Showing 156001 words to 159000 words out of 244445 words

Chapter 53 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16488

shiyasa gaba d’aya hankalinsu ya sake tashi suka cigaba da addu’a kawai..dan tunda har Yashjub ya sa baki ya k’i yarda to addu’a kawai za suyi ta yi su jira Ubangiji ya yi ikonsa ya ceto rayuwar Jidda.

28 September 1994
….zaune take a tafkeken parlourn gidan da ya ji kayan alatu daban daban…a cikin shekarun da ba su fi hud’u ba Mijin nasu bud’u yake samu ta ko ina Alhamdulillah..sun chanja gida ya gina musu bungalow guda biyu tafkeke iri d’aya a cikin gate da compound d’aya ko wacce da b’angarenta sai kuma boysquaters babba shima a ta gefe…ya siya musu gwala gwalai har motoci ya siya musu guda biyu iri d’aya zani kuwa mafi tsada na wannan zamanin shi suke d’aurawa ita da Abokiyar zamanta!sai dai fa ita duk wannan daula da ake ciki sam hankalinta ba a kwance yake ba zuciyarta babu dad’i nutsuwarta ba ta tare da ita sakamokon juya mata baya da Mijinta masoyinta abun k’aunarta ya yi tun lokacin da ta haihu shekaru hud’u kenan.
Tashi d’aya ya chanja mata ba tare da ta san laifin ta garesa ba.A yadda yake nunawa kamar har yanzu yana k’aunarta tunda yana masifar kishinta har yanzu kishi mai tsanani amma kuma ko kusa da shi baya so ta je..hantara kyara da tsangwama ne kawai yake shiga tsakaninta da shi gashi tsabar kishi ya maida ita kamar prisoner ko baranda ta fita indai mai gadi ko mai wanki wani ya ganta to fa ta shiga ukunta a ranar,hakanan tana ji tana gani Abokiyar zamanta za ta tambayi fita a barta amma ita ba ta Isa ba kitso kawai ta san tana zuwa bayan layi shima tare ita da Abokiyar zamanta.Ita sam ta kasa gane kan Imam kwata kwata dan kamar ma zarginta yake yi watak’il saboda ya san ba ya sauk’e hakkin ta da ya rataya a wuyansa shiysa yake zargin za ta je ta nema a waje…
A take hawaye suka shiga sintiri a kan kyakkyawar fuskarta,shin wannan wacce iriyar rayuwa ce??gashi ba ta da gurin zuwa da ma Imam d’in shine Uwa shine Uba kuma Masoyi a gareta yanzu kuwa abubuwan da yake nuna mata ita kanta ta san kora da Hali ne k’arara yake yi mata,ya gaji ita!
A da tana tunanin ta yi sa’ar Miji yanzu kam tabbas ta san ba ta yi ba,instead Ubangiji ya had’ata da mugun Miji Mugu ajin farko!
“Khadija wai har yanzu ba za ki bar kukan nan ba?na gaya miki addu’a itace mafita…wallahi Imam har yanzu bai yi miki rabin abunda ya yi mini ba,haka yake zai daina wata rana dan Allah ki yi k’ok’ari ki cire damuwa a ranki mana.”
Muryar Abokiyar zamanta wadda shigowarta cikin b’angaren nata kenan ta katse mata tunani.
A hankali ta d’ago ta kalleta daidai tana zama da Yaronta a hannunta.
Cikin sharar hawaye tace”ba komai Mommy,kar ki damu na san wata rana sai labari.”
Cikin son kawar da maganar dan zuwa yanzu ko lallashi ba ta so a cika yi mata gaba d’aya sai ta sake zama emotional dan haka ta d’an k’ak’alo murmushi tace”Yassir! Ina ka baro Yasira?ko tana chan tana sana’ar?”.
Ta fad’i hakan tana mai mik’awa Yaron hannu alamun ya zo gareta.

“Kamar kuwa kin sani..tun da Baba larai ta yi musu wanka ita da Yahanasu suka koma bacci har yanzu ba su tashi ba..”
Murmushi ta yi tace”Allah ya yi albarka ya had’a kawunansu”

“Am khadija ko za ki yiwa Hajiya Mama magana a samu Yashjub ya dawo..ya yi k’ank’anta a zuwa Hutu ya dad’e haka a wata k’asar gashi an koma makaranta.”

