Showing 150001 words to 153000 words out of 244445 words
yi su Yasira tun suna magana da suka ga su Siyama da Manubiyan sun k’i sake wa sai kawai suka d’aga k’afa suma suka yi shiru.
Suna a haka suna jimami Ya Nafi’u ya kira su Jidda yace”mutum biyu su fito a bar mutum d’aya a gidan za su wuce gida su fara tartara kaya an sallami Baba..
Siyama aka bar mata,Jidda da Muhsin kuma suka tafi dan idan zai yiu a yau suke so su tashi daga gadon k’aya su koma sabon gidansu dake a gandun albasa wanda Yashjub ya basu.Ba su yi ma tunanin za a sallami Baban yau ba da tuni sun yi parking d’in.
Ita Aisha Mama Anty Umma da Inna ne suka tartare komai kafin dare sun kammala komai ya Nafi’u da Muhsin kuma su sakayi ta zirga zirgar kai kaya a motarsa da motar kai kaya.
Sai da suka gama kammala kai komai gidan tukunna suka d’auko Baba daga asibiti suka nufi tsohon gidan nasu dan su je su yiwa su Uncle sallama saboda Baba dagewa ya yi yace”shi fa sai ya yi musu sallama.”
Suna zuwa Baba da Ya Nafi’u suka nufi wajen su Uncle d’in Inna da su Mama kuma suka nufi wajen matayensu.…yunwa Jidda ta ke ji dan ba ta tsaya taci abinci sosai ba,shiyasa ta je kitchen ta d’aura ruwan zafi da niyyar ta je ta siyo milo da madara ta sha tea…
Sai da gabanta ya yanke ya fad’i sakamokon k’amshin turaren da hancinta ya fara jiyo mata,a take a ranta tace “nooo..it can’t be,ta ya ma zai shigo nan.”daga haka ta mik’e bayan ta gama saita murhun ta juya za ta fita ta ga mutum a tsaye kyam!…..
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”tace a fili kafin ta d’an d’ago wayarta ta d’an haska dan ta samu ta tabbatarwa kanta da shi d’in ne…
Suna had’a ido ta fashe da kuka tace”dan girman Allah ka fita Ya Al’ameen kar ka janyo mana masifa”
Ahankali ya yi taku d’aya ya matso gareta muryarsa har tana d’an karkarwa yace”D’azu na ji Mama tana gaya wa Ammi cewa za ku tashi…”
Cikin sharar hawaye tace”eh,mun ma tashi..dan Allah ka fita…”
A hankali yace”Jidda ni da ke fa?ba za ma ki tsaya ki ji uzuri na ba?tun safe nake ta faman zirya Ina lek’en gidan nan Jidda duk dan saboda ke amma kora ta ma kike yi?”
Bai jira jin amsarta ba yace”a lokacin da na tafi,wallahi wallahi tun a kwana biyu da na kirawo wayarki na ji ba kya picking na had’o kayana na biyo jirgi na sauk’a a garin Abuja,inaga cousin d’ina da muka tafi tare da shi ne ya kirawo su Ammi yace musu na taho dan flight d’ina yana shirin boardn zuwa Kano Mahaifina ya kira ni yace idan na zo sai ya tsine mini tunda bani da hankali. Kalar fad’an da ya shiga yi min a wannan lokacin ni kaina na san akwai abunda Ammi ta gaya masa mai muni shiyasa ya yi fushi sosai ya ji haushi dan ko fad’a bai cika yi mini ba.A wannan lokacin babu yadda ban yi da shi ba amma ya k’i saurarona yace in juya in koma. Tun daga ranar ya daina kulani ya yi fushi da ni yace kuma wallahi idan ya ji labarin na zo Nigeria ba tare da na gama abunda ya tura ni ba sai ya bani mamaki yace kuma ko waya na yi miki bai yafe ba. Sai da na dawo tukunna a cikin maganarsa na fahimci Ammi ce ta ce masa saboda ke na rubuta letter na bar course d’in da ya tura ni in yi saboda kince ‘Baba zai aurar da ke a Yusuf idan ban dawo an yi auren da ni ba’.
