Showing 105001 words to 108000 words out of 244445 words
one seater tukunna ya zaunar da ita ya zauna a gefen ta kafin yace
“Do u like it ?The house!ya yi miki kyau?”
Sai da ta kuma k’arewa parlourn kallo tukunna tace “Sosai ma kuwa,ya yi kyau over”
Ta fad’i hakan tana kallon parlourn..
murmushi yayi ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace
“MashaaAllah na ji matuk’ar dad’i da kikace ya yi miki saboda dama Inata adduar Allah yasa yayi miki kyau…wannan shine Gida na farko da na fara siya a rayuwata,it’s so dear to me shiyasa na mallakawa the closest person to my heart and soul.Gidan ki ne…da na baki as a
gift halak malak”
Da sauri ta juyo ta kalle sa
sai kuma ta kalli parlourn kafin ta sake juyowa tace
“Bai yi yawa ba kuwa?…ba ma a Nigeria ba fa..
Cikin janyota jikin sa yace
‘’Gift da kyautar da kika yi mini Baby sun fi k’arfin wannan idan na ce zan biya ko zan kamanta to fa sai na baki komai nawa tass ba tare da na kamo k’afar biyan ki ba ma..to amma kinsan an ce yaba kyauta tukuici shiyasa na baki nawa tukuicin ki karb’a kawai ke dai ki yi min alk’awarin kasancewa a tare da ni a ko da yaushe..idan ki ka yi mini haka kin gama min komai Baby…”
“Already takardun are under your name tomb print d’in kawai za mu mayar ya koma na ki.”
Ahankali tana kallonsa tace”we are one remember?ba sai an chanja tombprint d’inba..we will always be together inshaaAllah”
Sai kuma ta sunkuyar da kanta ta d’ago ta kallesa dan Wallahi ita ba ma ta san ta Ina za ta fara yi masa godiya ba gaba d’aya ya saka ta a shock
Da kyar ta bud’e bakinta tace
“Nagode Sosai Allah ya saka da allhairi na s……”
Da sauri ya rufe mata baki yace “ni ne da godiya”
Bai sake ba ta damar yin magana ba sakamokon kissing dinta da ya fara yi da sauri da sauri yadda ta ji jikinsa har karkawa yake yi ne ya sanya ta hak’ura kawai dan ta san ba sarara mata zai yi ba……
Sai da gari ya fara haske tukunna ya samu kanshi..sai bayan kusan 2 minutes tukunna ya d’ago yana kallonta yana mayar da numfashi still yace”mu je mu yi sallah sai in nuna miki gidan naki,ke kika tsayar da mu ba mu yi tour ba”ya fad’i hakan yana murmushi.
Turo baki ta yi ta d’an kauda kai dan haka ya yi dariya ya fara yi mata cakulkuli duk yadda ta so dakewa sai ta gagara ta fara dariya itama a haka ya d’auke ta suka nufi d’aki tana cewa”dole ma ta yi kib’a ko dan yadda yake d’aukarta anyhow daganan sai ta ga yadda zai yi…..”
Wanka suka fara yi suka yi sallar Asubah suka ci abincin da ya yo musu order tukunna ya ce su je ya nuna mata gidan
D’akuna uku ne sai kitchen da store da tafkeken parlour.
Ta baya kuma pool ne da pool house sai garden ata gaban gidan mai d’ankaren kyau….
Suna gama zagayen ya kira masu gyaran gida aka zo aka gyara aka share aka goge koina tass tass.
Sun ci sa’a kusa da restaurant suke shiyasa order d’insu ba ya d’aukar lokaci…..sai la’asar tukunna komai ya kammala suka yi wanka sukai sallah.
Kwata kwata hutun awa uku ya bari suka yi daganan ya d’aura daga inda ya tsaya…ita kamar wanda ake yiwa ruwan energy ma haka take ganinsa dan sam ba ya gajiya…..
