Showing 210001 words to 213000 words out of 244445 words

Chapter 71 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16417

aikin muka gwada in banda wasu sabbin masifu a kan na da babu abunda muke gani a tauraron Yassir amma ita d’ayar Yarinyar lafiya lau dan zuwa wannan lokacin mun fahimci twins ne.

Kamar kullum a wannan lokacin ma Baba larai ce ta kawo shawarar’mai zai hana mu yi hak’uri mu taushi zuciyoyinmu mu raini Yashjub tunda shi zai yi albarka in ya so idan ya girma ya gama tara abunda ya tara sai mu San yadda muka yi muka d’aura Yassir a kan dukiyar sa shi kuma mu kashesa komai ya dawo hannun mu in ya so sai Yassir ya kula da komai tunda ba Yassir d’in ne ya fara tara wa ba ta san komai zai tafi cikin sauk’i abun zai yi albarka dan shi Yassir d’in abunda ya fara ne dakansa ba zai yi albarka ba.inshaaAllah komai zai yi kyau.
Sannan idan hakan ta faru babu batun wulak’antacciyar mutuwa a Yassir tunda a yadda ta gani sai idan ya rasa komai ya rasa kowa tukunna wannan al’amarin
zai faru da shi.

Ko kad’an ban yi mata jayayya ba dan nima plan d’in ya yi mini d’arr bisa d’ari.
Dan haka muka tashi muka tsaya tsayin daka na danne zuciyata na ja Yashjub a jikina na kula da shi duk dan saboda y’ay’ana sai dai kuma tun lokacin da Yashjub ya kai shekaru 5 a duniya na fahimci kamar ma ya tsane ni!sam ba ya son magana ma da ni ba ya son shiga jikina baya jan y’an uwansa a jiki…
Gashi duk ciki mahaifinku ya fi son shi
Daga k’arshe ma Hajiya mama ta d’aukesa gaba d’aya ya koma wajenta…na so ya dawo a wannan lokacin amman a banza dan yadda Hajiya mama ta ga na d’aga hankalina na san shiyasa ita kuma ta ce ba zai dawo ba.

Yashjub tun yana zuwa mana
hutu sau 2 a shekara daga baya ya koma sau d’aya ko
bayan shekaru biyu daga k’arshe ma ya daina sai dai Daddy da su Yassir su je ni kuma a lokacin mun yi kacha kacha da su Hajiya mama tace idan ta ganni a inda take sai ta yi mini abunda ban tab’a tsammani ba.

Tun Yashjub yana shekaru 17 na so ya fara saka su Yassir d’in a jikinsa da suka girma suka yi wayo nan ma na yi masa maganar ya fara saka shi a business d’insa amma ya k’i na zo nace to ya bashi jari nan ma ya k’i gashi a lokacin na fahimci son kan da Daddy ya kuma yi a share na company d’insa shima
gashi shi Yashjub d’in ba ma ya nan ballantana in san yadda zan yi in yaudare sa ya ja d’an uwansa shi kuma asiri bai cika tasiri a kan sa ba kamar Khadija
Hankalina ba k’aramin tashi ya yi ba da na ji kishin kishin d’in Na’ima ta ce wa Yassir Yashjub take so dan dukda cewa na san mun cire masa son mata da sha’awar su a rai amman kuma na san in dai har Na’ima ta gayawa su Daddy tana son shi tofa dole ya aureta kuma yau da gobe sai Allah na san duk abunda muka yi dole wata rana Na’ima ta iya samun ciki…Shiyasa muka k’arawa abun namu k’aimi gaba d’aya ya kuma tsanar mata sannan muka fara aiki a kan ya dawo a yi ayi ya d’aura Yassir da Yassira a kan komai na dukiyar sa mu samu mu kashe sa dan na yiwa kaina alk’awarin jinin khadija bai Isa ya rayu ya ji dad’i har ya yi aure ba,saboda yadda Yashjub da mahaifiyar sa suka d’aga mini hankali he don’t deserve to live
That is my revenge….


