Showing 129001 words to 132000 words out of 244445 words

Chapter 44 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16430

ne!.”
Cikin sauk’e ajiyar zuciya ta kamo hannun Baba larai ta ci gaba da cewa”dama ai ya san za mu je mu tayata gyaran gidan ko?”ba ta jira jin mai Baba laran za ta ce ba ta d’aura da cewa”zan yiwa su Yasmeen magana da su Yusra na yi miki alk’awarin inshaaAllah daga yau mun chanza zani,amma Ya’isha ba za ta bimu ba dan na san za ta iya b’ata mana komai…ki had’a duk wasu abubuwa da ya kamata inshaaAllah this time around ba za mu baki kunya ba ,za ki sha mamaki…”


“Allah ya yi miki albarka Yasira,zuwa dare zan ganku ke da su Yasmeen d’in kafin ku tafi”

Jin jina kai Yasira ta yi kafin ta kalli Mommy tace mata”Daddy yana son ganinki…”
Daga haka ta juya ta fita ta rufo musu k’ofar….

Tana fita Baba larai ta saki murmushi dan tabbas ta hango jajircewa a idanun Yasira,ta san kuma su Yasmeen ma za su yi mata biyayya inshaaAllah wannan karon akwai nasara….cikin jikin Manubiya za su fara farma a yadda Yash yake ji da cikin nan ta san easily za su samu matsala da shi da ita idan har suka nuna masa kamar Manubiyan ce ta zubar,but tayaya za su nuna masa hakan??dole su nemo reason da zai yarda da shi……
Tana wannan tunanin ta ji Mommy tace”bari in je…”
Kallonta Baba larai ta yi kafin tace”Juyin duniya!Khadija kar ki kuskura ki bari ya fahimci kin san wani abun”
Jinjina kai Mommy ta yi gabanta yana dukan uku uku ta juya za ta fita…cikin son kwantar mata da hankali Baba larai ta ruk’o hannunta tace”ki kwantar da hankalinki…”
Hawayen da suka b’allewa Mommy ne suka sanya ta kasa ci gaba da magana,a hankali ta rungumota ta shiga lalllashinta..fashewa Mommy ta yi da kuka cikin kukan tace “dan Allah dan annabi larai kar ki sake cewa za ki tafi,a wannan worst situation d’in larai idan kika tafi kika barni Ina makomata??…”

Ajiyar zuciya Baba larai ta sauk’e ta cikata tace”ba bu inda zan je amma Khadija kema sai kin chanja zani!kamar yadda su ka yi alk’awari dan Allah kema ki gyara…mu samu Yarinyar nan ta tafi daganan mu aura masa Kausar bayan shekara d’aya ko biyu idan ta haihu muka samu abunda muka so sai mu k’arasa shirin mu a samu a rufe chapter nan wallahi na gaji,sai abu d’aya ake yi yau kusan shekara nawa amma ba riba!”

Ajiyar zuciya Mommy ta fesar kafin tace”Larai I can’t trust Kausar with Yashjub anymore,a da na d’auka soyayyar da take yi masa mai sauk’i ce ko kuma lust ko wani abu makamancin haka shiyasa na yi tunanin idan suka yi shekara d’aya ko biyu ta samu abunda takeso ta haihu ta d’an zauna da shi ya fara fita a ranta to za ta iya yi mana abunda mukeso dan na san tunda ba ya sonta musguna mata zai ta yi…amma yanzu na fahimci masifaffiyar soyayya take yi masa,no matter what she’ll stick around and always love him unconditionally….abunda Yasmeen ta yi mini akan batun zubar da cikinnan ya sanya na fahimci Yaran nan ba za a dad’e ba kowacce za ta fara fito da nata view d’in tana jayayya da ni,kuma indai har Yasmeen y’ar cikina za ta iya yi mini hakan to abu mai sauk’i ne ga Kausar dan ta bijere mini,shiyasa na gama yankewa akan’babu maganar Kausar da Yashjub za mu san yadda za mun yi amma I can’t trust Kausar akan wannan Lamarin gaskiya…..”
Shiruu Baba larai ta yi kafin tace”to amma kuma ta ya za mu samu wanchan abun kenan?ko mun b’ata shekaru a banza kenan?ki duba future d’in Yassir ki sake tunani….”shiruu Baba larai da maganar ta d’an yi tunani kafin tace”to ko Manubiya za mu jira ta haihu idan ta haifa sai mu rik’e…….”

