Showing 60001 words to 63000 words out of 244445 words

Chapter 21 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16481

mik’e suma suka bi bayanta.Suna fita su Yadira ma suka fice.
Za’a fara maganganu da gulmace gulmace
Iya ramma ta yi sauri ta mik’ar da Manubiya ta nufi k’ofa da ita,ganin haka yasa Umman su Siyama ma ta mik’e haka ma
su Yahanasu.

Su Maman Baraka sun shiga
wajen Amaryar uncle basanan akayi show d’in,labari kuma yana zuwa musu da suka fito lokacin suka tarrar har an fito da Manubiya,sun so sun tarar sun ganewa idanunsu…..sallama suka yiwa Amaryar uncle suka bi bayan y’an kai Amarya,kar a yi babu su.

Babu yadda Manubiya bata yi ba amman haka tanaji tana gani suka hanata shiga wurin Inna wadda tun d’azu ta lura ta fita daga parlourn,ba tare da sun barta ta shiga d’akin nasu ba aka yi waje da ita aka saka ta a mota tanata kuka kamar ranta zai fita,Mata kuma sunata rangad’a gud’a!.

Yahanasu tana fitowa daga gidan su Manubiya ta d’au waya ta kira Yashjub….duk abunda su Yassira suka yi saida ta kwashe kaff ta gaya masa komai har abubuwan da suka faffad’a akan gadon Manubiyan d’azu da rana sai da ta fad’a masa.
Ran Yashjub idan yayi dubu tou yau ya b’aci shiyasa ko gama sauraronta ma bai iya yi ba ya kashe ya kira Yasira ransa a masifar b’ace yace mata”kar ta kuskura ko da wasa ta k’arasa masa gida!tunda mahaukaciya ce ita to ta kad’a kan ragowar mahaukatan su wuce gida in suka kuskura suka je masa gida wallahi sai ya ba su mamaki,Iyakar b’arnar da suka yi masa ya Isa haka kuma hakan ma su jira zuwansa gobe zai samesu they will answer to him…”

Tabbas yau mai rabata da Yahanasu sai Allah dan tashi d’aya ta san itace ta gaya ma Yash! Abunda basa so kenan
gashi kuwa tun yanzu ya fara korarsu yana cewa ‘kar aje masa gida’.

Sun kusan Isa gidan lokacin da ya kirata,haka nan tana ji tana gani ta kira Yasmeen da Ya’isha ta zaiyyane musu tace”su juya akalar motocin su su nufi gida,Ida suka isa gidan sai a tattauna,sai da suka yiwa Ya’isha da gaske tukunna ta yarda ta yi reserve dan da cewa ta yi wallahi sai ta je,haka dai ta hak’ura ta nufi gida tana jin kamar ta kama da wuta dan bala’i…..

Guiwa a mugun sace sannan zucyoyinsu fal takaici da bak’in ciki suka k’arasa gida Yasira tana ji tana gani next step d’insu ya tafi a banza dan akwai abunda ta kuma shiryawa za su yi a gidan Amaryar……


Maman Siyama da Iya ramma ne a gefe da gefen Manubiya,sai Maman
Aisha a gaba.
Kukan da takeyi sai da ta bawa kowa tausayi,Yassir kam wanda shine ya d’auki amaryar ba k’aramin mamakinta yake yi ba,dan shi bai yi tunanin Amare suna kuka har haka ba besides ita da za ayi mata gata!ita da za a
d’auketa daga wannan garbage d’in a kaita aljannar duniya ga kuma mijinta miji kmr Yashjub ta samu amma
shine take wannan kukan!…..shiyasa gaba d’aya mamakinta ya rufe sa ya shiga
tunani da kuma san ya nemo
ko dai akwai wani dalilin da ya sanyata kuka….
“Mu je”
Muryar Iya ramma ta katse masa tunani. Jin jina kai kawai ya yi daga haka ya kunna motar ya danna double signal,ragowar na gabansa da bayansa suna ganin haka suma suka tashi motocinsu da suka cika taff da jama’a suka sanya double signal suka fara k’ok’arin barin layin…..

