Showing 87001 words to 90000 words out of 244445 words
dai baka da ikon koro su…in har kuma kace za ka yi taurin kai to zan sa ka had’omin spare key na kaff gidan naka in rabawa ko wanne a cikinsu….
Ban d’aura auren da zai tarwatsamin kan ya’ya na ba wallahi.!”
Yana gama fad’in haka ya mik’e ya ce
‘’a kiyaye” daga nan ya wuce sama.”
Shiruu Yashjub yayi ya ma kasa cewa komai
Har sai da Mommy tace
“Sai magana ta uku!Yadira ta had’a kayan ta tun d’azu
In kun zo tafiya ku wuce da ita
za ta zauna a gidan naka for sometimes.”
Saida ya lumshe idanunsa ya bud’e tukunna ya ce
“To Mommy ba damuwa,amma jiya na gaya miki za mu tafi Cyprus..y not a bari sai mun dawo t….”
Cikin tarar numfashinsa tace
“Ka wuce da ita,idan kun zo tafiya sai ka dawo da ita in kuka dawo sai ku koma tare da ita”
Ahankali yace”Mommy, jibi ne ai…”
Cikin fushi tace
“Ka san Allah Yashjub in ka gwada min taurin kai idan bance ku tafi honeymoon d’in tare da ita ba ka chanja min suna..”
Shiruu ya yi kafin ahankali ya ce “Shikenan Mommy..ki yi hak’uri”kafin ya kalli Yadira ya ce “Ki d’auko jakar ta ki yanzu zamu wuce.Bari in yi wa Daddy sallama”
Ya fad’i hakan yana mai hayewa sama.
Murna a wajen Yadira ba a magana…tashi d’aya itama ta yi wuff ta haye ta je d’auko kayanta.
Ko da Yashjub ya je wajen Daddy basa hak’uri yayi sosai
tukunna dakyar ya samu ya d’an sauk’k’o bayan zazzafan warning d’in da Daddyn ya zuba masa akan “indai har yanaso su zauna lafiya da shi tou ya ja k’annen sa a jiki…duk ranar da aka ce ya mutu shi ne Uba!…kar ya biyewa mace ta rabasu tun yanzu.”
“InshaaAllah”kawai Yashjub d’in ya ce daganan yayi masa sallama suka rabu lafiya
A ranshi yana mamakin yadda Daddyn yayi masa sannan yadda suka d’auki laifi kachokam suka d’aura akan Manubiya wadda bata ji ba bata gani ba
It’s like kamar ma Daddyn har ya fara jin haushinta ne tun kafin a je koina kawai dai bai nuna masa bane but ya fahimta dan tunda har Daddy yace “har Kausar sai Manubiya ta gaida ita ai abun babu sauk’i dan duk mutumin da Daddy zai yi favoring Kausar akan sa to yakamata ayi gaggawar gyara tsakanin su
Shiyasa kawai ya hak’ura yake ta basu hak’uri…ya san su iyaye ne fushin su garesa masifa ne sannan kuma yasan yanzu yana yin taurin kai ko ya yi wata maganar to Manubiya zai sake janyowa bak’in jini a wajensu.
A d’akin Yahanasu Yadira ta samesu dan haka suka fara shirin tafiya.
Manubiya ce tace “tana so ta je ta yiwa su Mommy da Ummi sallama”dan haka Yadira da Munirat suka tafi rakata.
Suna fita Yahanasu tace
‘Ayi hak’uri Yash
ayita hak’uri…d’azu Ina kitchen naji mommy tana waya da su
Yassira suna ajjiyewa na ji ta kiraka dama tun daga nan na san akwai matsala aikuwa da suka tashi shigowa kusan dukkansu da kuka suka shigo
wai ka kore su k’annenta kuma suna gidan yanzu haka.
Dama yadda na ji Mommy da su suna yiwa Daddy bayani shi kuma yana fad’a na san kawai ya riga ya hau shiyasa ban saka Baki ba.
Na yanzu ya faru sai a kiyaye gaba dan Allah Yash karka basu k’ofar da zaka janyowa baiwar Allah n nan bak’in jini a wajen Daddy…”
Ajiyar zuciya ya sauk’e daganan yace
“InshaaAllah’’
Ba a wani dad’e ba su Manubiya suka dawo
Sark’ar gold Ummi ta bata y’ar k’arama wadda ba za ta wuce 4OOK ba a cewarta ta ajjiye a tunanin ta za’ayi bud’ar kai ne sai ta bata tou kuma ashe su basa bud’ar kai…daga nan ta d’an yi mata nasiha.