Cikin katseta da d’an b’acin rai Mommy tace”haba larai!ke fa da kanki ki ka sanar da ni illar kasancewar Manubiya a tare da Yashjub kuma gashi muna gani muraran!…besides ko dan masifar da wannan cikin da Uwarsa da Ubansa suka sakani a ciki wallahi dole sai ya fita!ko ana ha maza ha mata……”



K’ausar tana hawaye,a haka ta k’arasa side d’in Mommy ta shiga ta wuce parlourn ta nufi bedroom,har za ta tura k’ofar d’akin ta shige ta ji Mommy tana cewa”za dai mu san abunyi za mu nemo mafita amma cikin jikin Manubiya ya zama dole ya fita,sannan ba zan tab’a bari Kausar ta auri Yashjub ba!.”
Wani irin duhu duhu dishi dishi Kausar ta fara gani…ita da ta zo a kan ta cewa Mommyn ‘mai zai hana a yi tricking Yash ta samu ciki ta yadda dole sai ya aureta…’
amma shine take jin wannan batun daga bakin Mommy??
Dama ita ba ta yi shirin gaya mata tana da ciki ba dan ta san ba za ta yarda a aurawa Yash ita da cikin Yassir a jikinta ba,shiyasa take so ta bata wannan idear ta yadda ko shi Yassir d’in bai Isa ya san cikin nasa bane kawai kowa a tafi a kan cikin Yash d’in ne,ta samu ta rufawa kanta asiri burinta ya cika.Sam ba ta yi expecting haka daga Mommy ba,wato ta barta ta gama lalacewa shine yanzu take kyamar ta had’a d’anta da ita kenan ko yaya?
tabbas blood is thick! Ita kuma ta tabbata all alone….
Wani Irin kuka ne ya taho mata dan haka ta yi sauri ta juya gudun ma kar su jiyo ta ta nufi k’ofar parlourn hannunta a kan bakinta tana mai k’okarin hana sautin kukan nata fitowa.Kusan karo suka yi ita da Daddy wanda ya turo k’ofar parlourn ya shigo.
Shi ya wuce ya nufi d’akin ita kuma ta fice ta nufi d’akinta tana kuka kamar ranta zai fita.

A tsaye ya same su ita da Baba larai….sum sum haka Baba larai ta sa kai ta fice bayan ta yiwa Mommy wani kalar kallon da su kad’ai su ka san me take nufi.

Tana fita ya lumshe idanuwansa ya d’an bud’e kafin ya k’arasa kusa da ita yana mai kallon cikin idanuwanta yace”mallan lawal ya rasu”
Gefe da gefe ta kalla kamar irin tana tunani d’innan kafin tace”Daddy mai ya faru??? Kai fa ka ce a daina maganar nan kuma yau kai da bakinka ga shi ka kawo ta?”

K’ura mata ido ya yi,dama yana so ne ya ga reaction d’inta ko zai iya kamata da laifi amma babu alamun hakan a tartare da ita!
Ya san yadda Mommy ta kula da mahaifiyar Yahanasu suka zauna lafiya idan ya zargeta a kan incidence d’innan to bai yi mata adalci ba,amma kuma tunda mallan lawal ya kirasa d’azu ya fara basa hak’uri yana cewa yana son magana da shi to tun daga nan ya fahimci anya ba sharri aka k’ulluwa Khadijansa a wannan lokacin ba kuwa! sannan kuma kan sa ya d’aure matuk’a ta inda yana da tabbacin mallan lawal d’in ya mutu tun shekaru wajen ashirin da bakwai baya amma yanzu gashi ya ji sa a raye dan ko a mafarki idan ya ji muryar mallan lawal sai ya gane,shiyasa tashi d’aya ya tabbatar akwai k’umbiya k’umbiya a cikin al’amarin..
Khadija ba ta shiga ko mak’ofta sai tare da Mommy kuma ko hayaniya ba ta tab’a yi da kowa ba ita ba ma ta iya fad’an ba,duba da haukar da Mommy ta yi a lokacin da yace zai k’ara aure da kuma yadda ta shiryu lokaci guda ta rungumi Khadija tashi d’aya dama tun a wannan lokacin ya ke zarginta kuma ya ke ganin kamar akwai abunda ta ke shiryawa amma bai yi tunanin za ta iya yi mata wanchan sharrin ba!