Komawa ciki Siyama ta yi domin taje ta taho da su Jidda dan ta lura ba su fito ba.
Sir Najeeb sam bai yadda ya bud’e motarsa a kowa ba,ba ya so Siyama ta hango sa ta k’i shiga kuma ba ya so a cika motar dan bai shirya d’aukar kowa ba sai su d’in,shiyasa ya ji dad’i sosai da ya ga har an fara tafiya su basu riga sun tafi ba.Dan haka ya gyara motar tasa a dai dai k’ofar gidan.
Babu irin neman da Ya’isha ba ta yi masa ba….shi kam ya ganta sarai amma ya manna mata!dan tana d’aya daga cikin reasons d’in da ya d’auko mota mai tint kuma da ya zo d’in ya sake jin takaicinta dan tun daga farkon zuwan su har kawo yanzu da aka fito duk yana kallonsu,ba k’aramin haushi ta sake basa ba da yaga kalar shigarta!kayan jikinta da kuma yadda ta rufa mayafinta a iyaka kai
gaba d’aya jikinta a bud’e gashi ta yiwa lace mai mugun tsada d’inkin fitted gown matsattse har da tsaga a baya,a rayuwarsa ko bai san mace ba sam ba ya so ya ga ta yi irin wannan shigar.

Yana wannan tunanin yaga su Siyama sun fito ita da Jidda har da Munirat. Tsayawa kawai ya yi yana kallon yanayin shigar ta simple and cute so breathtaking!.
Yana kallonsu suka bud’e har motoci biyu amma babu guri.
Haka kawai dama Siyama ta ji motar datake fake a k’ofar gidan bata burgeta ba,ganin ana shirin wucewa a barsu
yasa taja hannun Jidda suka nufi motar,sai a lokacin ya sauk’e ajiyar zuciya.Bai ji dad’i ba da Munirat ta bud’e gaba ta shiga,ya so Siyaman ce ta zauna a gaba…tana shiga tace “laa!Ya Najeeb Ina wuni.”

“Alhamdulillah”kawai yace a hankali ba tare da ya kalleta ba dan baya so Siyama da take shigowa yanzun ta fahimci shi d’in ne.
Tana shiga ta rufe ta juya ta kalli Jidda tace “Da ikon Allah motar kuma empty ma”
Yana jin ta rufe k’ofar ya sa lock ya kunna motar dai dai itama ta fahimci ashe shi d’in ne dan gefen fuskarshi kawai ta kalla ta gane shi.Da sauri ya kunna motar ya bi bayan convoy d’in.
Yana ganin ta tana ta k’ok’arin bud’e k’ofar amman ta kasa,dariya ta basa dan yadda ya ga ta had’e rai ba kad’an ba ta burgesa,abunda ya kasa fahimta guda d’aya shine idan ta samu ta bud’e k’ofar motar shin fita za ta yi kenan a haka yana cikin tafiyar ko yaya?…..Murmushi ne ya sub’uce masa wanda duk saida suka ji,daga nan ba wanda ya yi magana haka suka d’au hanya motar shiruu
a haka har suka k’arasa gidan amarya Manubiya,dan already Yassira ta sa Yassir ya gayawa ragowar ba sai an je gidan Mommy an gaida ita ba direct kawai a wuce gidan amarya.
….
Ko da su Yasira suka fito daga motocinsu babu wadda ta iya cewa k’ala har Baba larai,hakanan suka nufi cikin gidan kowa da abunda take sak’awa a cikin ranta…..ba k’aramin dad’i suka ji ba da suka hango Daddy zaune a main parlourn k’asa yana kallo,tashi d’aya Ya’isha ta k’ak’alo hawaye ta k’arfi da yaji,ganin haka ya sa su Yusra yin kalar tausayi suma,yanayin su kawai Daddy ya kalla ya fahimci akwai matsala shiyasa ya kafe su da idanuwa har suka k’araso suka shiga gaishe sa,bai amsa gaisuwar ba sai tambayarsu da ya shiga yi akan “mai ya far?”.
nan kuwa suka zauna suka shirya masa k’arya da gaskiya…
A haka Mommy ta sauk’o ta samesu,ba k’aramin dad’i taji ba da ganin yadda Daddyn ya fusata matuk’a….ya na jin jina maganar tana kuma yi masa zafi…ta ya ana bikinka zakace ‘k’annenka kar su kai Amarya’har wani ‘kar suje masa gida’!.Tabbas da sake
dan ba zai yiu ba,dole ya san abunyi!,bai aurowa d’an sa wadda zata raba masa kan ya’ya ba ba wallahi…!