Dariya ta yi kafin tace”yanzu Mommy sai in kira Hajiya Mama in ce mata Yashjub ya dawo ya yi k’ank’anta?ai sai a ga rashin karar mu..ki yi hak’uri ita kanta na san nan ba da jimawa ba za ta dawo da shi..ke da ya kamata ace yanzu fafutukar ta yadda za ku shirya ma kike yi! idan ta ji mun ce Yash ya dawo ai bak’in jini za ki sake gogawa kanki har ni sai ta shafa….”

Shiruu Mommy ta yi kafin ta sauk’e wata nannuyar ajiyar zuciya tace”Allah ya sa mu dace”
“Ameen”Khadija ta yi ta fara yiwa Yassir wanda ta karb’a wasa shi kuma yana dariya.

“D’azu dai Daddy ya kori mallan lawal,ai dama na gaya miki yadda ya sakawa Yaron nan k’ahon zuk’a ba zai barshi ba.”
Shiruu Khadija ta yi kafin tace”yanzu kenan ta tabbata Daddy zargin na yake yi?”
“Ba zarginki yake yi ba Khadija masifar kishi ne kawai,ke dai ki yi ta addu’a sannan kamar yadda kika fad’a wata rana sai labari..
Ki yi ta sallar dare kina gayawa Ubangiji na san kina yi amma ki k’ara,jikina yana bani inshaaAllah yana dawowa daga Abuja za ku shirya komai ya zama labari…”

A hankali Khadija tace”Au ya tafi?”.
Jin jina kai Mommy ta yi kafin tace”bai yi miki sallama ba?”
Sai kuma ta kawar da zancen tace”bari in je in had’o y’an kud’ad’e in bawa mallan lawal,Yaron yana bani tausayi wallahi bashi da kowa fa maraya ne gaba da baya.”
Tana gama fad’in haka ta mik’e ta bar mata Yassir ta nufi k’ofa tana cewa “bari na je na d’auko.”
Daga haka ta fice….

Tana fita itama ta mik’e ta nufi bedroom d’inta da Yassir a hannunta…wajen ajjiye kud’ad’e ta d’aga ta zaro masu nauyi da niyyar idan Mommy ta dawo ta bata tace ta bawa mallan lawal d’in dan ko ba komai shima maraya ne kamarta kuma saboda ita a ka koresa….tana d’aukowa ta jiyo kenan suka yi ido biyu da shi,da farko tsoro ya bata saboda ta san mallan lawal d’in da ta sani ko giyar wake ya sha bai Isa shigo mata har cikin bedroom ba,ganin yana magana yana matsota ne ya sa ta fahimci tabbas fa shi d’in ne dan haka cikin tsoron gudun a gansu fushi da hargowa ta fara ce masa”ya fice mata daga d’aki”
Ba tare da b’ata lokaci ba.
Gadan gadan ta ga ya nufo ta
daga haka bata sake tuna komai ba…sai farkawar da ta yi
wadda ta ji inama ba ta farka ba inama wucewa lahira kawai ta yi da ya fiye mata kwanciyar hankali.
Daga ita sai under skirta kwance a gado d’aya lullub’e cikin bargo d’aya da mallan lawal wanda shima wando ne kawai a jikinsa yana kwance yana sharar baccinsa peacefully.
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
Ta shiga ambato ba k’ak’k’autawa tana jin wani irin bak’in ciki da tashin hankalin da bata tab’a jin kwatankwacin irin sa ba.
Tashi d’aya ta fashe da kuka ta fara k’ok’arin tashi amma sai ta kasa motsi kwata kwata saboda wani masifaffen tashin hankalin da ya sake mamaye ta sakamokon muryar Daddy da ta ji yana cewa”har fa na kama hanya kuka saka ni na dawo saboda takardun! ke da kika gansu a hannun Yarinya ai kamata ya yi ki amshe ki kawo mini.”
Cikin kwantar da murya ta ji muryar Mommy tana cewa”to ai Daddy ban yi tunanin naka bane ni na d’auka na Maman nata ne da na ga ta yo
nan d’in da su,ba dan yanzun ka gaya mini kalar envelope d’in ba ma da yanayinta da ba ganewa zan yi ba….”