Kwatsam!! Sai kuma tauraruwar mace ta fara b’ullowa wadda Baba larai tace ita za ta kawo
k’arshena muddin muka bari aka yi auren….
Yo dama ai ko ina hauka Yash bai Isa ya yi aure ya haihu ya ji dadi sannan Yaro ya shigo cikin gadon sa ba….ga kuma maganar matar ma ta zo har da su kawo k’arshena shiyasa na tsani kuma bata son Manubiya kamar mutuwa ta!

Ajiyar zuciya Mommy ta sauk’e kafin ta kalli Yahanasu tace”yanzu na san kin fahimci dalilina na aikata duk wani abunda na aikata kuma inda ace ba na sonki ko ban d’auke ki a matsayin jinina ba Yahanasu da ba zan tab’a zama in faiyyace miki komai in bud’e miki cikina kamar haka ba!!
Na san na yi laifi na san na yi kuskure amma Daddynku shine ummulaba’isin komai da na fara aikatawa sannan da tafiya ta yi tafiya na san kin fahimci saboda Yassir da kuma ku na aikata ragowar abubuwan da na aikata.
Sannan Manubiya had’ari ce ga rayuwata shiyasa ya zame mini dole in….”

Cikin tarar numfashinta Yahansun tana wani irin kuka kamar ranta zai fita tace”Mommy babu ruwan Mannubiya da duk wani abu da ya sameki da kuma yake shirin samunki Ubangiji ne ya fara nuna miki k’arshenki!!…”
Wani irin abu ne ya rik’e mata zuciya da mak’ogaro dan haka ta yi shiru numfashinta ya tsaya da kyar ta samu ya dawo ai kuwa tashi d’aya ta mik’e ta kamo hannun Mommy ta fara janta sai da suka isa bak’in k’ofa tukunna ta bud’e ta had’e hannuwanta waje guda tace”dan girman Allah ki fita,ki fita kafin ki sa zuciyata ta buga!!!!”

Tabbas Mommy ta fahimci tarkon ta ya kama kurciya Yahansu ba za ta iya yin komai ba kamar yadda take ik’irari kuma yadda ta bud’e mata cikinta ta fad’a mata sirrin ta ta san hakan ma sake k’ulle Yahansun ta yi da jijiyoyin jikinta dan haka ba za ta iya yin komai ba.
Shiyasa kawai ta shafa fuskarta a hankali ta d’an goge mata hawayenta daga haka ta sa Kai ta fice hankalinta a d’an kwance dan tun d’azu da Yahansu tace’ guilty conscious zai addabeta idan ta fad’i abubuwan da ta aikata aka hukuntata’
Ya sanya ta fahimci all she needs to do shine ta sake nunawa Yahanasu itan fa itace mahaifiyarta kuma tana sonta daga nan ta san za ta yi silencing d’inta shiyasa ta bud’e mata cikinta saboda tana so ta ga ta yarda da ita kuma ta d’auke ta y’a.
Kafin ta gama fita daga shock ta dawo dai dai ita kuma InshaaAllah kafin nan da lokaci k’ank’ani za ta san yadda zata da su Daddy za ra san yadda zata yi
distroying d’insu gaba d’aya ta kawo k’arshen su kar ma su sake bata ciwon kai



Mommy tana fita da sauri Yahanasu ta mayar da k’ofar ta rufe k’irjinta yana dukan tara tara dan bayaga haushi da takaici har ga Allah zuwa yanzu kam tsoron Mommy take ji Anya kuwa Mommy tana da zuciya a cikin k’irjinta??ita da Baba Larai anya kuwa za su ga Annabi?ashe dama akwai mutane irinsu har yanzu a duniya?
A da ita tana jin haushin Mommy saboda abubuwan da ta yiyyi ashe ba ta ji duka ba ba ta san duka ba!!!!
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
Ta shiga ambato a cikin zuciyarta kanta yana wani irin sarawa…tabbas kamar yadda Mommy ta yi zato a yadda ta zauna ta bud’ewa Yahansu cikinta hakan ya sanya Yahanasun ta d’an ji d’arr sannan kuma ta yarda Mommy ta d’auke ta a matsayin y’a!!
Ba wai ta yafe mata abubuwan da ta yiyyi ba kawai dai hakan ya sanya ta sake fad’awa cikin duniyar tsoron tona mata asiri saboda ta san guilty conscious ba zai bartaba no matter what uwa uwace gara kawai ta barta Ubangiji ya nuna mata iyakarta…
Ba za ta sake da ita ba ba kuma za ta kula ta babu ruwan kowa da kowa kamar da dan tabbas Mommy ba uwar da zaka sake ka yi mu’amala da ita baceba,she is everything Bad!…..