Jidda Course d’in duk yawansa na san ba zai kai wata hud’u ba shiyasa na hak’ura na yi masa biyayya akan idan na dawo sai a yi komai amma ko a wannan lokacin sai da na saka mai gadin mu ya sa mini ido gudun kar Ina chan Ina shirya ta yadda zan shayo kan iyayena ke kuma a aura miki Yusuf.”
Shiruu ya yi kafin ya d’aura da cewa”wannan shine abunda ya faru Jidda shiysa kika ji ni shiru na san waye mahaifina yana son duk abunda nake so kuma zai tsaya mini a kai amma muddin na yi masa taurin kai na san tsaf za a samu matsala kuma na san halinsa da bin diddigi yadda yace”kar in kiraki wallahi da ace na kiraki sai ya sani ni na san waye shi”” na san kuma ya yi hakan ne saboda ya ga zan yi masa biyayya ko akasin hakan.
Cikin sake yin taku d’aya zuwa gareta yace”I love you!always and forever ba zan iya hak’ura dake ba Jidda gara ma tun wuri ki yi saurin karb’ar uzuri na ki yafe mini mu fara nemawa kan mu mafita!”
Shiruu ta yi a ranta ta ji matuk’ar sanyi da dad’i da ta ji ba banzatar da ita ya yi ba,a fili kuma sai tace”Ya Al’ameen ni kam na dad’e da hak’ura da kai,ka duba fa ka ga Mahaifinka ma ba so yake yi ba tunda shi ne yace kar ka ki…”
Cikin tarar nufashinta yace”noo Jidda wallahi ba da ke ya ke fushin ba da ni yake yi kuma na saboda ya ji batun aurenku da Yusuf ya taso da zai yi wani abun …a ranar da zan tafi a airport na yi masa bayanin komai na ce masa Ammi ba ta so,shi da kansa a wannan lokacin ya tabbatar mini da cewa”inshaaAllah ina dawowa za a yi auren mu kuma kafin ma in dawo za a yi tambaya batun Ammi kuma kar in damu ya san yadda zai yi da ita ba matsala inshaaAllah,but for now in yi k’ok’ari in yi concentrating a kan abunda na je yi saboda it’s very important for our business”
Shiysa da ya ji na shallake sa na bar ma makarantar ya ji haushi ya yi mini haka,amma wallahi ko yanzu Mahaifina a shirye yake ya d’aura mana aure ko a yau!ita ma Ammi ta amince this time for real saboda halin da na shiga ta tsorata ta yi nadama ta gaskiya ba kamar wanchan lokacin ba da ni kaina ban san linke ni ta yi a baibai ba”
Babu wani ragowar reason d’in da Jidda za ta d’aura laifi a kan Al’ameen saidai ta san su Baba ba za su tab’a fahimtarsa kamar yadda ita ta fahimce sa ba,shiyasa kawai ta d’an ja da baya cikin sharar kwallah tace”ka yi hak’uri Ya Al’ameen mu yi hak’uri kawai”
Ta fad’i hakan tana mai fashewa da kuka.
Da sauri ya sake matsowa yana mai cewa “noo Jidda kar ma ki fara cewa mu yi hak’uri wallahi ba zan iya ba”
Ganin sa daff da ita ya sa ta yi sauri ta sake ja baya ita shaf ta ma manta da murhu da ruwan zafin da ta d’aura,shi kuma abunda ya hango kenan dan haka ya yi saurin ruk’ota zuwa jikinsa ganin za ta afka kan murhun yace”careful!wuta a bayanki”
Salatin Ya Yusuf wanda ya hakse su tarr da wayarsa da kuma”Jidda”d’in da Baba yace ne ya fargar da su.
Da wani irin sauri ta ture Al’ameen shima da mugun sauri ya cikata ya matsa ya shiga ambaton”Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
a cikin zuciyarsa
Juyawa kawai Baba ya yi ransa a mugun b’ace ya fice daga gidan yayin da Yusuf ya yi kansu zuciyarsa tana wani kalar mahaukacin tafasa..kamar wani mahaukaci sabon kamu haka ya koma yana zuwa ya rarumi wani k’atoton iccen ya makawa Al’ameen a kai da mugun sauri wanda hakan ya yi sanadiyyar fad’uwarsa a wajen gefen kansa ya shiga zub da jini.