A hankali Khadija ta koma ta kwanta ta ja bargon ta lumshe idanuwanta kawai saboda no way out dan a halin da ake ciki ma key ta ji Daddy yana murzawa ta waje zai bud’e k’ofar ya shigo yana cewa”yau kuma Khadija rufe kanta ta yi ta ciki kenan!Allah ya kyauta!”.Gashi ba ta ga makulli a jikin k’ofartata ta ciki ba.


Tsabar tashin hankali sumewa ta yi,ruwan da Mommy ta shek’a mata ne ya sa ta farka a gigice chan ta hango Daddy ya nufo ta gadan gadan da wuk’a a hannunsa kafin ta yi wata wata har ya Burma mata a ciki………
Sama sama ta ke jin Mommy tana kuka tana rok’on Daddy tana cewa”kar ka yi haka Daddy,Ubangiji kad’ai ne ya Isa ya yanke hukunci kar ka yi abunda zaka kai kanka prison ka bud’e musu su fito dan girman Allah…..”
K’aurin wuta ta fara ji kafin hayak’i dga haka ta ga wuta tana ci wanda hakan ya tabbatar mata tabbas Daddy wuta ya cinna musu.
Kamar d’azu yanzun ma ba ta yi yunk’urin yin komai ba dan ba za ta iyaba gashi jikinta ba kwari ba ma ta gani sosai ga tashin hankali..ko yatsarta ba ta iya d’agawa.

…..Ba ta san Ina Mallan lawal ya yi ba ita dai ta ji an d’auke ta sannan muryar wani yana cewa”ta nan za ku bi”
Wanda har gobe ta kasa tantance muryar mutumin ballantana ta yanke hukunci.

A cikin wani d’an madaidaicin gida ta farka ta ganta ana yi mata k’arin ruwa ga likita a gefenta da mallan lawal.

Rufar mata suka yi suna tambayar ta ya jikinta itakam bak’in ciki da tsananin tashin hankalin da take a ciki ma bai barta ta ko kallesu ba…duddubata likitan ya yi ya cewa mallan lawal “idan wani abun ya tashi ya nemesa” daga haka ya yi musu sallama da Allah ya k’ara sauk’i ya fice.
Yana fita mallan lawal ya gyara zama ya fara magana”Khadija ki yi hak’uri dan girman Allah..wallahi sharrin shaid’an ne amma inaso ki san cewa babu abunda ya shiga tsakaninmu dan ko da na yunk’ura kasa aikata komai na yi a gareki….na san kin tsaneni ba kya son jin ko murya ta ma shiyasa na zab’i in yi nesa da ke daga yau har abada.
Ga gida nan ki zauna a ciki kar ki tambayeni a ina na samu kud’in kawai inaso ki san wannan gidan na ki ne ga takardun nan a cikin wachchar drawer!ki yi hak’uri ki yi hak’uri ki yafe mini dan girman Allah”.
Yana gama fad’in haka ya mik’e yace mata”a cikin garin Abuja muke ba a kano ba.”
Daga haka ya sa kai ya fita.

Sai da ta tabbatar da ya yi nisa tukunna ta mik’e tsaye..d’inki ne a cikinta amma kawai tsintar kanta ta yi da fara takawa a hankali a hankali a haka har ta fice da ga d’akin ta fice daga cikin gidan gaba d’aya,ta ya ma za ta fara zama a gidan da lawal ya ajjiyeta?! ba zai yiu ba!.
Dare ya yi a lokacin gashi unguwar shiruu babu ma mutane sosai…..
Tafiya kawai take yi ba ta san ina za ta je ba ba kuma ta san abunda ya kamata ta yi ba…wani ikon Allah zuwa yanzu ta nemi zafin da cikin nata yake yi ta rasa amma kuma ko ba ta kalla ba ta san d’inkin ya warware dan tana jin yadda jini yake bin jikinta…ta lura da yadda wata mota take ta binta a hankali sai da aka yi kusan tafiyar minti ashirin da mutumin ya ga ba ta da niyyar tsayawa gashi sai faman zubda jini take yi yayi parking motar a daidai gabanta ya fito yana k’are mata kallo.

Sai a lokacin wata juwwa ta kwasheta ta tafi ta zube a wajen.

Sai da ta yi kwana biyu tukunna aka samu ta farfad’o da mugun kyar.