Hatta Baba larai zagewa ta yi suka yi ta shirya labarai ba kunya ba tsoron Allah dan ta san Daddy ba zai yi titsiye yace zai bi diddigi ba shiyasa suka shirga k’arya kala kala
kuma duk a bayanin nasu suna yi ne akan wai misunderstanding suka samu su da k’annen amarya shine Yashjub ya bi bayan k’annen matarsa har ta kai sa ga hanasu zuwa kai amaryar.

Sai da suka tabbatar Daddy ya hau ya zauna daram!tukunna
kowacce ta zame ta wuce
ciki.
Dukda bak’in cikin dake k’unshe a cikin zuk’atansu game da auran da Manubiya da Yashjub d’in kansa sai da suka ji kamar su taka rawa,dan a yadda suka ga yanayin mood d’in Daddy
sun san gobe akwai case!!!!

Direct d’akin Mommy Baba Larai ta wuce,a tsaye ta same ta kamar yadda ta yi zato…tana shigowa ta k’arasa inda take tace”Ya ake ciki”
Tiryan tiryan Baba larai ta zaiyyano mata yadda suka yi na k’akarin ganin sunyi ammman Yahanasu ta kafa ta tsare ta hana a yi komai….”

Dab’ass!!!
Haka Mommy ta zauna akan gado ta yi shiru kawai dan ta ma rasa me zata ce.

Ajiyar zuciya Baba larai ta sauk’e kafin tace
“Ki yi hak’uri wallahi d’azu shiyasa da suka zo chanja kaya na k’i yarda in shigo
saboda banaso in baki mugun labari….so na yi idan aka tafi kaita ko da ace ta riga ta shiga gidan ne in samu in yi dan da babu gara ba dad’i to sai kuma Yash d’in ya hanamu kai amarya.
Amman kar ki damu,na hango mana wata hanyar da za mu iya bi cikin sauk’i mu yi nasara a kanta,shiyasa ma kika ga na hawo da kwarin guiwa ta.”
Ba ta jira jin me zata ce ba ta d’aura da cewa”Yanzunnan yanayi da mood d’in da Daddy ya shiga daga jin bayanin su Yassira ya sanya na fahimci idan akace Yashjub da matar sa su dawo cikin gidannan da gudu zai yarda…Daddy yana son Yash matuk’a na san ba yadda zai yi ne shiyasa tun farko ya barsa ya je ya tare a wani waje daban amman in ta shine bai k’i su zauna a nan a bangaren Yashjub d’in ba kusa da shi tunda akwai space……yanzu a yadda na lura da shi ya fusata all we need to do shine mu kuma d’aura sa akan ‘idan ya yi sake to Manubiya da y’an uwanta za su kwace masa d’a!’,ke kuma sai ki tado da maganar dawowar ta su nan,daganan inshaaAllah za ki ga yadda al’amari zai chanja,ni kuma daga nan zan karb’i aikin kuma muddin ta dawo nan d’in wannan karon kam InshaaAllah bazamu samu failure ba.Dan zaman ta a kusa da mu kamar k’arshen ta ne…”

Ita dai Momy da “to”kawai ta bi Baaba larai dan ba kad’an ba ta ji haushi kuma ta tsorata da ta ji tace “ba su yi komai ba”a ganinta tunda har basu yi d’in ba kuma ga abunda ita kanta baba larai d’in ta fad’a da farko akan abun to fa babu wani abu da zasu yi daga baya wanda zai yi tasirin da za su samu nasarar cire Manubiya a gidan….da sauri ta kawar da tunanin gudun ma kar tunaninta ya tabbata dan idan ya tabbata bata san kuma ya zata yi ba….cikin son bawa kanta kwarin guiwa ta d’aura gaba d’aya hope d’inta akan zancen dawowar Manubiya da Yash kusa da su.Sannan tana addu’ar Allah ya sa kar Manubiya ta samu ciki kafin ta dawo cikin gidan da zama...
Tana cikin wannan tunanin ta ji Baaba larai tace”sai kuma maganar Yahanasu itama ya kamata asake..”
Dasauri Mommy ta katseta ta hanyar cewa “Larai mu bar maganar Yahanasu tukunna”
Cikin tarar numfashi ta Baba larai tace”She is out of control
Yahanasun da na sani ko
shegen duka su Yassira sukayi wa Manubiya bai kamata ace ta yi magana ba,kar fa Yarinyar nan ta zo ta yi miki b’aramb’atama wata rana.!”

