Showing 204001 words to 207000 words out of 244445 words
kashe mahaifiyata kuma na tuna yadda ko shekara ba a yi ba Daddy yace mana kar wanda ya sake kiran ko da sunanta kuma akwai ranar da na ji yana kuka yana cewa Hajiya mama da ya sani ya tsananta bincike da ya sani bai kunna musu wuta ba.
Shiyasa na fahimci komai na fahimci tabbas duk shirin ku ne ke da Baba larai.
So na yi in tuna muku asiri amma sai na ji kina cewa”shikenan na yarda da ke amma gaskiya ya kamata ki yi Abu mai k’arfi wannan karon a kansu ki sake kafe ta a duk inda take inda Hali ko makwabta kar ta samu jin dad’in shiga saboda wallahi na tsorata matuk’a sannan inaga larai gara kawai in fito in gayawa Yahanasu gaskiya ta san cewa ni ce na haifeta na san za ta fahimceni!kalli fa yadda Khadija take zuwa wajenta a b’oye a matsayin Mahaifiyarta itama kuma ta b’oye mana!
A gaskiya abun ya fara damuna kuma Ina tsoron kar ta girma abun nan da na yi kuma na yi shiru ya yi affecting relationship d’ina da ita”
Ban yarda da abunda kunnuwana suka jiye mini ba sai da na ji Baba larai ta katse ki itama tana cewa”Khadija ki rufa mana asiri kar ki ja mana,kar ki je garin soyayya da k’ulaficin y’ar ki ki je ki tarwatsamu!!Wallahi ko da wasa idan aka san Yahanasu ce y’arki ba Yashjub ba to komai ya lalace mana kenan..kar ki yi tunanin idan kika gaya mata maganar za ta b’uya ni na san dole za ta fito dan haka ki ja bakinki ki yi shiru mu samu mu cimma burinmu tukunna sai mu san abunyi!as far as I know Yahanasu tana gabanki za ki kula da abarki sannan babu wanda zai cutar miki da ita dan haka idan har zan baki shawara ki d’auka to ki ja bakinki ki yi shiru.
And again!yadda kike yi a gaban Daddy ki d’an rage har ma su Yasirar suma ki rage..jiya bakiga shock da mamakin da Daddy ya shiga ba da akace masa kin daki Yasira saboda Yahanasu kuma itama Yasira suna cin abinci ina jinta tana cewa Mommy ta fi son Yaha a kansu!!dan haka ki ja bakinki ki
Iya takunki tun kafin ki tonawa kanki asiri.”
…….
Hawayen da suke zubo mata sharkaff ta sa hannu ta goge kafin ta ci gaba da cewa”Ina jinta tana ce miki kar ki damu ko nan da shekara nawa ne indai kika gaya mini ke ce mahaifiyata ta asali ba zan guje ki ba kuma ba zan ji haushin ki ba,za ta yi mini katanga da mutane saboda gudun kar in yi k’awaye a gaba in fahimci duniya su zuga ni idanuna su waye in fahimci kin zalinci ni.
Sannan za ta rufe mini Baki saboda kar in gaya wa kowa na ga Mama sannan za ta rabani da Mama ba zan nemeta ba ta inda za ta yi mini abunda ba iyaka maman kad’ai ba ban Isa in sake shiga jikin wani har mu yi sirri da su in kasa fad’a miki ba,nan k’arshen kuma tace”za ta yi abunda ke kad’ai za ta bari a jikina bayan ke babu wanda ya Isa ya shiga jikina ya san cikina komai kawai kika ce zan bi ki in karb’a hannu bibbiyu ba zan yi jayayya ba.!
Saboda har abada ba za ki gaya wa Daddy gaskiyar tsakanina da ke ba gudun matsala,so idan kika yi mini haka za ki gaya min ke mahaifiyata ce zan amince in karb’eki
Hannu biyu kuma ba zan gaya wa kowa ba ba zan kuma ji haushi ba!.