Sai da Baba larai ta yi sati d’aya tukunna Mommy ta basu izini suka fara nemanta sai dai kuma babu kalar kiran da ba su yi mata ba amma wayarta ba ta shiga kuma sun kira k’auyensu ance bata je ba dan haka hankalinsu ya tashi matuk’a.


A b’angaren Kausar da Yassir kuwa ko da yayi mata maganar aurenta da Yashjub nuna masa ta yi itama ba ta so kuma ta yi abunda ta yi ne saboda ta yi tunanin Yash d’in zai fara bata wani abun daga cikin dukiyar sa ko ya ba ta gida ya ce ta zauna a inda za ta je d’in…amma ita sam ba ta yi tunanin su Daddy za su yi musu aure ba.Dan haka ya taimaka ya taya ta nemo Yash ya sauwwak’e mata ita kam aurensa ba ya cikin plan d’insu.
Sai da Yassir ya nuna mata b’acin ransa na k’in tuntunb’arsa da ta yi kafin ta yi abun ita kuma ta basa hak’uri tare da alk’awarin ba za ta k’ara ba tukunna ya yi mata alk’awarin nemo Yash a duk inda yake ko ta message ne a samu ya sake ta…Hakanan suka rabu daga shi har ita babu wanda ya san ba aure ma tsakanin Kausar da Yashjub d’in.
Bayan kwana biyu ta san yadda ta yi ta bincika wayarsa ta d’auki number mutanen nan masu evidence ta b’oye numberta ta tura musu message tace”su turawa Yashjub da duk wasu mutanen da suke neman wanda ya yi aika aika a Estate d’in Yashjub za ta basu ko nawa ne.”

Saboda ita har ga Allah Yassir ya ishe ta kuma ta san idan ba kama sa aka yi aka kashesa ba to tabbas ba zai barta ta sakata ta wala ba.



Abuja su Manubiya suka fara zuwa kafin su gama shirye shiryen tafiya….sai bayan sati biyu tukunna suka isa Copenhagen Denmark suka yi settling
Cikin rarrashin da tsoron shiga Hakki ta shiga k’ok’arin fahimtar da shi cewa “ko ba komai fa Kausar matarsace!!”

Har ga Allah sai da ya yi mata bayanin da shi kansa sai a cikin jirgi da kwakwalwarsa ta d’an huta tukunna ya tuna sannan itama ta tuna tabbas fa da gaske babu aure tsakanin Kausar da Yashjub saboda ba a d’aura aure da ciki!!
A ranar tsakanin Manubiya da Yashjub ba za a ce ga wanda ya fi wani murna ba……daga nan suka kawar da duk wani b’acin rai suka shiga shimfid’a rayuwarsu mai dad’i a Copenhagen dan basu ga ranar dawowaba….


Mommy kuwa zuwa yanzu ta san me za ta yi game da auren Kausar da Yashjub…………MANNUBIYA
(Book 2)
Page 41
Na
Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.