To dai kamar yadda Yashjub ya fad’a mata ashe da gaske shi bai ma fara cin amarcinnasa ba sai yanzu dan ita kanta ta tabbatar a Nigeria appetizer ya yi….Sai da suka shafe sati
d’aya da kwana uku ba ta lek’a waje ba shima haka dan da kyar ma aka samu ya d’an fita ya je ya sissiyo musu abubuwan da za su buk’ata daga nan sai da suka yi sati d’aya da kwana uku tukunna suka d’an fara fita suka fara zageye island d’in,ita Manubiya har ga Allah so take yi ta zauna a gidan ta yi barci sosai ta huta amman kuma ta san idan suka zauna a gidan ba barinta ta huta d’in zai yi ba shiyasa kawai take yarda tana biyosa suna fita yawon ba dan tana jin dad’in yawon ba gashi dai the view da duk wani abu about Cyprus is heaven amma ita sam ba ta enjoying tsabar gajiya…
A haka dai kafin su yi wata biyu ta samu ta d’an saba kuma ta yi accepting mijinta a yadda yake dan ta fahimci ba wai don ya takuramata bane hakanan halittarsa ta ke ga kuma gudummawar da soyayyarta da k’aunarta suke badawa..
Shi kansa Yashjub ya na mamakin yadda Manubiya ta taso masa da wani tsumin dake a jikinsa wanda a da sam bai san da shi…dan a da kwata kwata ko kallon mata ba ya son yi ballantana su basa sha’awa..yana jin sha’awa ba wai kwata kwata ba ya ji ba amman ko ta d’an taso masa to ba zai yi 10 minutes yana jin wannan feeling d’in ba dan tashi d’aya zai ji ya nemi feeling d’in ya rasa shiyasa a wannan lokacin wani zubin har tunani yake yi akan’Anya kuwa lafiyar sa k’alau!?’.
Kafin 2 months itama ta ware ta zama y’ar gari ta shiga faranta wa Mijinta rai yadda ya kamata Wanda hakan ba k’aramin dad’i ya yiwa Yashjub ba dan shi sai a wannan lokacin ne ma tukunna ya ke sake experiencing wasu ni’imomin da aure ya k’unsa…
Zaman lafiya kwanciyar hankali da asalin tattalin so da k’aunar juna shine definition d’in zaman Manubiya da Yashjub a Cyprus..wani zubin idan ya yi mata wani abun har kukan farin ciki takeyi ta yi sujjada ta yi ta godiya ga Allah S W A dan itakam in dai a fannin so da k’auna na tsakani da Allah ne to ba shakka za ta fito ta bugi k’irji tace “ta fi ko wacce mace sa’ar mijin aure…”
Hutun su kawai sukeyi gaba d’aya sun manta da matsalolin su sun yi fari sun yi k’iba abunsu….suna waya da video call da su Jidda haka shima Yashjub ya na waya da Mommy kuma ba yabo ba fallasa suke gaisawa ita da Manubiya itama Manubiyan da kanta takan kirata ta gaida ita ba yabo babu fallasa take amsawa.
Haka suna waya da chattin da su Ummi Yahanasu da Munirat sosai su Yasira kuwa ko ‘hi’ babu a tsakanin su da Manubiya amma suna kula d’an uwansu.
Yashjub ya lura kuma ya sani amma bai yi magana ba itama bata ce komai ba dan ko kiran sa sukayi basa cewa ya bata shima kuma baya bayarwa..Manubiya ba ta nuna masa text d’in da Ya’isha ta yi
mata ba 2 month ago kafin su taho amma shi ya gani..so yake kawai ya ga iyaka gudun ruwansu Daddy ya huce daganan zai san abunyi.
Watansu biyu da sati biyu Daddy ya kira Manubiya..ta yi mamakin ganin kiran amma sai ta d’auka da mutuntawa ta gaidashi
Da kulawa ya amsa ya tambaye ta ya Cyprus tace alhamdulilah daga haka yace”yaushe za su dawo?”
Diriricewa ta yi ta rasa bakin magana da kyar dai tace”Yash d’in bai gaya mata ba”
Jinjina kai Daddy ya yi kafin yace”ok shikenan daga haka ya kashe wayar.