Da farko ce mata kika yi a’a amma da ta ci gaba da tsara ki Mommy saboda tsabar son kai da son zuciya tashi d’aya kika amince a yi mini duk wa’ennan abubuwan duk dan kar in tona miki asiri kuma kar in k’i amincewa da ke as mahaifiyata a lokacin da kika gama tsara plan d’inki kika shirya karb’ata kika shirya gaya mini ni y’arki ce.”
Cikin kukan Yahansu ta ci gaba da cewa”sam ba ki yi tunanin hakan da kika yi mini zai iya shiga tsakani na da aure ba!.”ta k’arashe maganar tata cikin tsananin fashewa da kuka kafin ta ci gaba da cewa
“Ina tsaye a wajen Ina kuka har Baba larai ta fito daga d’akin naki ta ganni, na san ta san idan kika ganni a haka kika fahimci na ji komai to za ki karaya ne kuma ta san akwai matsala,shiyasa a wannan lokacin ta toshe mini Baki ta ja ni d’akin ta ta zaunar da ni.
Ita kanta na san a wannan lokacin ta sha mamaki na dan bata yi tunanin na yi wayo har haka ba saboda duk yadda ta so yi mini wayo ni kuma na k’i Bata k’ofa kuma ta fahimci na san komai na kuma gane komai inaga shiyasa ta je ta yi tsafe tsafenta ba tare da ta sanar da ke cewa na ji komai ba.
Na san da ke da ita duk kun d’auka asirinku ne ya yi tasiri a kaina na daina shiga jama’a kamar yadda kuka tsara amma asalin gaskiya Mommy tsanar ki bak’in cikinki da haushinki ne suka maidani na zama abunda na zama har kawo yanzu.
Sai yanzu Mommy ta iya tsayar da kukanta da kyar tace”Yahanasu dan Allah kar ki ce kin tsane ni! Komai da kika ga na yi wallahi duk na yi ne saboda ku!”
Cikin d’an d’aga murya Yahanasu tace”saboda ke dai Mommy!duk abunda kika yi saboda kanki kika yi!!!.
Mommy kina kallo fa tun Ina y’ar k’arama ko jama a idan na gani kuka nake yi hakanan na tsani komai na tsani kowa nima mutane suka tsane ni,
Kina gani yadda aka dinga yawo da ni k’asashen waje dan a gano matsalata na dinga shan wahala daga k’arshe aka ce depression gareni lokacin ko shekaru sha biyu nan Kai ba amma mommy ba ki yi motsin komai ba.
Sau nawa ana fasa d’aurin aurena kin san bani da kowa ba ni da komai amma Mommy haka kike murzawa idanunki toka ba kya zuwa ki dad’e da ni ki ji ainihin matsalata saboda kar a zargeki kar asirinki ya tonu,
a gaban idanunki su Yasira suke yi mini duk wani kalar cin kashi amma sai dai ki zuba ido kawai idan anyi sa’a shine za ki ce musu su daina amma ba ki tab’a tsawatar musu ko kuma ki tsayamini ba.!
Ta ina hakan ya zama ba selfishnesse ba???ta ina hakan ya zamo duk a ta dalilin neman farin cikina ne????”
Yahanasu ta yi mata tambayar cikin d’aga murya.”
Cikin share hawaye ta sake cewa”kuma ko tsafin ma da kuke tunanin shine ya yi tasiri a kaina ba ki tab’a yunk’urin gyarawa ba despite duk wannan wahalwahalun da na sha a rayuwa amma a haka kike tunanin idan kika ce mini ke mahaifiyata ce a gaba zan karb’eki in yafe miki saboda kina tunk’aho kin yi mini asiri ko?”.
Ba ta jira Mommyn ta bata amsa ba tace”Never!!!”
Sannan ta d’aura da cewa”Mama Khadija itace mahaifiyata har gaban abada shiyasa kika ga kawai na zuba miki idanu ban tab’a tunkarar ki da komai ba saboda ban d’auke ki uwa ba!
kamar yadda ba ki damu da ni ba nima haka ban damu da ke ba, na san a baya a lokacin da na ji maganganunku na shiga tashin hankali ga k’arancin shekaru ga kuma no one to talk to amma believe u me wallahi wallahi Mommy yanzu abun ba ya gabana. Alhamdulillah I ‘ve move on Ubangijina ya yaye mini damuwa.”