A b’angaren Mommy kuwa zuwa yanzu ta san me za ta yi game da auren Kausar da Yashjub.
Ta riga ta san zuwa yanzu Yashjub ya san babu aure a tsakaninsa da Kausar..kuma ita kanta zuwa yanzu ta san ba ta da lokacin da zata ce sai sun cire Manubiya tukunna za su kashe Yashjub! shiyasa kawai ta ma hak’ura da sake k’ulla auren Yash da Kausar d’in a karo na biyu.
Ta dai ji Daddy yana cewa Ummi”Kausar d’in tana a matsayin matar Yash a idanun duniya har zuwa lokacin da za ta haihu.Gudun b’acin suna.”
So ita kuma kafin nan da zuwa lokacin da Kausar d’in zata haihu inshaaAllah barinta zai cika kud’irinta zai cika kuala ta san barin Kausar d’in ma da aka yi a mazaunin matar Yash d’in Allah sai nuna hanyar da za su yi taking advantage d’in hakan inshaaAllah..
Kawai ita yanzu wuyarta ta san inda Baba Larai take,she really needs her yanzu kam saboda ta riga ta gama tsarawa akan duk bala’i wuyarta Yashjub da Manubiya su sako k’afa a cikin k’asar Nigeria wallahi sai ta ga bayan su!!
Dole a yita ta k’are abun ya yi yawa kuma anzo gab’ar da dole ta yi musu hakan cikin gaggawa idan ba haka ba kuwa to tana cikin masifa!!!!
Zuwa yanzu idanunta sun rufe..as far as she knows Ita da Yassir suna cikin gadon Yashjub dan haka ba sai ta wani jira sun yi abunda suka yi an mallaka masa dukiya ba,iyaka kason da za su samu ma idan an raba gado ya isa!
Daganan su kuma su Daddy da Ummi da su Hajiya Mama duk za ta saka su a saiti InshaaAllah ta san me za ta yi musu,gara kawai a yita ta k’are……
amma kuma rashin sanin whereabout d’in Baba larai babban fullstop zai sakawa mission d’in nata saboda Baba larai d’in ce za ta yi komai tun daga kan dawowar da take so suyi da gaggawa har mutuwarsu.


Tsakanin Mommy da Yahanasu sam ba jituwa kwata kwata Yahanasun ta k’i yarda ta ba ta chance har y’an gidan sun fara lura da yadda Mommyn take binta ita kuma tana kaucewa…
Mommyn har da ce mata “InshaaAllah za a karya abunda aka yi mata a samu ta yi aure!”
Ita kuwa Yahanasu tace”dan girman Allah kar su karya komai!
su barta a yadda ta ke ta yi Imanin Ubangiji ne kad’ai zai iya yin ikonsa a kanta.”
Kamar yadda Mommy ta yi zato Yahansun ba ta tona mata asiri ba ammafa tun daga wnanan ranar ko had’a hanya Yahanasu ta daina yarda ta yi da Mommy,k’ofar d’akinta kuwa kullum a rufe.
…..
……Wata d’aya wata biyu tun su Mommy suna d’aukar b’atan Baba Larai abun kamar wasa har suka zo suka fara tsorata dan yau kwana sittin kenan babu ita babu alamarta wayarta ba ta shiga gashi suna tsananin buk’atarta dan Ya’isha ta d’aga musu hankali akan auren Najeeb da Siyama gashi Yash da Manubiya babu su babu dalilinsu ba ma ta jin za su dawo bikin,Yassir kam ya sake tab’arb’arewa company d’in da Yash ya bud’e masa ma ya tashi a aiki Hatta building d’in nasa ya sayar motocinsa masu tsada ma ya siyar kuma har yau ba a san Ina yake kai kud’in ba..
Kausar kam ba k’aramin Namijin k’okari take yi wajen danne zuciyar ta game da shi ba gashi mutanen da ta addaba da kira a kan su tona masa asiri a samu a kashe sa ta hutu!sun daina sauraronta kamar waenda ya yi musu tsafi!
A fannin lamarin Yash kuwa ita kad’ai ta san me take going through ta kira sa ta yi message amma duk baya shiga ba ya tafiya tsabar bala’i har depression ta kamu da!
da kyar ta samu ta nutsar da kanta ta ke shan magani ganin tana shirin haukacewa!!
Inda ace babu aurenta a kan Yash ya yi wannan dogon zangon da baza ta tab’u sosai ba
amma wannan zumar da aka lasa mata a baki aka janye shi yafi komai haukatata!!
……saboda Allah ace ranar da ake shirye shiryen kai ka gidan Miji mijin ya gudu kuma har yau bai dawo ba!(dan ita har yau ba ta san ba matar Yashjub bace ba ita.)
Dukda wannan bala’in da take ciki amma tana namijin
k’ok’ari wajen rik’e kanta da controlling kanta,zuwa yanzu ba ta da komai against su Mommy amma haka kurum take jin she can’t share matsalarta da su she can’t trust anyone anymore….. abunda Mommy ta yiwa Baba larai ma ya sanya Kausar d’in ta d’an tsorata da Mommyn,ta ja jikinta sosai
Doctor d’inta dai yace mata hakan sign ne na depression d’in da ta kamu da shi saboda ta yi going through a lot a rayuwarta da yawa shiyasa ba za ta iya sake trusting kowa ba(ta zama so secretive)sai dai sam ita ba ta wani yarda ba,ta fi raja’a akan kawai dai shekarunta da suka ja ne suka sanya ta yi wayo ta zamo silent ta kuma koyi rik’e sirrinta.
A kaff y’an matan gidan har ma da Mommyn babu wanda ya lura da cewa ba ta ma da lafiya saboda kamar yadda take cikin masifa hakanan suma kowa a cikin masifar take!
Su Yasira zuwa yanzu rashin aure ne matsalarsu dan auren Yadira da suka ga ya taho gadan gadan ya sake uzzura musu son aure a cikin zuk’atan su especially ma Yasira da ta fissu shekaru sai dai kuma ko talakan saurayi babu mai shi a kaff cikinsu,Ya’isha kuwa tata damuwar daban ce dan ji take muddin Najeeb ya auri Siyama a gaban idanunta to kuwa sai ta mutu!!!
Mommy kuwa nata tashin hankalin ya fi na kowa dan itama rashin auren nasu yana damunta amma ba kamar yadda komai ya rinchab’e mata ba!!
Ta ko’ina babu haske babu sauk’i babu nasara……Kausar d’in ma da ta shirya akan za ta yi mata Abu da Yashjub a kan Daddy gashi yanzu babu auren,kuma a yadda take ganin Daddy kwana biyun nan in dai ba irin wannan aikin aka yi ba tabbas akwai gagarumar matsala.