Kallon da taga Mommy tana yi mata ne yasa ta had’iye maganar ta ta kasa ci gaba da cewa komai.
Ahankali Mommy tace
“Dan girman Allah ki yi min uzuri akan case d’in Yahansu Larai,ko me za ta yi kiyi min alk’awarin za ki tsaya akai mu gyara b’arnar da ta yi kawai
dan abunda kike tunani bazan iya sake bada goyon baya akai ba…na ga illar hakan!.
A ganina Yahanasu k’aramin alhaki ce a halin yanzu da ke kanki kin san idan ba mu tsayawa kanmu ba komai mai iya faruwa ne,dan haka mu ajjiye batun Yahanasu a gefe mu yi focusing akan abunda yake most important.”

Ajiyar zuciya Baba larai ta sauk’e kafin ta mike tsaye
tukunna ahankali tace “inshaaAllah,as u say…sai da safe.”………
…..
Motar Najeeb ce ta k’arshe
shiyasa basu samu damar yin parking a cikin gidan ba,sai
a waje a bakin titi.

Yana sane ya k’i bud’e side d’in Siyama,ita kanta ta fahimci shine ya k’i bud’e mata dan tare suka fara kokawar bud’ewa ita da su Jidda
amman duk na su ya bud’u nata kuma shiru.
Ganin tana ta bawa kanta wahala ne ya sa ta hak’ura
da niyyar Jidda na fita itama za ta bi bayanta ta fice.
Munira ce ta fara fita
Tace”mun gode”
Da murmushi ya amsata dan ba k’aramin farin ciki yake ciki ba dramar Siyama burgesa takeyi yadda ta had’e rai ta chuno baki abun ba k’aramin dad’i yake yi masa ba.

Jidda tana da sauk’e k’afafunta k’asa ta juyo ahankali cikin nutsuwar ta tace masa”Mun gode”daga haka ta sauk’a a motar.Ganin Siyama har ta matso tsakiya yasa ya yi
sauri ya juya ya sa hannun sa ya janyo murfin motar yana me cewa “Ba komai Jidda”
Yana dariya k’asa k’asa yana kallon Siyaman,bayan ya tabbatar ya sake saka lock a duk k’ofofin.

B’ata rai ta yi sosai kafin tace”
Zan fita”.
Murmushi ya yi tukunna yace
“Ashe Inada aiki a gabana sosai ni ban saniba,dan handling mace mai kishi
Is not an easy task!”.
Da sauri ta d’ago ta kallesa
sai kuma ta kau da kanta kawai.
Ganin tak’i cewa komai ne yasa yace “Amman naki yayi tsauri sosai,ya yi yawa pls a d’an rage,atleast a bani chance inyi explaining kaina”.
Cikin tarar numfashinsa tace
“Ni fa ba kishi nake yi ba besides i just knew you,yau kad’ai fa na sanka ta ya zan yi
kishi??infact ba wani abu a tsakanin mu!,kuma na riga na sani
Ya’isha girlfrnd d’inka ce
Ita zaka aura kowa ya sani…bai
shafe ni ba sannan It’s fine
dan kayi hugging d’inta saboda ba hurumina bane
tsakanin ku ne ku da ubangijinnku,so pls dan Allah ka daina cewa ina kishi saboda babu komai tsakanina da kai sai mutuncin da muka yi a iyaka yau!
Ba ruwana da relationship d’inka Kai da Ya’isha!
Bud’e min k’ofa in fita
Pls.”
Ta fad’i hakan tana mai sake matsawa kusa da jikin k’ofar dan ta samu ya d’auke hannunsa yanzu.

Ya d’an ji zafin yadda ta ce”ba ta kishinsa amman sai ya kawar yace
“Okay!In yi miki tambaya guda d’aya zaki amsamin?”
Kamar ba za ta ce wani abun ba sai kuma ta d’aga masa kanta alamun ‘yes’
ba tare da ta kalleshi ba.