Dan Khadija ko y’an uwa ba ta da shi balle ace wani ne ya yi mata sharri tabbas wannan aikin Mommy ne…
Sannan a cikin gidan ya yi waya da Mallan lawal ya san maybe Baba larai ce za ta gaya mata,shine ta kashe sa kenan??gudun kar asirin ta ya tonu?Tabbas kuwa indai hakan ya tabbata to bai ma san wanne kalar hukunci zai yanke mata ba!
Matsalar guda d’aya shine yadda ta yi d’innan ba dan shi da kansa gaba d’aya alamomi suna masa nunin kamar ita ce master ba,to ba dalilin da zai sanya ya zargeta.

A b’angaren Mommy kuwa in banda lugude babu abunda zuciyarta take yi!k’arfin hali ne kawai yake amma a mugun Muhsin hargitse take tun da ya shigo ta firgice…

“Daddy ka yi shiru”
D’in da tace ne ya katse masa tunani…
A hankali yace”yanzunnan ya rasu”
Wata zabura ta yi tace”innalillahi wa inna ilaihirrajiun,
Daddy dama chan bai rasu ba??me ya faru?kiranka ya yi?”.
Ta fad’i hakan ita kanta ba ma ta san ta fad’a ba tsabar rashin sanin tudun dafawa,kar ta yi shiru ya zargeta shiyasa ta zab’i ta yi maganar da ta zo mata.

Wani kalar mahaukacin bugawa zuciyar Daddy ta yi dan tabbas Mommy ta k’ulle kanta da kanta..ta ya aka yi ta san kiransa ya yi?

Jin jina mata kai ya yi yana jin kamar ya shak’e ta ya kashe ta right away,da kyar ya iya cewa”kira na ya yi ya ce in yafe masa yana buk’atar gani na da gaggawa.”

Zuwa yanzu yadda Mommy ta fara gumi ya gama tabbatar masa da komai,dama abunda ya zo tabbatar wa d’in kenan shiyasa ya zo mata a haka,cikin son sake ganin reaction d’inta yace”tun lokacin da ya kira ni ya fara magana gaba d’aya hankalina ya karkarta ne a kan watak’ilan Khadija ma tana raye.”

A take ya ga idanuwanta sun fara ciccikowa da hawaye kamar za ta yi kuka…da kyar bakinta yana wani irin karkarwa ta samu tace”Noo Daddy it can’t be,idan shi ya rayu ita ba zai yiu ta yi rai ba,ko ka manta yadda ita d’in da hannunka fa ka c….”
Yadda taga idanuwansa sun yi jaaa a take ne ya sa ta had’iye maganarta ta sunkuyar da kanta,kafin da kyar ta sake d’agowa tace”amma ban sani ba sai dai mu fara bincikenta,watak’il itanma she made it out alive..saboda ka san dama na gaya maka wajen yadda ya koma ba mu iya detecting ko da biro ba ballantana gawa komai ya kone k’urmus ruwa kawai muka yayyafa aka yi musu salla a haka…..”

Wuff kawai ta ga ya juya ya fita zuciyarsa ta na wani irin tafarfasa dan ya san tabbas idan ya ci gaba da zama to zai iya aikata abun ban mamaki ga Mommy…Mommy ta yi masa abubuwa daban daban tun daga kan yadda ta tilasta masa aurenta har kawo yanzu kullum a cikin b’acin ranta ya ke,amma bai tab’a tunanin za ta iya aikata haka ba,sannan gashi still k’ok’arin b’oyewa amma ya san ta yadda zai kamata dumu dumu yadda zai k’ulleta da jijiyoyin jikinta ya tona mata aisiri kowa ya ganta…hacking wayarta kawai zai yi ta yadda ko typing take yi sai ya gani.A nan ne kawai zai ji komai da take yi ya ga komai ya kamata dumu dumu ya tabbatar da zarginsa a kanta.
He really can’t believe this!he can’t believe Mommy ta saka shi ya kashe Khadijah da hannunsa ba tare da laifin ta ba,dan kamar yadda ita ma Mommy ta fad’a idan mallan lawal ya samu ya yi making out alive ita Khadijah ba ta Isa ta fita da rai ba.