Cikin sake matsowa daff da ita tana kallon yadda take kuka billhakki da gaskiya tace”Dan haka Ina mai sake gaya miki ki janye maganar tsinuwa sannan ki kirawo Yashjub ya dawo gida cikin family d’insa if not tabbas Mommy za ki yi mamaki na saboda a yadda na ke jin haushi da takaicinki tona miki asiri its the least I can do a halin yanzu.”
Dai dai nan Baba Larai ta turo k’ofar ta shigo a d’an hargitse!
Kallonsu ta yi kamar yadda suma suke kallonta,ta riga ta san Yahanasu ta gama fasa kwai duba da yadda Mommy take kuka kamar ranta zai fita amma ba ta wannan ta ke ba tukunna dan haka ta kalli Yahanasu tace”D’an bamu guri!”
Daga haka ta ja hannun Mommy suka nufi bedroom d’inta.
Had’e rai Mommy ta yi kamar ta turje ta k’i binta sai kuma kawai ta rabu da ita ta yi mata shiru dan tsabar mugun mugun takaici da haushin Baba larai d’in ma ya sanyata ta kasa cewa komai.
Suna shiga Baba larai ta turo k’ofa ba tare da ta damu da yanayin Mommyn ba tace”an yanka ta tashi fa!babu aure tsakanin Kausar da Yashjub!..”
Ba ta jira Mommyn ta tambayeta k’arin bayani ba ta d’aura da cewa”kin san ai kawar musu da lissafin duk wani abun da zai sanya a fasa auren nan muka yi dama,shiyasa kwata kwata ba su yi tunanin ‘ba fa a d’aura aure da ciki ‘ ba.
Ni kaina ban sani ba sai yanzu da na fito zan zo nan na ji suna maganar Abhi da Daddy..wai har wani babban malami suka tambaya ya tabbatar musu da cewa ‘ba a aure da ciki!’
Ban ji bayanin nasu sosai ba dan k’us k’us suke yi a chan corridor na babban balcony kamar harda Hajiya mama suke maganar ta waya,shiyas….”
Cikin katseta Mommy tace”Larai me yasa kika b’oye
mini batun Yahanasu???”
Cikin rashin jin dad’i Baba Larai tace”kash!!!
Ki bar wannan maganar za mu yi ta amma ba yanzu ba yanzu mu ji da wannan ba mu san wani step su Daddy za su d’auka next ba ya kamata mu yi musu shigar sauri!”.
Cikin daka mata tsawa Mommy tace”ni kuma wannan maganar nake so mu yi dan haka ki amsa ni idan na ce miki me yasa kika b’oye min batun Yahanasu sannan me da me kika yi mata? Har ma da ni kaina tabbas kin yi mini abu dan haka ina son jin komai a yau a yanzu ba sai anjima ba idan ba haka ba wallahi za ki sha mamaki na!!”
Numfashi Baba larai ta fesar kafin tace”shikenan tunda kin dage sai kin ji!
Duk abunda na lissafa miki nace ce za mu yi mata shi na yi…”
Cikin tarar numfashinta Mommy tace”Sannan nima kika d’auke hankalina daga kanta ko?saboda akwai abubuwan da kika saka ni na yi kika kuma bani na ci duk sai yanzu kwakwalwata take fassaramin ma’anar su sannnan tun da na yi har yau ban k’ara tunanin fad’awa Yahanasu gaskiya ba!
Dan haka ba na son k’arya da b’oye b’oye larai!! Inaso ki gaya mini gaskiya tun rai na bai gama b’aci da ke ba!!!”.
Ajiyar zuciya Baba larai ta sauk’e kafin tace”Mommy gani na yi kina shirin tona mana asiri ni da ke kina shirin kaimu prison saboda muddin Daddy ya aan mun musanya Yara to
duk wani Abu da muka yi sai ya bnciko ya fito kowa ya gani a hankali a hankali k…”
Marin da Mommy ta d’auke ta da shi ne ya sanya ta yin shiru ta zuba mata jajayen idanuwanta cike da mamaki da shock.
