Showing 207001 words to 210000 words out of 244445 words
yi…..
Sai bayan kwana d’aya tukunna Mommy ta je d’akin Yahanasu dan ta san zuwa lokacinta d’an huce.
A zaune ta sameta suna waya da Yashjub tana ganin ta shigo ta yi sauri ta kashe ta ajjiye wayar ba tare da ta kalletaba ta ce”bacci zan yi”
A hankali Mommy ta sauk’e ajiyar zuciya ta nemi guri ta zauna a kusa da ita ta kamo hannuwanta.
Kawar da kai Yahanasu ta yi,tsabar takaici da bak’in ciki ba ta san lokacin da hawaye suka shiga sintiri a kan fuskarta ba.
A hankali tace”na san na yi miki laifi Yaha amma ba laifi na bane ba completely.
Na shirya gaya miki komai in gyara tsakanina da ke amma da Larai ta fahimci hakan gudun kar asirinmu ya tonu sai ta je ta yi abunda ta yi ta kawar da tunanin ki daga gabana if not because of that Yaha da ba zan tab’a bari mu kawo war haka a hakan ba!
Amma yanzu komai zai gyaru Yaha saboda ke da kuma na fahimci Larai ta saka na cuce ki yanzu haka ba ta cikin gidan nan tun jiya saboda ke y’ata.
Na san this is a lot to ask for amma dan Allah ki dubi uwar da aka shiga tsakaninki da ita ba tare da saninta ba ki yi mini adalci ki bani chance Yahanasu….
Mik’ewa da sauri Yahanasu ta yi tace”dan girman Allah ki fita!ba na buk’atar gyaruwar komai a tsakanina da ke Mommy kawai ki bari mu k’arashe rayuwarmu a haka
Me ye ne ma ya rage??
You’ve missed out all the important stages na rayuwata da na fi buk’atar ki dan haka yanzu ban ga amfani idan kin gyara komai ba wallahi,I don’t need you in my life na riga na san ba kya so na ba kya k’aunata kin yi amfani da ni saboda ki samu abunda kikeso which u do dan haka na rok’eki da girman Allah kar ki nemi ki ja ni a jiki saboda ba zan janyu zuwa jikinki ba.
Dan haka kawai ki yi harkar ki nima in yi tawa harkar ba zan tona miki asiriba saboda unlike you idan na yi Abu yana damuna na san kuma duk lalacewa ke mahaifiyata ce dan haka muddin na bada gudummawar na zamo silar tafiyar ki prison to abun sai ya dameni har k’arshen rayuwata shiyasa kawai na zuba miki ido na ke jira Ubangiji ya yi ikonsa a kanki amma fa muddin ba ki daina treatning Yash da tsinuwa ba Wallahi kamar yadda na gaya miki shekaran jiya tabbas zan fad’a masa ba ke ce kika haifesa ba!
Saboda kamar yadda na san guilty conscious zai addabeni idan na fad’i abubuwan da kika yi aka hukuntaki haka zalika guilty conscious zai addabeni idan na bari bak’in cikin ki ya kashe Yashjub dan haka ki daina threatening d’insa!!!
daga nan ni da ke mu ci gaba da treating juna just like before iyakacin abunda nake buk’ata kenan daga gareki ba wai sulhu da fahimtar juna ba!
Kin riga kin cuceni wata shari’ar sai a lahira,Mommy ba wai iyaka hakki na ba wallahi ko da Hakkin Mama khadija kad’ai aka barki ke da Mallan lawal da Baba larai ya isheku…..”
Shiruuu Mommy ta yi haka itama Yahanasu…tun shekaran jiya da Yahanasu ta je d’akin ta ta yi threatening d’inta ta san tsaff za ta iya yin abunda ta fad’a shiyasa ta ke so ta lallab’ata..tana son y’arta kuma ta na so su fahimci juna Sannan da gaske ne Baba larai asiri ta yi mata ta kawar da Yahanasun daga ranta gaba d’aya amma ita Mommy a halin yanzu Babban tashin hankalinta shine kar Yahanasu ta tona mata asiri
Ta ji haushin Baba Larai kuma ta na so ta san ta yi mata laifi ta yadda ba za ta sake yunk’urin yin wani ba shiysa ta barta ta tafi kuma ta hana a nemota amma fa Yahanasu tana daga cikin dalilin da ya sanya ta yiwa Baba larai abunda ta yi saboda tana so Yahanasu ta gani ta san ta yi abu Babba haka duk dan ita sai dai kuma ta lura hakan ko a kwalar rigar Yahanasu gashi a iyaka maganganunta na yanzu ma ta lura Yahanasu fa ta san har case d’in abunda ta aikatawa Khadija….dan haka dole ta d’auki risk ta aikata dukkan abunda za ta iya ta samu ta yi manipulating Yahanasu ta shawo kanta su fahimci juna tun kafin ta b’allo mata ruwa.
A hankali ta ce mata ki zauna mu yi magana Yaha zan fad’a miki duk abunda na yi tare da alk’awarin ba zan sake ba..kuma na san idan kika ji bayani na za ki yi mini adalci idan kika fahimci dukkan nin abubuwan da na yi na aikata su ne saboda ku y’ay’ana.
Yahanasu ba ta zauna ba ganin ba ta da niyyar zaman ne ya sanya Mommy ta fara magana.
“Kamar yadda na fad’a ba zan b’oye miki komai ba saboda Ina so ki yarda da ni mu fahimci juna.