Tabbas kisan kai it’s too easy for Mommy…shi kansa yana jin tsoron abunda zai yi mata Wallahi.





Kasancewar Yassir a napep ya taho ya sanya sai yanzu ya samu ya shigo cikin gidan…..

Yana zuwa a fusace ya haye sama ya nufi d’akin Kausar,zuciyarsa tana wani irin tafarfasa.


Kausar ta na wani irin kuka haka nan ta shiga d’akin ta ta fad’a kan gado…..ta yi kuka a wannan rana kamar ranta zai fita kafin ta mik’e ta fad’a toilet ta shiga wanke fuskarta a ranta kuwa ta gama aiyyanawa “wallahi
daga yau ita ma ta kanta za ta yi farin cikin ta kawai za ta duba!kowa ya yi ya kansa….inshaaAllah sai ta mallaki Yashjub ko ta halin yaya ne,daga nan za ta nunawa Mommy wacece Kausar,sai ta san ta yi betraying d’inta wallahi daga kanta ko d’an aiki ba za ta sake betraying ba.”

Tana wannan lissafin ta fito daga toilet d’in…a d’akin ta tarar da Yasira,cikin rashin kwarin jiki Yassirar ta mik’e ta k’arasa ta ruko hannunta kafin tace “ta zo ne akan ta yi mata gargad’in ta bi Yassir a hankali kar ta bari ya fahimci wani abun gudun kar yaje ya yi mata kwab’a.Dan yadda ya yi mata d’azu a asibiti ita kanta ta d’an tsorata gaskiya”da “to” kawai ta bi ta daganan Yasirar ta juya ta fita dan ta fahimci kamar Kausar d’in ta na buk’atar space.
Tana fita Kausar d’in ta girgiza kai a ranta tace’’kwab’a kuma ta nawa?bayan abunda ya aikata,’’wannan shine karo na biyu da ya so ya kashe Yashjub kuma ta lura Mommy ma ta fahimci wani abun amma ta ga kamar k’ok’ari ma take yi ta b’oye…

A hankali tana jin kanta yana wani irin mahaukacin sarawa
ta nemi guri ta kwanta.
Lumshe idanuwanta tayi
atake hawaye suka shiga sintiri a kan farar fuskarta
Wannan wacce irin rana ce ta risketa?…ga ciki tana d’auke da shi,ga Mommy wadda ta juya mata baya ga kuma Yassir wanda take zargi da wannan
shirmen a karo na biyu
sannan bata Isa ta tunkare sa da maganar ba dan ba ta so ya
fahimci wani abun
Sannan ga rayuwar Yashjub dake a cikin hatsari ga Manubiya ga shi Yashjub d’in ma kansa har yanzu ta kasa samun sa!,ta Ina za ta fara ne?dan abubuwan sun yi mata yawa.

K’arar bud’e k’ofar d’akin nata ta ji da mugun k’arfi dan haka ta tashi a d’an rikice duk da kuwa da ma ta riga ta san waye ne.
A tsaye a bakin k’ofar ta gansa yana huci kafin ya juya ya rufe k’ofar ya murza key tukuna ya nufota gadan gadan…
Duk tsaurin idon Kausar sai da ta tsorata dan haka tun kafin ya k’araso ta mik’e tsaye tana mai gyara doguwar rigar jikinta ta hau inda inda cikin in’ina tace’’Yassir I’m sick dan Allah ka bar….’’
Mahaukacin marin da ya d’auke ta da shi ne ya sanya ta gagara k’arasa maganar tata,sai da numfashinta ya d’auke na y’an seconds tsabar tsananin shock d’in da ta shiga,a rikice ta d’ago fuskarta da ta yi jajir ga shatin y’an yatsunsa sun fito rad’o rad’o a fuskar tata tace ‘’Yassir ni ka mara??’’
Cikin karsashi yace‘’appetizer ne wannan kar ki damu,if you like ki bari in yi miki tambaya ki yi mini k’arya…’’
Ya fad’i hakan yana mai kunce belt d’in wandon sa.
Cikin fushi tace “dukana za ka yi?baka da hankali ne?duk abubuwan da ka yi basu ishe ka ba???’’