Sarai Yashjub ya ji komai ya fahimci me Daddyn yake nufi da yin haka dan haka ya d’au waya ya fita ya kira sa…
Suna gaisawa Daddy yace”a lokacin da Manubiya ta mari Yadira na ji haushi sosai kuma yadda ka yi zato jiranku kawai nake yi ku dawo in had’a ka kai da ita Manubiyan in yi muku warning kuma in yi riga kafi saboda gaba amman tunda har za ka iya yi mana k’aura saboda hakan InshaaAllah maganar ta wuce kuma komai ya wuce amman a kiyaye gaba…come home..da ni da y’an uwanka da Mommynka muna buk’atarka a kusa da mu ba ka tashi tare da mu ba bai kamata yanzu ma ka sake barinmu ba”
Shiruu Yashjub ya yi kamar zai faiyyace wa Daddy halin su Yasira ya kare Manubiya amman kuma kawai sai ya bar maganar yace”ka yi hak’uri Daddy dama nan da 4 days ma za mu wuce Uk mu yi musu sati biyu daganan sai mu dawo inshaaAllah”.
Ahankali Daddy ya ce”Allah ya kaimu”daga haka ya kashe wayar ya dafe kansa…he really can’t believe Yashjub ya d’auke matarsa sun yi nesa da su saboda ba ya so a nuna mata ta yi laifi kuma bayaso ma a ga laifinta a kan komai,tabbas da alama Yarinyar nan ta juya kwakwalwar Yash kuma son da yake yi mata ba na wasa bane dan tabbas zai iya rabuwa da kowa akanta dan ga alama nan….
Dan haka zai yi iyaka bakin k’ok’arinsa wajen ganin ba ta raba sa da d’ansa ba inshaaAllah daga yau ba zai sake ba shi reason d’in da zai yi tunanin barinsu saboda ita ba…
Shikenan fa yanzu da bai ankare da wuri ba da sai dai Yash ya zo yi musu sallama,dan tsaf zai yi transferring komai nasa garin da yake so ya je ya ci gaba da business d’insa da rayuwar sa a chan su ya barsu a nan.
Tabbas ya yi regretting aurawa Yash Manubiya dan gashi tun ba a je koina tana pulling Yash away from them amma tunda aikin gama ya riga ya gama kuma ba komai inshaaAllah ba zai sake bawa Yash reason d’in da zai guje su saboda ita ba.
Tsaraba sosai suka shiga jida a Cyprus dan sun kusa wuce wa Uk inshaaAllah.
Sarai Manubiya ta fahimci dalilin Yash na tambayar ta akan batun period d’in ta kusan kullum
Ko last week har asibiti suka je yace a yi musu checkup d’in su malaria da komai amman ita sai da aka had’a mata har da scanning
Da farko abun dariya yake bata dan ita a ganinta ko wata uku basu cika ba amman ace har ya fara k’ulafucin ciki sai dai kuma yadda ta ga yanayin sa tun jiya da ya ga ta fara period d’inta abun ya bata mamaki matuk’a dan tun jiya taga ya zama so silent da kyar yake iya dariya sannan ko bacci bai yi ba a jiyan dan ko da ya tashi ya yi sallar dare ya ida kasa komawa ya yi har asuba.
Yanzu kuma da safe tana kitchen ya shigo ya ce mata “ya tafi jugging”
bayan da tare da ita suke fita kullum..kafin ma ta gama yi masa a dawo lafiya har ya sa kai ya fice daga kitchen d’in.
Ajiyar zuciya ta sauk’e ta juya ta ci gaba da aikin ta jiki duk ba kwari tana ta tunani…a haka ta kammala ta jere abincin a kan dining daga haka ta juya ta nufi d’akin su domin yin wanka.
Ta ji matuk’ar tsoron ganin sa da ta yi a d’akin zaune a kan gadon dan batayi tunanin har ya dawo ba,ba ta ji shigowar sa ba sannan bai ce mata ya dawo ba kuma idan sun fita jugging d’in sukan d’an jima kafin su dawo…
Ta na wannan tunanin ta ga ya sakar mata murmushi kafin ya mik’a mata hannu alamun ta zo garesa.
Ahankali ta d’an matsa kamar mai jin tsoro ta zauna a kan cinyarsa…cikin cusa fuskarsa cikin wuyanta yace
“Morning wife!”
