciyar ta,a yanzu kuwa tabbas

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login