A asibiti ta bud’e ido ta ganta,wannan mutumin da ya tsinceta ne yake sanar da ita cewar”kwananta hud’u da kyar aka samu ta farfad’o a ranar.”
Babu yadda bai yi da ita akan ta gaya masa inda family d’inta suke ba amma ta k’i magana..ganin kamar ba ta ji kuma ba ta magana ne ya sanya ya hak’ura ya rabu da ita ya had’a ta da nurses ya biya kud’in komai yace “idan akwai emergency a kirasa”daga haka ya tafi.

Duk yadda ya so ya manta da al’amuranta sam sai ya gagara,gaba d’aya tausayinta ya hana sa sukuni lamarinta ya tsaya masa a rai..ya san tabbas tanada buk’atar taimako.
Ba a yi sati uku da rasuwar k’anwar sa ba,sun yi mata aure sun d’auke ta sun kaita jos ashe mijin ba zaman adalci yake yi da ita ba k’arshe sai ciwon zuciya ne ya kasheta…..
Mahaifiyarsu ta rasu kuma su biyu ne kad’ai shiyasa har gobe yake blaming kansa dan in da ace yana yawan zuwa dubo ta kuma ya saka idanu a kanta da hakan ba ta faru ba.

Sai da ya tabbatar ta warware ta fita a shock,almost 1 month tukunna ya koma,a lokacin ta warke amma wani ikon Allah damuwa ko kad’an ba ta barta ba asalima kuka ya je shi ya tarda ita ta na yi.
Ya kad’u sosai da lamarinta dan haka bayan sun gaisa ya amsa godiyar da ta yi masa da kulawa ya zauna ya shiga tambayarta “menene matsalarta har haka?,kar ta damu ta d’aukesa a matsayin yayanta ta fad’a masa komai.”
Sau uku tana bud’e baki da niyyar bashi tarihinta amma tana fara cewa”Mijina ne…”
Sai kuka ya ci k’arfinta……
Zuwa yanzu ya fahinci inda gundarin matsalar take shiyasa kawai ya ce “ta yi shiru…..ta yi hak’uri ko ma me ya yi mata ta yi hak’uri Allah zai saka mata.”

Sai da ya tabbata ta d’an nutsu tukunna yace”akwai wanda take so ta kira a cikin y’an uwanta?”
Ba b’oye b’oye tace masa ”ba ta da kowa”

Jinjina kai ya yi yana mai jin tsananin tausayinta,haka kurum take tuno masa da marigayiya k’anwarsa tun ba ma da ya ji itama sunanta Khadijah kamar k’anwar tasa ba.Ya jima yana nazari kafin yace”kina buk’atar ganin shi Mijin naki ne?a nem…”
Tun kafin ya rufe bakin sa tace”A’a”
Dan ba wai iyaka Lawal da ya k’ulla mata sharri take jin haushi ba har da Imam wanda ya yarda ya aminta ta aikata abunda aka nunawa idanunsa on top of that ya hari rayuwarta.

“In kai ki Gidana za ki taya matata zama?,Dr ya ce mini a yau zai sallameki inshaaAllah”
Muryarsa ta katse mata tunani.
….Da farko k’in amincewa ta yi tace”ya barta a asibitin ko kuma ya barta ta tafi kawai za ta san abunyi.”Shi kuma ya k’i dan a yadda take da damuwar nan idan ba ta samu wani da zai yi mata gata ya tsaya a kanta ba tabbas akwai matsala shi kuma haka kurum ya ji yana so ya taimake ta kuma yana so ya yi making up to negligence d’in da ya yi wa sister d’insa shiysa ya nace ya k’i barinta har sai da ta amince ta bisa suka tafi gidansa.
D’ansa d’aya mai suna Al’ameen da matarsa suna ce mata Ammi dan shima mai gidan sunan mahaifiyar sa ne da matar tasa.
Dama tun farko Ammi ta fara nuna kishi da Khadija dan ce mata ya yi y’ar uwarsa ce cousin za ta zauna da su. Daga baya kuwa da ya fad’a mata gaskiya dan shi bayason b’oye b’oye,da kuma itama y’an uwanta suka zugata shikenan ta fara hauka!……har ta yi haukar ta kuwa ta saduda babu wanda ya biyeta,ita da kanta ta zauna ta yi lissafi mai kyau ta nemi gafarar mijinta da khadija aka zauna lafiya dan a lokacin sun kusan shekaru shidda tare shiyasa lissafinta ya bata inda ace fa aurenta zai yi tou da tuni ya aura.Kuma yadda Khadija take kula mata da Al’ameen ko ita ba ta kula da shi..mai d’a wawa!ta haka Khadija ta siye zuciyar Ammi gaba d’aya.