Cikin fushi bak’in ciki da b’acin rai Mommy ta fara magana”a duk tsawon tarayyata da ke ban tab’a ce miki ki je ki yi gaban kanki ki yi kutse cikin rayuwata ki yanke hukuncin da kika ga ya dace miki ba! A tunani na shelter abinci da gatan da na yi miki ya ishi ace kin yi hankalin respecting d’ina da decision d’ina ba tare da kin yi mini shishshigi ba.!”
Cikin fushi sosai itama Baba larai d’in tace”Khadija ni kuma a tunani na na wuce wacce za ki ajjiye hakanan a cikin gidan ki tana yi miki duk abunda kike so kawai kamar wata y’ar aikinki,a tunani na ni yayarki ce shiysa har na yi miki shishshigin da kike magana a kai na yanke hukuncin da na tabbatar it’s for your own best!
Amma tunda duk irin rufin asiri da abubuwan da na yi miki tsawon shekaru sama da talatin duk ba ki gani ba yau ta kai har kin d’aga hannu kin Mareni shikenan!!!ba komai Allah ya had’a fuskokinmu da alkhairi..
Daga haka ta juya ta nufi k’ofa taana tsammanin Mommy za ta tsaida ita amma har ta fice daga d’akin Mommy ko tari ba ta yi ba.
Za ta nemo ta amma bayan ta tafi su daidaita su shirya dan tabbas
Yau kam ba za ta tsayar da Larai ba wallahi,sai ta nuna mata abunda ta yi ba ta kyauta mata ba ta yadda gobe ba za ta k’ara ba,kalli yadda ta saka k’iyayyarta a cikin zuciyar Yahanasu ta dalilin makircinta sannan gashi kwata kwata Yahansun ma ba ta k’aunarta sab’anin yadda Baba larai d’in tace Yahanasu ba za ta iya ko jayayya da ita ba! A tunanin ta aikinsu ne yake ci da ta ga Yahanasun shiru shiru ashe tsana da haushinta ne ya cika mata zuciya shiyasa ta ke yawan yin shiru ba ta kulasu.
Sai da ta tabbata Baba larai ta fice da ga side d’inta gaba d’aya tukunna ta fito daga bedroom d’in nata!kamar yadda ta yi zato ba ta tarar da Yahanasu ba dan haka ta zauna ta yi shiruu ta shiga lissafin ta hanyar da za ta bi ta daidaita tsakaninta da Yahanasu.
Ta fi minti ashirin a zaune su Yasira suka shigo a mugun hargitse suna cewa”ta zo
ta hana Baba Larai tafiya,ga ta chan ta had’a kayayyakin ta tsaff!tun d’azu suke lallashinta amma ta kafe Akan Itafa sai ta tafi kuma sai kuka take yi dan Allah ta zo ta tsayar da ita ta lallasheta maybe Daddy ko Hajiya mama ne suka yi mata wani abun.
Mik’ewa kawai Mommy ta yi ta fad’a cikin bedroom d’inta ta kullo k’ofar wanda hakan ya sanya suka
fahimci matsalar daga wajenta ta taso kenan dan haka kawai suka sauk’a da niyyar su je su ji da Baba larai first tukunna su dawo wajen Mommy su ji dalilin fad’an nasu sai dai suna sauk’a suka tarar da su Yasmeen suna shigowa cikin parlourn suka ce ta riga ta tafi jaka d’aya ma ta samu ta tafi da ita dan sun rik’e ragowar sun hanata ita kuma ta tafi kawai ta bar musu.Sun so su bita amma ba wani Napep d’in nata kuma a baki baki ta zauna ta k’i basu access har aka ja aka yi gaba,kuma kafin su shigo su d’au mota sunsan sun riga sun b’acewa ganinsu……
Duk wannan dramar da ake yi su Daddy suna jin su suka manna musu hauka daga k’arshema garden suka fice suka ci gaba da tattaunawarsu….Daddy ji yake kamar ya fi kowa farin ciki a ransa kuwa addu’a yake yi in shaa Allah Baba larai ta tafi ta bar gidansa kenan har abada next kuma Mommy ce!….Hajiya Mama ta ji dad’i da suka kirata suka gaya mata,tana fushi da su shiyasa yanzu ma kamar d’azu da suka kirata suka gaya mata zancen aure ba ta biye musu ba kawai dai tace”a ci gaba da addu’a”
daga haka ta kashe wayar tana jin sanyi a ranta,in shaa Allah k’arshen Mommy ya zo
kenan sannu a hankali za ta gani ne.