Ba ta amsashi ba sai da ta mik’a masa tata gaisuwar tukunna .
Sannan ta d’an kalle sa ta ce
“Kanada damuwa! mun ce ba za mu dinga b’oyewa juna komai ba.
Talk to me Dan Allah”.
Saida ya d’an shafa cikinta ya kalli cikin tukunna ya d’ago ya kalleta yace”Na ji har yanzu shiru ne!.
Baki tab’a shan wani magani mai k’arfi ba ko da na malaria ne? Ko mu je a duba ki sosai sosai..kin san yawanci y’an mata fa kunada matsalar da ku kanku baku sani ba sai likita ya duba da ikon Allah sai kiga an dace…”
Shiruu ta yi ta sunkuyar da kanta k’asa alamun ta shiga damuwa shiyasa tashi d’aya kamar zai yi kuka yace “Shiyasa fa kika ga na kasa yi miki maganar tun tuni
Banason b’acin ranki ni kuma har ga Allah a matse nake inji good news…”
Murmushi ta yi tace “ba b’acin rai bane kawai dai nima kasa na fara tunani ne..”
Sai kuma ta d’an yi shiruu kafin ta sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya tace”Mu yi addu’a !mu yi ta addu’a!”
Daga haka tayi shiruu ta fa’da duniyar tunani….itanma babban burinta a yanzu shine ta ga babyn ta da Yash amma gashi shiru har yanzu, da farko tana gani kamar ya yi wuri amman itanma yanzu ya jefata a damuwa…wat if ta kasance a cikin matan da basa haihuwa ya kenan?ta san shikenan ta rasa soyayyar Yashjub
Dan a yadda ta ga k’ulafucin son haihuwa a kwayar idanun sa ba lalle ya iya zama da ita kad’ai ba tare da yara ba sannan ba lalle ya ci gaba da sonta kamar yadda ya ke yi ba.
Yashjub ya riga ya saba mata da zazzafar soyayyar sa
Idan ya juya mata baya ba ta san ya zata yi ba.
Da sauri a cikin ranta tace
“Ya Allah ka sa zan haihu nima Ya Allah ka bamu y’a y’a masu albarka.”
Ahankali yace”kar fa ki saka damuwa a ranki
Ki yi hak’uri idan na d’aga miki hankali”
Girgiza kai kawai ta yi tace “ba komai”ta d’an yi murmushi daganan ta mik’e ta fara shirin ta shi kuma ya fad’a toilet yin wanka.
Har ya fito a yadda ya shiga ya barta hakan ya dawo ya tarar da mood d’in ta shiyasa ya yi ta janta da wasa yana k’arfin halin ganin ta sake dan shima a damuwar yake
Ya san it’s too soon amman mostly ana samu da wuri ai.
A haka suka yi breakfast d’in kowa da abunda yake tunani kafin yace “ta zo su je su d’an kammala shirin tafiyar tasu dan jibi suke so su wuce uk su duba jikin Na’ima su yi musu two weeks inshaaAllah daga nan sai su wuce Nigeria.
Ko da suka fita gajiya ga ciwon marar period d’in da take yi ne ya sa Yash ya dawo da ita bayan ta gama duk abunda ya kamata shi kuma ya koma.
Sai dare ya samu ya dawo
Washegari komai nasu ya kammala ta inda zasu bar Cyprus nan da kwana biyu.
A cikin kwana biyun nan saida Yashjub ya san yadda ya yi ya cire mata damuwa dan ya lura tunda ya yi maganar ciki hankalin ta a tashe yake.
Ba wai dan hankalin nata ya kwanta ba ta sake ta ke walwala dan ta lura ba zai barta ba idan har ba ta sake d’in ba
Amman a chan k’asan zuciyarta tana da damuwa da ta duk’ufa gayawa Allah.
Tun daga nan zaman su ya dawo kamar farko in ka gansu kowa wasai dan shima Yash d’in daurewa yayi sosai ya ke k’ok’ari wajen b’oye tasa damuwar.