A kwana a tashi zama ya dawo da su Kano.Sai a lokacin Khadija ta gaya musu tana da y’a Yahanasu.
Addu’ar ta d’aya Allah ya sa ba a chanja musu makarantar da ta san an fara saka su ita da Yashjub tun farko ba,dan haka suka tambayi baban Al’ameen suka tafi ita da Ammi.
Ba su sha wahala ba dan tashi d’aya matar ta shaida ta ta amsheta hannu bibbiyu har da hawayenta tana cewa”ai ce musu aka yi ta rasu,amma ta je gida an ganta?ko dai nan wajen Yahanasu ta taho direct??ta je su ganta suma hankalinsu ya kwanta waye waye…”
Ita dai Khadija ce mata ta yi tou kafin tace”a kawo mata Yahanasu da Yashjub.”

“Yashjub ai ya dad’e da komawa Uk,amma Yahanasu dai tana nan,da tare take ma da siblings d’inta to yanzu basu da nursery section sakamokon gobarar da suka yi shine aka chanja musu school.”
Matar ta faiyyace mata hakan tana mai fita domin ta je ta taho mata da Yaha.

Sai da Khadija ta yi kuka,saboda da kyar Yahanasu ta shaida ta.
Tana murna tana kuka kamar ranta zai fita haka ta mak’alk’ale y’ar tata.

Hatta Ammi da mai makarantar sai da suka yi kuka..

Tun daga ranar duk ran Jumaah kafin su d’auki Al’ameen a school sai sun biya sun ga Yahanasu,Yarinyar ta shak’u da mahaifiyarta sosai zuwa yanzu….Khadija Ammi da Baban Al’ameen suna shiryen shiryen zuwa su je a yi magana ta fahimtar juna a samu Imam ya bawa Khadija Yahansu kwasam rannan sun je mai makarantar tace “Mahaifin Yahanasu yace idan ta sake barinta ta shiga makarantar sai ya k’ulle ta!.
Dan Allah dan Annabi ta yi hak’uri ta tafi kuma yace idan har ta sake zuwa kusa da y’ar sa wallahi kowa sai ya ji kansu kuma kowa sai ya ji abunda ta aikata har ita y’ar tata”…

….Babu kalar tambayar da su Ammi ba su yi mata ba a kan ta yi musu k’arin bayani amma ta k’i cewa komai,Baban Al’ameen da har yana shirin shiga kotu a samu a kwato mata y’arta amma ta hana ta kuma rok’esu akan kar su sake yin maganar a bari ya wuce kawai…Zuwa yanzu sun riga sun san Khadija sun san ba muguwa bace ba kuma ba ta da wani mummunan hali,shiyasa ba su dasa ayar tambaya a kanta game da hakan ba kuma suka bar maganar ya wuce kamar yadda ta rok’a ta buk’ata.

A b’angaren Khadija kuwa,abubuwa da dama ne suka had’e mata!
Kenan har yanzu Imam bai yi bincike ya goge zarginta ba!bai yi nadamar abunda ya aikata mata ba?
Sannan ko kewarta
ma bai yi ba all this years bai nemeta ba bai nemi ta dawo garesa ba instead yana so ma ya yi cutting duk wani ties da suke da shi,y’ar cikinta ma ya raba ta da ita kenan yanzu.!
Abu na uku kuma ta san tana da gaskiya akan sharrin da Lawal ya yi mata amma kuma har ga Allah idan akwai Al’amari mafi k’ololuwar tozarci da Muni da masifar tashin hankalin da ba ta son
tunawa a rayuwar shine wannan incidence d’in,ita kanta ita kad’ai idan ta tuno ji takeyi kamar ta binne kanta tsabar tashin hankali ba don k’arfin addu’a ba da tuni ta zauce tsabar yadda abun yake addabar ta a ko da yaushe idan ta tuna,A yadda Imam ya zama wani irin mugun mutum ta san zai yi mata terere ne kamar yadda mai makarantar su Yahansun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login