Har yanzu mamakinsu take yi tana mamakin yadda ita kanta su Mommy suka goge mata hadda!!amma ba komai ai gashi nan sun fara gani tun yanzu,kad’an ma suka gani in shaa Allah.
A daren ranar Hajiya Mama ta bi jirgin k’arfe hud’u ta nufi Uk,duk da yadda abubuwa da suka wakana suka yi mata dad’i amma
tana so ta tafi…fushin da ta yi ta ga positive effects d’insa sosai a kan Daddy dan haka ta yanke a kan za ta tafi ta je ta yi ta yi musu addu’a Allah ya sa a dace in shaa Allah Mommy ta kusa ganin k’arshen ta kuma duk wasu abubuwa da ta rufe sai sun bankad’a a idanun kowa ya gani.
Ya’isha tafi kowa gigita da lamarin tafiyar Baba larai dan ta san Baba larai itace gatan su saboda yanzu haka aiki take yi mata a kan Siyama da Najeeb!!shikenan ta san ta shiga ukun ta itakam yanzu..Yasira ma ta gigita sosai dan itama ta san Baba larai d’in dai itace gatan su dan haka da daddare bayan ta bari Mommy ta d’an huce ta je ta sameta cikin son fahimtar da ita ta fara yi mata bayanin illar tafiyar Baba larai a garesu kuma ko ba komai bai kamata ace sun yiwa Baba larai haka ba!ko me kuwa ta yi musu ba ta yi deserving haka daga garesu ba.”
Cikin nuna halin ko in kula Mommy tace”Yasira ba fa ni na cewa Larai ta tafi ba ita da kanta ta yi zuciya ta ce za ta tafi shiyasa ni kuma ban hana ta ba besides abunda ta yi mini ma ya sanya dole in hukuntata in nuna mata iyakar ta dan haka indai na Isa in fad’a miki ki ji to ki tsame hannunki ki gaywa su Yusra ma duk su tsame hannayensu a lamuranta ko waya bana so ku yi mata,Allah na tuba idan banda failure me muke fuskanta aikin nata yanzu duk ya daina ci!”
Cikin mamaki da tsanannin rashin jin dad’in abunda Momyn ta yi ta kuma fad’a yanzu Yasirar tace”idan na fahimceki Mommy a yanzu dai Baba larai ba ta da wani amfani a gareki shiyasa kika b’ige da cewa kinaso ki hukuntata ne saboda na san inda ace a lokacin da Baba larai take ganiyar taimaka miki komai yake tafiya daidai ne to da ko me ta aikata a gareki ba za ki tab’a barinta ta tafi ba,me ye ma ta aikata miki yanzun da ya yi zafi har haka???”
Yasira ta yi mata tambayar cikin b’acin rai.
Mik’ewa tsaye Mommy ta yi ta nuna mata k’ofa tace”get out Yasira tun kafin ran ki ya b’aci!!!
Za ta yi magana ta kuma daka mata tsawa tace “get out nace!!!”
Juyawa kawai Yasira ta yi ta fita ranta a b’ace da takaicin Mommy dan ita a rayuwarta ba ta son mutum mai use and dump kawai idan ana tare to a kasance tare har abada through thick and thin kuma a taimaki juna amma ita Mommy bayaga use and dump d’inma da ta yiwa Baba larai,
tun ba yau ba ta lura da Mommy she’s just looking out for her self kawai using d’insu take