Mommy kuwa sallama kawai sukayi daganna suka fito Manubiya tana mamakin yadda yanayin fuskarta ya chanja dan d’azu sam ba haka ta yi mata ba a gaban Yash.
Yash yaji dad’in gift d’in Ummi matuk’a kuma bai ji dad’in rashin ganin gift daga wajen Mommy ba yana sane ko a lefe ma ba ta basa komai ba Mom da Hajiya mama sai Yahanasu ne kawai suka bada…dukda ya san yau d’in ranta a b’ace yake
amman ai dama Uwa tana tanadan gift d’in amarya a irin wannan ranar ko da ace ta bayar da na lefe,ya san maybe za suce ai ya yi komai ya saka komai amman ai Ana bada gift ne saboda karramawa ba wai dan babu ba.
Har mota Yahansu da Munirat da Yassir suka rakasu da Yadira da akwatunan ta biyu.
Sai da suka ga ficewarsu tukunna suka nufi main door,
signal kawai Yassir ya yi wa Munirat daga nan Yahanasu bata san inda sukayi ba ita dai ta ganta ta shiga parlourn ita kad’ai.
Kausar tana ganin ficewarsu ta windown d’akinta ta koma ta kwanta ta fashe da wani irin kuka babu abunda yafi b’ata mata rai irin yadda yake wani rik’e mata jaka yake bud’e mata murfin mota.
Tana kwance tana ta faman kuka a haka ta ji an bud’e k’ofar d’akin an shigo.
Ta san Mommy ce dan haka tace ‘’I’m fine”
Murmushi Mommy tayi ta nemi guri ta zauna a kusa da ita kafin tace”Ki yi hak’uri Kausar
saura d’an k’an’kanin lokaci
nasan da ciwo amman ki k’ara hak’uri…
Ki duba kiga yanzu da ikon Allah Daddy ya fara karkatowa side d’inmu duk abunda muke so shi yakeyi.
Shima Yashjub d’in ki duba kiga ni ko b’acin raina ba ya son gani ai da ba haka yake ba.
Ki kwantar da hankalinki na yi miki alkawri indai kina da ni bazakiyi kuka ba…”
Ahankali ta tashi ta zauna tana kallon ta tace”thanks for everything Mommy,but na ga suntafi da Yadira kenan ba ranar dawowarta nan gidan kwana kusa kenan?idan fa ba ta dawo ba babu ta yadda za ayi mu…”
Cikin katse mata magana
Mommy tace
“Kar ki damu zata dawo
komai a hankali a keyi
ki kwantar da hankalin ki kinji”
Ahankali Kausar ta jin jina Kai daganan ta matsa ta kwanta a jikin Mommy tana mai sauk’e wata nannnauyar ajiyar zuciya.
Mommy tana so ta fad’a mata zancen tafiyar su Yash honeymoon amma kuma bata san ta Ina za ta fara rarrashinta ba dan ita kanta tun jiya da ya gaya mata ta rasa Ina za ta sa kanta…she just hope Yadira ta yi abunda ta tura yi a gidan…inshaaAllah in dai har ta yi to ita Manubiyan ce da kanta za ta tarwatsa batun tafiyar tasu.
Suna fita Daddy ya sauk’e ajiyar zuciya dan shima yana tsaye ta window yana kallonsu har suka fice….ya san he s a little bit hard akan Yashjub b
amman kuma idan bai yiwa tufkar hanci da wuri ba tou tabbas akwai matsala.. duba da yadda ya Yash ya kori k’annensa ranar da aka je d’auko amarya dukda ya san laifin su Yasira ne but a yadda shi da kansa ya rok’esa sannan ya ce su had’a kawunansu sam bai yi tunanin Yash zai sake korar su daga gidan sa ba,baya ga haka kalli yadda yake nan nan da Manubiya ya san zafin soyayya ya san ya mutum yake ji shiysa ya fahimci indai har bai tashi ya tsaya a kan Yash ya yi masa wuta wuta ba to a yadda ya rikice a kan Yarinyar tsaf zai yi fatali da zumunci ya zab’i soyayya……MANNUBIYA
(Book 2)
Page 23
Na
Humayrah Bulama
Mikiya Writers Association.