Wata razananniyar k’ara Jidda ta buga ta yunk’ura da niyyar yin kan Al’ameen d’in dake nan kwance kamar gawa amma tashi d’aya itama Yusuf ya d’auketa da wani irin gigitaccen mari ya shak’o ta da dukkannin k’arfinsa ya buga ta jikin bango,dai dai nan su Anty Umma waenda k’arar Jidda ta Isar musu suka afko cikin kitchen d’in,da gudu anty Umma ta k’arasa ta shiga k’ok’arin kwatar Jidda wadda zuwa yanzu idanuwanta suka fara lullumshewa kafin duhu ya maye gurbin ganinta jikinta ya saki a take ta sume a wajen……
A hankali take bud’e idanunta da suka yi mata rauni..dishi dishi ta ke gani kafin ta fara gani da kyau kad’an kad’an..ba ta gama tantance a inda take ba…cikin fushi ta ji Baba wanda ta ga ya juya mata baya suna magana shi da Inna yana cewa”saboda su Uncle sun yi mini abu sai in d’aura karan tsana a kan Yusuf in rufe idanunwa na in k’i in bi bayan gaskiya?fad’a da su Uncle mu ka yi ba da Yusuf ba kuma suna d’in inshaaAllah wata rana za mu shirya amma ki daina saka Yusuf a cikin fad’an mu,ke ko irin karar da ya yi mana ma ba kya gani?wanne d’a ne kika tab’a gani ana fad’a da mahaifinsa amma ya rufe idanuwansa ya bi bayan k’anin mahaifinnasa da ake fad’an da shi? ki duba ki ga yadda ya dinga bin bayan mu a gaban Baba Habu har kusan marin sa fa ya yi suka samu sab’ani duk a ta dalilin mu amma duk da haka ke Yusuf bai kwanta miki ba?…….a da gaskiya na sa a raina ba za ta auri Yusuf ba amma kuma abunda idanuwa suka gane mini yau ya sanya naga dole fa in yi abunda na ga ya kamata a matsayina na ubanta ko so kike mu zuba mata ido Al’ameen d’in ya gama lalatata?ba ri ki ji abunda ba ki sani ba hatta makaranta wasu lokutan shi yake kai ta ya d’auko ta Yusuf ya dad’e da gaya mini hakan,ido kawai na zuba mata dama ina jiran ranar da zan kamata tana kulasa ashe abun nasu ma ya zarce misali!…”
Cikin kuka inna tace”yanzu zargin Jidda kake yi ba tare da ka tsaya ka ji bayanin ta ba??”
Cikin tarar numfashinta yace”tabbas!tabbas zargin ta nake yi..idan kuma za ki iya gaya mini uban me ta ke yi a ruk’umk’ume a jikinsa a kitchen cikin dare inda ba a tab’a tunanin ganin Al’ameen d’in ba to Ina sauraronki…”
Cikin d’an b’acin rai Inna tace”wallahi zan iya dafa Al’k’urani akan akasi aka samu,Haba Baba Jidda fa?ashe da ma ba ka yi mata sanin da za ka iya shaidarta idan irin haka ta taso ba?sannan kalli fa abunda Yusuf d’in ya yiwa Yarinyarnan har ta kaisa ga sumar da ita amma shine za ka d’auke ta ka aura masa ita? A ganinka hakan dai dai ne?
Sannan idan kace Yusuf a bayan mu yake ka ji ka gani ya zama mijinta me za ka ce a kan baba habu surikinta,wanda hatta yau da ya san tashi za ka yi a kusa da su kuma saboda su bai tsaya kun yi rabuwar arzik’i ba?”
Cikin tsananin fushi Baba yace”na riga fa na gama magana!babu wani abunda ya Isa ya sakani in chanja ra’ayina,na tabbata inda ace Musbahu ne ya ganta a yadda Yusuf ya gansu ita da Al’ameen da shima abunda zai aikata a gareta kenan tunda hakan ne dai dai…to shi Musbahu ya gudu ya yaye kansa da kansa dan hakan idan Yusuf ya hukunta Jidda a matsayinsa na yayanta hakan bai zama laifi ba….”