Da kyar ta samu ta dake ta sanarwa Kausar d’in da su Yasira babu fa maganar aure dan tausayinta take ji gara kawai ta sani ta cire hope,aikuwa ranar duk dauriyar Kausar kasawa ta yi,sai da suka yi sati d’aya a asibiti tukunna ta dawo dai dai da kyar ta fara gane waye a kanta.
Dole ta sanya Mommy ta fito mata a mutum ta ce mata kawai ta hak’ura da Yashjub!!!
Ta yi trusting d’inta sannan ta taimaki kanta ta cire Yash a ranta zuwa yanzu ya kamata ace ta fahimci zuciyar Yash ta Manu ce,dan haka dan Allah ta hak’ura kawai!
Tana cikin masifa gashi babu Baba Larai dan haka dan Allah ta ajjiye komai a gefe ta tashi ta tsaya mata
she should stand by her side as her only realative ta tsaya mata ta taimaka mata akwai labarin da zata bata amma ba yanzu ba sai nan gaba.
Ta ajjiye batun soyayya haka ta taimaka mata ta rai da tsira ake yanzu dan duk abunda ya sameta to itama ya sameta farinciki da nasara ko kuma akasin hakan…sannan su Daddy sun ce har ta haihu a idanun duniya tana a matsayin matar Yashjub ne…InshaaAllah a tsakankanin nan Ubangiji ta san zai nuna musu hanyar da za su bi komai ya tafi musu dai dai.”
Ita dai Kausar tace mata “to” ne kawai amma bata gama fahimtar inda zancen nata ya nufa ba sakamokon bala’in da take a ciki,ita kanta yanzu kam ba ta san ta Ina za ta b’ullo ta sake zama mata ga Yashjub ba!!she can’t believe gaba d’aya hard work d’inta ya tafi a banza kenan???inaa da sake!.



Har yanzu babu Munirat babu labarinta Ummi ta kuma zama abun tausayin Hankalinta gaba d’aya a tashe!
Daddy ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login