Ahankali ta juyo tace
“Dan Allah ku shigo mana”.
Yana shirin yin magana Yashjub d’in ya k’araso shima yana d’an murmushi yace “bismillah,amma dai next time ba sai na ce ka shigo ba gaskiya”.
Duk murmushi sukayi banda Ya Musbah wanda hankalin sa ya tashi da ganin yanayin Manubiya dan ya tabbatar da kuka ta yi kukan ma ba na wasa ba dan gashi hatta kan hancinta yayi ja!……
Anan parlourn k’asan suka nemi guri suka zazzauan
tukunna su Jidda suka shiga gaida Yashjub cikin girmamawa da mutuntawa.
Da kulawa ya amsa yana tsokanr Muhsin da d’an lukuti
kafin ya amsa gaisuwar Aisha da y’arta daganan suka gaisa cikin mutunta juna shi da su Ya Musbah.
Yunk’urawa Manubiya ta yi tace “bara ta kawo musu ruwa” da sauri Ya Musbah yace “A’a sauri fa mukeyi”
Aisha ce ta kalli Yashjub tace
ga gara nan mun kawo da kayan zak’i,Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya.”
Murmushi Yashjub yayi kafin yace”kun dage dai Aisha,har da wannan wahalar itama?. wannan fa duk bidi’a ne”
Sai kuma ya ce”An gode!haka ake cewa ko?”
Ya yi musu tambayar yana kallonsu.
Duk dariya sukayi kafin su fara mik’ewa da niyyar tafiya,da sauri yace”Au wai dama da gaske kuke?tafiya da wurwuri haka kamar ana korar ku?”
Wayar sa ce ta d’auki k’ara dan haka ya yi excusing kansa ya matsa gefe domin amsa kiran Mommy.
Yana wucewa Manubiya ta d’ago kai ta kalli Aisha wadda har yanzu bata zauna sosai ba tace”Wai da gaske tafiya zakuyi haba mana”
Ta fad’i hakan kamar zata fashe da kuka.
Murmushi Aisha ta yi ta na shirin yin magana muryar ya Musbah ya katseta jin yana cewa”Manu, kuka kikayi ne?”
Saida ta sunkuyar ta kanta k’asa na d’an lokaci tukunna ta d’ago ta kalle sa tace “A’a”
Sai kuma hawaye sharr suka b’alle mata a take kamar an kunna famfoo.
Cikin rashin jin dad’i Aisha tace
“Kinga dalilin da ya sa mukeson tafiya kenan!
Yanzu dan Allah in ya dawo ai sai yayi tunanin mu muka ce wani abun ko.Taya zaki sa kuka haka
So kike ki janyo mana bak’in jini?”.
Zuwa yanzu Ya Musbah ya tamke fuska tamau tsabar takaici!duk rashin hak’urin Baraka sai da ta yi wata goma sha d’aya a gidansa tukunna ta fara kuka a ranar sunan mai sunan baba dan ba’a yanka mata rago da tunkiya ba instead an yanka iyaka rago.
Amman shi kalli k’anwar sa ko sati d’aya ba ta yi a gidan miji ba amma har ta fara kuka!ba ma hawaye ba.
A hankali ya mik’e ya k’arasa inda take ya zauna a gefenta
yana jin tsananin tausayin ta yana ratsashi,cikin nutsuwa ya bud’e bakinsa ya fara magana”Manu ko ma menene ya faru ki yi hak’uri kinji ko?ki daina kuka,
haka auren yake sai hak’uri..”
Ajiyar zuciya Ya Nafi’u wanda ya ke shirin tsaida Ya Musbah ya sauk’e dan a tunanninsa tanbayar ta Ya Musbahn zai kuma yi akan ‘mai akayi mata’
amman sai yaga yayi lissafin manya dan haka ya d’an ji
sanyi aranshi saboda shima ba kad’an ba ya ji ba dad’i game da yanayin da suka tadda Manu d’in a ciki.”
Dakyar Ya Musbah ya sake cewa”Mun so mu d’an zauna amman kukan nan naki ya koremu”
Da sauri ta dag’o kanta ta shiga goge hawayenta tana cewa “Allah na daina”
Murmushi yayi yana mai jin inama ace yanada ikon da zai iya goge mata koma wanne irin takaici ne yake addabar zuciyarta haka.Sai da ya sauk’e ajiyar zuciya tukunna yace”Next time idan mun zo sai ki yi k’ok’arin k’in yin kuka ko?idan har ba ki yi ba sai mu zauna,kin ji?”