Cikin kuka inna tace”ta ya sumar da Jidda ya zama ba laifi ba?”
Da mugun k’arfi Baba yace”Aminatu!!!!!”
Cikin fushi ya d’aura da cewa”ba na son jayayya ki barni in ji da abubuwan da suke damuwa…ba na so in sake fuskantar tirjiya daga gareki,ina umartar ki da ki yi mini biyayya a yi auren nan a gobe a kaita d’akinta idan ba haka ba wallahi wallahi wallahi za mu samu gagarumin sab’ani da ni da ke!”
Yana gama fad’in haka ya juya ya fice…
A hankali Jidda ta mayar da idanunta ta rufe…tana jinta kamar ba a duniyar ba…tunda take ba ta tab’a jin Baba ya d’agawa Inna murya ba sai yau duk a ta dalilin ta…ta na son Al’ameen sannan ta san idan ta auri Yusuf tabbas bak’in ciki ne ajalinta amma kuma inshaaAllah ko alamun tashin hankali ko kuma yunk’urin kare kanta ba za ta yi ba…ta fahimci inna ta yarda da ita ta yi trusting d’inta Manu ma ta san za ta yarda da ita Baba kuma za ta barsa ya aurar ta a Yusuf d’in indai hakan zai sa ya huce,inda rabon wanke kanta wata rana shima zai fahimci ba wani abun suke yi da Al’ameen ba….za ta yi masa biyayya inshaaAllah dan tunda ta fara tirjiya a Yusuf ta nuna Al’Ameen take so babu abunda relationship d’inta da Al’Ameen d’in yake ta janyowa Ahalinta sai masifa………..
Siyama ba ta so kwana a gidan Manu ba amma haka suka tursasa ta gaba d’ayansu abun mamakin har su Yasira waenda suka yi musu k’abe k’abe ko motsi suka yi idanunsu a kansu yake ….su dai su Manubiya kawai sun zuba musu ido ne suna kallon ikon Allah da rashin wayonsu dan wannan rashin wayo ne saboda yadda suke yi kowa ya riga ya san they are up to something shiysa daga Manubiya har Siyama suke ta addu’o’i da neman tsari daga sharrin su…dukda kuwa d’azu Yasira ta bawa Manubiya hak’uri ta ce “ta yi hak’uri akan abubuwan da suka yi mata duk sharrin shaidan ne kuma sun fahimci itace zab’in yayansu ta yi hak’uri inshaaAllah hakan ba za ta sake faruwa ba they wants to start a fresh with her”amma hakan bai sa Manubiya ta yarda da su ba…kawai dai ta bita da murmushi tace mata “komai ya wuce”
Dukda gwaggwo ta zo hakan bai sa sun yi shirin tafiya ba..shima kuma Yashjub bai ce musu komai ba ya rabu da su amma dukda haka idanunsa a kansu yake.
Ko da dare ya yi su da kansu suka tsara cewa’Siyama ta kwana a d’akin Manubiya na da,su kuma za su zauna a d’akin da Yadira ta zauna’.Gwaggo kuma dama tana k’asa d’akin bak’i.
Murmushin yak’e Siyama ta yi dan ta yi tunanin a wajen kwanan ma za su nanik’e musu ne…Yasirar ma gudun kar su ga suna ta manne musu ne ya sanya wannan karon tace a yi hakan.
Sun mik’e kenan kowa za ta tafi ta kwanta wayar Manu ta fara haske a karo na biyar daga zaman su zuwa yanzu,duk tsura mata idanu suka yi sai da ta yi musu murmushi tace”sai da safe”daga haka ta juya ta nufi sama tukunna suma suka wuce d’aki.