Sai da ya sake juyowa ya fuskanceta sosai kafin yace
“D’azu,you were nice to me,amman tunda kika ganni da Ya isha ki kalleni ma aiki ne a wajenki kuma it’s obvious haushina kike ji,ta ya zaki yi min explaining hakan ba a matsayin kishi ba?.”

This time around murmushi ya ga ta d’an yi…tabbas idan ba ta yi da gaske ba to mutumin nan ba barinta zai yi ba and there is something about him wanda ta san idan har ba ta yak’i ta fatattaki tunanin sa da shi kansa daga rayuwarta ba
tou tabbas akwai matsala…kar ta je ta jangwalowa kanta abunda ba za ta iya ba dan haka ta d’ago ta kallesa kafin tace”Bana kishinka!like I just said ban ma sanka ba ballantana har in shak’u da kai
wanda shak’uwa ce za ta janyo abunda zai sanya in yi kishin naka,kawai dalilin da ya sanya ka ga Ina avoiding d’inka shine har ga Allah I’m sorry to say sam ba na shiri da Abota ko kirki ba na yadda in yi da Namiji irinka.”

Shiruu ya d’an yi kafin yace “Namiji irina?,menene ni d’in??”.
Itan ma sai da ta d’an yi shiru tukunna tace”Masu double dating!waenda a fuskar duniya ake yi musu kallon mayaudara!”.

Kamar zai fashe da kuka yace
“Siyama ni ba mayaudari bane ba,can you pls allow me to explain myself…”

Cikin katsesa kanta tsaye tace”a yadda ka karb’i number na da kuma yadda kake treating d’ina throughout today,da ni da kai duk munsan inda zancenka zai sauk’a,bayan kuma ka riga ka san kana da wadda za ka aura
wadda kake so itama take sonka.Menene hakan kake shirin yi min idan ba yaudara ba?

Ko mata biyu zaka aura a lokaci daya?besides na san ma itan zaka aura tunda itace type d’inka ni kawai a side kake da shirin ajjiyeni ka b’ata min lokaci”

Da sauri ya ce “in dan za a bani zab’i ke zan zab’a ke kad’ai!”
Da sauri ta d’aga masa hannu tace “Plss…dan Allah,banaso in ci gaba da gaya maka maganganu masu zafi
saboda despite abunda kayi
min still Ina respecting d’inka,na cire kunya na cire komai na gaya maka abunda yake raina da abunda na fahimta a kanka
which is the thruth
therefore dan Allah inaso ka fita hanya ta kwata kwata.
Bana son case da su Ya’isha
bawai tsoron ta nakeji ba amman duk inda nakai ga iya fad’a bazan iya had’a kaina fad’a da mutanen da basusan darajar d’an Adam daidai da kwayar zarra ba.
So pls
For the last time
Ka fita a hanya ta
sannan ka bud’e min k’ofa in fita.”

Shiruu kawai ya yi ya tsura mata ido…bai ma san me zai ce ba bai san ta Ina zai fara fita a hanyar tata ba,shi da yake son shiga cikin rayuwarta tashi d’aya tace masa ya fita a harkarta ma gaba d’aya which is the last thing da zai iya yi arayuwarsa,dan shi kansa ya san ba zai iya rabuwa da ita ba he’s sure of that,ba ta san yadda ya dinga fama da soyayyar ta sama da wata uku ba,ba zai iya yi mata alk’awarin fita a harkarta ko rabuwa da ita ba dan ya san ko ya yi alk’awarin to ba za ya cika ba.

Ahankali cikin son ta fahimce sa yace “Siyama ba zan iya rabuwa da ke ba,ki yi hak’uri ki fahimce ni ki bani chance ba zan tab’a yaudararki ko in cutar da ke ta ko wacce hanya ba,I promise!”

Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace “me ye tsakanin ka da ita
Ya’isha?just the truth!
dan Allah”

Sai da ya lumshe idanunsa ya bud’e tukunna yace
“She s my girlfriend”.

Yadda kalmar
‘She’s my girlfriend’
ta daki k’irjin ta
Ita kanta sai da ta yi mamaki.
Da kyar ta iya cewa “kuma har yanzu kuna tare ko?”

Still sai da ya d’an runtse idanunsa na y’an sakanni
tukunna ya bud’e yace
“Yea!but Siyama wallahi ke
nakeso kuma ba wai double dating zan yi ba,soon zan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login