Ya fad’i hakan cikin d’aga mata gira d’aya.
Dai dai nan Yashjub ya k’araso wajen, tun d’azu ya gama waya da Mommy amman ya kasa komawa wajen su..tun da yake bai tab’a jin kunya da nauyi irin wannan ba,dan tun d’azu tun da ya d’ago ya ga Manubiya tana kuka ya ji wata kalar kunyar ta da nauyin su Ya Musbah sun yi masa kawanya.He’s not supposed to make her cry,ever!.
Yana k’arasowa Ya Musbah ya mik’e ya k’arasa inda yake ya mik’a masa hannu,da kyar
duk su biyun suka k’ak’alo murmushi kafin Ya Musbah yace “Kayan suna varender anan muka jere su ,mun so mu shishshigo da su har kitchen mu d’an zauna to amman wannan shagwab’abb’iyar matar taka ta kore mu…daga
ganin mu ta hau kuka.
Bara mu wuce
Allah ya sanya alkahairi.”
Wani abune ya tokare k’irjin Manubiya ganin yadda duk cikinsu babu wanda ya damu ma ya tambaye ta me akayi mata sannan kuma bama za su tsaya ma ta gansu sosai su yi hira ta d’an ji sanyi ba,har zasu tafi..ga kuma kishin Kausar da zuwa yanzu haka kurum ta ji ya sake turnik’e ta
dan haka kawai sai ta mik’e da kyar ta je ta yi hugging su Siyama tace “na gode”
daga haka ta wuce sama da sauri mai kamar d’an gudu dan
bataso ta sake sakin wani kukan a gaban su kar su ce sun fasa dawowa next time d’in ma gaba d’aya.
Tun kafin ta kai ga k’arasawa d’akin nata ta saki kuka.
Yashjub ne ya rakasu har mota yana ta musu sannu da godiya da basu sak’on gaisuwa a Baba da Inna,dauriya ce kawai yake yi dan gaba d’aya jin sa yake wani iri duk ba da’di.Sai da ya ga fitarsu tukunna ya kira masu gadi yace su shigar da komai ciki.
Kasa tsayawa ya yi har su gama,hakanan ya barsu anan k’asan ya nufi d’akin Manubiya ransa duk a jagule…ya lura bayan cin fuskar da su Yassira suka yi wa Manubiya da kuma zancen Kausar tabbas akwai shagwab’a da tab’ara a lamarin ta,ya san sai ya yi lallashin da gaske tukunna za ta sak’k’o…gashi Mommy ta kira sa tace “ya zo shi da Manubiya yanzun nan!…..”
Kamar d’azu yanzun ma a zaune ya same ta a bakin gado
tana kuka.
A hankali ya k’arasa inda take ya durk’usa a gaban ta….shi fa bai iya lallashi ba wallahi bai ma san ta Ina zai fara ba!.
Tun lokacin da ya durk’usa a gaban ta gaba d’aya sai ta ji ba dad’i!no mattar what komin takaicin da take ji bai kamata ta bar sa ya d’urkusa haka da sunan bata hak’uri ba dan ta san hak’urin zai bayar.
A hankali cikin sharar hawaye tace”Ka tashi,ba kuka nake yi ba”
Murmushi yayi kafin ya ruk’o k’afafunta ahankali yace “Dan Allah ki yi hak’uri…”
Da sauri ta zamo daga kan gadon ta fara k’okarin kwace k’afar ta tana cewa”Ni dai dan Allah ka daina!babu kyau.”
Y’ar guntuwar dariya ya yi yana kallonta yace
‘’babu kyau miji ya bawa matar sa hak’uri?’’
Cikin tarar numfashinsa tace
‘’A’a babu kyau ka durk’usa kamar haka,dan Allah ka daina kana sakawa Ina jin ba dad’i”
Ta fad’i hakan tana mai goge ragowar hawayen da sukayi saura a fuskar tata.