Suna shigewa Manubiya ta dawo da sauri ta Isa gaban Siyama wadda ke k’ok’arin shiga d’aki itama tace”Siyama dan Allah ya ake yin blocking mutum,na kasa”
Kallonta ta yi kafin tace”ki duba goggle”kamar ba za ta tambaya ba sai kuma tace”wa za ki yi blocking haka jikinki har yana rawa”
“Abbakar”Manubiya ta bata amsa a tak’aice tana mai daddana wayar hannunta kafin ta d’aura da cewa “ya ishe ni da kira,wai dan Allah yana buk’atar taimakona. Kin san shi kuma Ya Yash ya ce ba ya so ko gaisawa in yi da shi”
Ta faiyyace mata hakan a lokaci guda tana k’ok’arin blocking Abbakar dan har ta gano yadda za ta yi.
Shiruu Siyama ta yi tana tunanin”ko dai ta gaya mata Mahaifiyarsa ce a kwance a gadon asibiti rai a hannun Allah, ta san shi yasa yake ta kiranta.
Ko kuma kawai ta rabu da ita inyaso ita da Jidda sai su san yadda za su yi su karb’i kud’in a hannunta su basa dan ta san kud’i yake so.”
“Done!”
D’in da Manubiya tace ne tana haki kamar wadda ta yi y’ar tsere ya katsewa Siyama tunani.Daga haka Manubiyan tace mata sai da safe ta juya ta haye chan sama.
Sai da Yusra ta ji Siyama ta shige ciki ta rufo k’ofa tukunna ta juya ta nufi su Yasira waenda suka tsura mata ido tana wani irin murmushi….tana zuwa ta zaiyyane musu abunda kunnuwanta suka jiye mata Manubiya da Siyama suna cewa…ji suka yi kamar an yi musu bishara da gidan aljannah!Tabbas Allah ya na son su,saboda dama neman hanyar da za su bi su nunawa Yash kamar Manu ce ta zubar da cikin da kanta suke yi yanzu kuwa Yasira tana jin wannan batun tashi d’aya ta san abun da ya kamata ta yi dan haka ta cewa su Yusran gobe duk runtsi su yi ta kwak’umarta har sai sun ga password d’in wayarta daga nan kuma sai su nemi number a wayr tata,saboda ita gobe za ta fita office…Yadira tana da kwakwalwa shiyasa tashi d’aya tace mata d’azu dai da yake ta kira ta ga number 090443 ne farkon number k’arshen kuma ba ta gani sosai ba
”Ba damuwa,Allah ya sa ba ta yi deleting history d’in ba idan muka d’au wayar time d’in kawai za mu duba na san lokutan da ya kikkirata ai”
Cewar Yasira.
Cikin tarar numfashinta Yusra tace”ko ta goge ma ni na san inda zan shiga in dubo,Allah ya kaimu goben da rai da lafiya.”
Baba larai suka kira suka sanar mata sannan suka d’aura da cewa”Sun fara zuba abubuwan da ta basu a duk abincin gidan,sannan ba za su samu matsala wajen jefa mata tablet d’in a ruwa ta sha ba saboda lucky for them ba ta shan bottle water ko na dispencer iyaka ruwan borehole kawai take iya tara a cup ta sha sakamokon laulayin ciki shiysa easily d’azu tana ajjiye cup d’in kafin ta je ta dawo suka jefe mata kwayar ba tare da sun farga ba daga ita har Siyama,to dai da ta dawo ta d’an yi sip biyu daga nan ta ajjiye maybe taste d’in ne ta ji ya chanja mata shiysa suka yanke shawarar raba kwayar gida uku saboda kar ta gane,to dai a halin yanzu sun zuba mata a gorar ruwanta na borehole uku da ta tara ta saka a fridge za ta dinga sha…”
Murna a wajen Baba larai abun ba a cewa komai..ji take kamar ta zuba ruwa a k’asa ta sha…kafin tace”amma Yasira cctv fa?”
Dariya ta yi tace kar ki damu Baaba ba zai tab’a ganewa ba ta cikin fridge d’in muka saka kuma ba direction d’in cctvn take kallo ba…murmushi ta yi tace”MashaaAllah Alhamdulillah,Allah ya ci gaba da taimakon mu”
daga haka ta mik’awa Mommy,itama duk da tashin hankali da fargabar Daddy sai da ta yi farin ciki matu’uka ta yi