A ranar tafiyarsu Manubiya ji ta yi kamar kar su tafi.Ta ji dad’in Cyprus kwarai ta ji dad’in gidan ta ji dad’in rayuwar da sukayi fiye da komai a rayuwarta rayuwar da ta tabbata ko wacce mace idan ta samu za ta ji dad’i za ta yi alfahari da sannan zata ajjiye a kwakwalawar ta har k’arshen rayuwarta.
dan tabbas rayuwa ce mai tsada mai dad’i da mutun bai Isa ya mance ba…
Da rana wajajen 2:34 british airways ya sauk’e su a Heathrow Airport London.
Suna fitowa Yashjub ya hango Junior ya nufosu yana murmushi dan haka shima ya sake rik’e hannun Manubiya suka nufe sa.
Yana zuwa ya yi hugging Yashjub kafin ya juya ga Manubiya suka gaisa cikin girmama juna daga nan suka nufi inda ya yi parking motarsa da su da waenda suka d’aukar musu luggage d’insu.
“Ga inda ake k’anin miji mai hankali”
Manubiya ta fad’i hakan a k’asan ranta.
A bakin wani babban gida mai d’ankaren kyau Junior ya yi parking ya danna horn
kafin mai gadi ya ja musu suka nufi ciki.
A bakin entrance na shiga babban parlourn gidan suka tarar da Hajiya mama tana jiran su….tunda Manubiya ta fito ta kafeta da ido ta shiga yaba Yarinyar a ranta gata da nutsuwa dan tunda ta tunkaro ta kanta yake a k’asa kuma tana lure da yadda ta zame hannunta a cikin na Yashjub a hankali a time d’in da ta lura da ita.
Murmushi tayi lokacin da suka k’araso Manubiya tana shirin durk’usawa Hajiya mama ta yi sauri ta tarota ta sakata a jikinta ta rungume
dai dai nan mom ma ta fito…haka itama ta yi hugging Manubiya cike da so sunata murna kamar za su maida ita ciki kafin su nufi cikin parlourn da ita
Saida suka zazzauna tukunna Manubiya ta samu da zamo daga kan kujerar ta gaida su da girmamawa
murmushi kawai sukayi suka amsa
kafin Hajiya mama ta d’aga Kai ta kalli Yashjub tace
“To fad’o mini a ka…yau kenan miskilancin ta kaina ya biyo”.
Da sauri Junior yace
“Inaaaaa!Hajiya mama ai this a new B Yashjub fa”ya fad‘i hakan yana mai nuna Yash kafin ya d’aura da cewa”ai ya daina miskilanci yanzu,tunda fa muka taho yake zubawa sweetheart d’insa surutu yana nuna mata wajaje da favorite places d’insa.
Love ya chanja sa ya koma mai surutu”
Dariya duk sukayi yayinda Yashjub ya d’an yi murmushi ya na mai sunkuyar da kai a ranshi kuwa shi kansa yana mamakin yadda soyayya ta chanja shi.
Sai da ya kuma yin wani murmushin mai cike da ma’anoni tukunna ya kalli Hajiya mama yace”Ba fa ki kulani ba
A bakin k’ofa kika barni kika ja hannun kishiyar ki ko ‘hi’ baku ce min ba daga ke har mom..”
Murmushi mom ta yi ta mik’e ta k’arasa ta je ta yi huggin nashi tace”welcome welcome”
Daga nan ya yarda ya bita ta zaunar da shi kusa da ita.
Lek’awa Hajiya mama ta yi ta rankwashe sa tace
“Da wani katoton kan sa!wa za ka yi wa shagwab’a??”
Kwashe wa da dariya Junior ya yi dan haka Yashjub ya d’ago yana masa irin kallon ‘ka fa fita a idona’d’innan wanda ya sa Junior d’in saurin gimtse dariyar tasa ya shiga yin ta k’asa k’asa sai kuma duk aka sa dariya
banda Yashjub wanda ya ke kallon Manubiya da kalar tausayin irin ‘har da ke ake mini dariya’…….
Masu abinci ne suka fara gabatar musu da kalolin dishes saida aka kaisu d’aki suka yi wanka suka yi sallah tukunna aka kaisu wajen Na’ima,jikin nata da sauk’i dan k’afar