Dakatawa ya yi daga nad’e k’asan belt d’in da ya ke yi around his fingers kafin ya d’ago jajayen idanuwansa ya zuba su akanta tukunna yace ‘’abubuwan da na yi?me da me na yi kenan?’’
Ya fad’i hakan cikin matsowa daff da ita yana mai tsare ta da dara daram idanuwansa da suka yi jajir hatta fuskarsa ta yi jaaa tsabar bala’i.

Ahankali ta d’an ja da baya dan a mugun tsorace take dashi
Sai da ta d’an kauda kanta gefe tukunna ta yi k’asa da murya tace’’ Wallahi zan tona maka asiri,in har ka tab’a lafiya ta sai kowa ya san kai ne ka tura y’an fashi estate d’in Yashjub yau’’

Cak!haka ya k’ame,kafin ya juyo da fuskarta cikin karsashi yace ‘’Kausar ni za ki yiwa sharri da borin kunya saboda kinga na kama ki dumu dumu?’’

Ganin yadda jikinsa ya yi sanyi kuma ta ga ta d’an samu galaba a kansa ne yasanya ta fincike fuskar ta tace’’ba iya wannan ba ma Wallahi har tayar motar sa da ka cire kwanakin baya sai na fad’a kowa ya ji ,tun da dama son da nake yi maka ne yasanya nake rufa maka asiri amma in har zaka iya d’aga hannu ka mareni to na san ka daina sona dan haka nima ban ga amfanin ci gaba da son ka Ina bin bayan ka ba ,’’
Ta fad’i hakan tana mai rushewa da wani uban kuka wanda yayi tsananin tasiri akan Yassir.

Ganin kamar so take ta bugi cikinsa sannan kamar wayo take so ta yi masa ne yasanya ya dake yace’’ke!Kausar bana son hauka da shirme da sharri…idan ba so kike in yi miki more than abunda na yi niyyar yi ba to kawai ki bani amsoshina da na zo k’arba mu yi ta ta k’are,”
‘’How dare you!ta ya ma zaki k’ala mini sharri wai ni Ina so in kashe Yashjub! baki da hankali ne?kuma wa kike tunanin za ki gayawa wannan maganar ya yarda?bari ki ji ko Mommy idan kika gayawa wallahi ba za ta tab’a yarda da ke ba,za ki sha mamaki idan ta juya miki baya har abada ,dan babu uwar da za ta yarda wata tazo ta ce mata d’anta yanaso ya kashe d’anta!’’.

Goge hawaye Kausar ta yi ta d’ago ta fuskance sa tukunna tace’’Yassir cewa na yi ‘zan fad’awa kowa kaine ka cire tayar mota sannan zan fad’awa kowa kaine ka saka bomb a estate d’in Yashjub’.A kaff cikin maganata ka ji ta inda nace ‘kana so ka kashe Yashjub’?’’.

Cikin fushi hargagi da hargowa yace’’Kausar zan illataki fa! ni za ki yiwa wasa da tunani?ai indai aka ji kince na cire taya to an san kashe sa nake son yi kenan!’’
Tsit!haka muryarsa ta tsaya chak!yana mai recalculating what he just said yanzun a cikin kwakwalwar sa’’

Kafin ya yi cilli da belt d’in hannunsa tukunna ya d’aga hannu kamar zai damk’i wuyanta kamar kuma wanda ya tuna wani abun sai ya tsaya chak!! kafin ya juya mata baya yana wani irin huci kamar mayuncin zaki….

Wata bahaguwar ajiyar zuciya Kausar ta sauk’e kafin ta d’an matsa garesa tace’’ Bari kaji abunda baka sani ba! Ko da ace Mommy bata tab’a shiga aji ba,wallahi ba zan yi kaffara ba itama ta d’an fahimci wani abun,sakamokon yadda ka dinga k’ok’arin tonawa kan ka asiri tun a crime scene d’in,har sign na dinga yi maka da ido amma sam ka kasa fahimta
Shiyasa ka ga hankalina ya tashi raina ya b’aci,ga kuma rashin lafiyar da take damuna,’’
Ahankali ta sake taku d’aya ta kamo hannunsa ba tare da ta zagaya gaban sa ba ta ci gaba da cewa’’ranar a d’akinka na gaya maka we re on this together,Yassir tunda har na iya danne zuciyata na had’a ka da Munirat inaso ka san na d’auki mission

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login