Cikin kwabe fuska tare da kwaikwayar muryar ta yace
“To ke ba ki san babu kyau ki yi ta kuka kina d’aga min hankali ba?sannan kalli fa a yadda su Siyama suka tafi na san duk hankalin su a tashe yake za ayi tunanin ko har na fara cutar da ke ne tunda daga ni sai ke a gidan.Ni addua ta d’aya ma kar su gayawa su Baba”.
Shiruu ta yi tana sauraron sa
ganin haka yasa ya matso kusa da ita sosai ya tallafo fuskarta a tafin hannun sa yace “Hawayen ki tsada gare su,dan Allah dan Allah Baby ki daina saurin zubar min da su
kalla idanunki gaba d’aya kin wahalar min da kanki ba tare da kin tsaya kin ji kan zancen ba ma.”
Shiruu ta yi kawai ta kasa cewa komai,haka shima yayi shiru ya zubawa kyakkyawar fuskar ta ido…kad’an kad’an ta ji yana matso da fuskar ta ta garesa yana d’an murza gefen kumatunta,ta san inda ya nufa shiysa ta yi saurin mik’ewa ta juya masa baya tana kallon gadon tana mai gyara d’aurin dankwalinta.
Lumshe ido ya yi ya bud’e kafin ya mik’e tsaye ya na kallonta,lokaci d’aya ya saka hannu ya yi hugging nata tsantsan ta baya a hankali ya d’aura kansa a kan dokin wuyanta yana mai shak’ar k’amshin jikinta mai sanyaya zuciya had’i da dimauta sa a ko da yaushe.
Cikin tsananin mutuwar jiki ya ce “ki yi hak’uri ban gaya miki asalin maganata da Kausar ba
dalili kuwa shine a time d’in da na ji maganar sam ban dauk’i abun serious ba shiyasa kikaga ban saka shi a fannin da yake important na rayuwata ba.Dukkannin abunda na gaya miki kika sani game da ni tou shine important duk abunda kika ga ban gaya miki ba tou bashi da amfani shiyasa amma naga kamar rashin gaya miki maganar Kausar d’in yana neman janyo wani labule a tsakanin mu wanda ba zan bada k’ofar hakan ba.”
A hankali ya juyo da ita yana facing d’inta rik’e da k’ugunta ya fara zaiyyano mata yadda ranar ya ji Kausar tana gayawa Mommy ‘tana sonshi’
sannan ya d’aura da cewa”Wallahi Wallahi apart from Kausar d’in da Mommy sai kuma Yahanasu da ya gayawa sam shi bai ma san wani a ciikin su Yassira ya san zancen ba,bai san maganar ta je kunnuwansu ba ta yadda har suke tunanin zai aureta,shi a mazaunin shirme da rashin tunani ma ya d’auki maganar tata shiyasa bai bawa abun importance ba.Amman yana so ta yi masa alfarma d’aya!’ta manta da komai da kowa
ta yi trusting d’insa akan abunda zai fad’a mata yanzu
‘Tun yana Yaro shi tsarin mace d’aya garesa kuma Kausar is the last parson da zai iya aura
saboda kwata kwata jinin sa bai d’auke ta ba tun yarinta,
ko da ace su biyu ne kad’ai suka rage a duniya ba ya jin zai iya rayuwa da Kausar a matsayin matarsa’….’’
A hankali Manu ta sunkuyar da kanta tana jin wani sanyi da nutsuwa yana lullub’eta dan tabbas maganganun sa sun rufe kusan kaso arba’in na damuwarta zuwa yanzu ta fahimci ba b’oye mata yayi ba.
Dukda tana fargaba da kuma kishin yadda Kausar d’in take son Mijinta amman still ta d’an ji sauk’i da ya fito ya gaya mata komai,sannan she has chosen to trust him akan lamarin,kamar yadda ya buk’ata.
Cikin son sake kwantar mata da hankali ya d’ago da fuskarta yana mai kallon kwayar idanunta yace”Mannubiya ce kad’ai a cikin zuciyar Yashjub!Ba ki san yadda kika tare gaba da baya ba shiyasa kike wannan tunanin amma inda ace kinsan yadda kikayi bake bake a cikin zuciyata da ko ni da kaina in nace miki zan k’ara aure ko zan kula wata na san ba za ki tab’a yarda ba
I love you only you no one else!
So idan ma akwai wani tunanin zan auri wata ko zan kula wata a ranki gara ma tun wuri ki cire
saboda wahalar min da zuciyar ki kawai kike