……….Idan ana maganar rashin jituwa da rashin zaman lafiya da rashin so da k’auna to shine asalin zamana da mahaifinku tun lokacin da muka yi aure…ko
Irin soyayyar na ta amarci bai nuna mini ba, k’arshen rashin mutunci da kyara shi Imam ya dinga nuna mini,tunda muka yi aure sam ba ya ja na a jikinsa ba ya nuna mini kulawa.
Ban rufe watanni biyu a gidan Imam ba ya tubure ya dage ya d’agawa kowa hankali shi fa sai ya k’ara aure…sai ya auri budurwarsa wadda na san yana masifar so kamar ransa dan k’iri k’iri ya kan ce mini saboda suna na ya zo d’aya da ita ne dalilin da ya sanya yake d’an kulani.
Babu kalar masifar da ban yi ba amma sai da aka d’aura auren nan lokacin ma da aka d’aura ba na nan ya kaini gidanmu yace a yi mini fad’a Abban mu kuma ya goyi bayansa aka mini horo mai tsanani ta inda aka ce ba zan koma gidan ba Ina ji Ina gani aka yi auren Khadija ta tare suka gwangwaje amarcinsu ni Ina gidanmu hankalina a tashe.
Yadda na fita daga haiyyacina sai da ya bawa mahaifiyata da Hajiya Mama tsoro amma mazajensu suka tsawatar musu aka ce a rabu da ni hakanan sai da na gama shan wahala imam ya gama cin amarcinsa tukunna Abban mu ya ce in koma tare da zazzafan warning d’in idan har ya ji case ya taso daga waje na to na bar Imam kenan har abada ba zai bari in koma gidansa ba.
Ina mutuwar son Mijina ba zan tab’a iya rayuwa babu shi ba gashi ba zan iya zama da kishiya ba shiyasa na shiga tsaka mai wuya na rasa abunyi na rasa tudun dafawa
A wannan lokacin ne larai ta dawo hannun Mahaifiyata da zama (matsayinta na y’ar uwar mahaifiyarta)saboda an samu matsala da ita a k’auyen su an d’aura mata sharrin maita.
Itama tana da damuwa nima Inada damuwa shiyasa muke zama muke tattaunawa…Larai ta tausaya mini sosai haka kurum da na zo komawa tace Tana so za ta biyo ni.
A wannan lokacin da kyar su Abba suka amince saboda Larai a k’alla ta bani shekaru sha biyar kuma suna so in je in zauna lafiya ni kad’ai in yi hankali kar mu je da larai in ga mu biyu ne in yi rashin mugunci..amma sai mahaifiyata tace ba komai mu je kawai saboda ta ga mun shak’u muna d’ebewa juna kewa sannan tunda Larai ta zo ba mu sameta da wata muguwar d’abi’a ba in banda addini da sanin ya kamata da muka santa da shi.
Haka nan aka tambayi Imam ya amince muka tafi gidana tare da Baba larai.
A ranar da na koma ma Imam ba a d’akina ya kwana ba,ko kallona ba ya son yi sai bayan kwana hud’u ya kiramu ya raba mana kwana Akan za mu dinga yin kwana uku uku ni da Abokiyar zama na.
Sai da girki na ya zagayo sau hud’u tukunna ya fara kwana a cikin d’akina saboda da a parlour yake kwana,ko da ya fara kwana d’akin nawa shima kuma babu abunda yake shiga tsakanina da shi sai dare wajajen 12 zai shigo Idan aka kira assalatu kuma ya fita da ga nan ba zan sake saka shi a idanuna ba sai wani daren a cewarsa aiki ya yi masa yawa!
Da gaske na san ba ya gidan tun safe har dare amma kuma sai ranar girkina ne ya ke yin scarce dan duk ranar da aka ce miki yau girkin Khadija ne to tun kafin Magrib yake shigewa d’akinta ba abunda yake fito da su sai sallah da cin abincin dare da ake yi tare daga sun yi isha ya kira ta ba kuma zan sake ganinsu ba sai washegari,haka nan zan yi ta jin hirarsu yana dariya yana raha.
Abun ya ishe ni gashi ban Isa yin rigima ba na san tsaf su Abba za su raba auren ni kuma ba zan iya rayuwa babu shi ba shiyasa na yanke shawarar kashe kaina kawai!!!!…
ranar da zznyi abun Allah ya taimakeni na d’aga kwalbar fiya fiya kenan zan sha Larai ta shigo ganin yadda na firgita ta fahimci ba ni da gaskiya aikuwa tun kafin ta gama dubawa ta gane menene a ciki.
Hankalinta ba k’aramin tashi ya yi ba dan haka ta fito min a mutun k’iri k’iri tace min Itafa ta biyo ni ne saboda tana so za da taimaka mini..
Ba ta b’oye mini komai ba tace a kwai wani boka a k’auyensu mutumin tun yana zuwa mata a mafarki har ta gano location d’insa a wata bukka chan a cikin daji ta je..nan yake sanar mata tun ranar da aka haifeta ya san dama itace za ta gaje sa…
Tun bata d’auki abun serious ba har ta d’auka!!!
bata da uwa sai matar uba dan haka bata yi shawara da kowa ba ta biye masa! ba a yi wata d’aya ba ta koyi kusan komai ya kokkoya mata abubuwa yace ta rik’e da kyau hannunta yana da zafi fiye da zaton mai zato
Akan wata k’awar su da suka yi fad’a ta fara gwadawa matar har yau tana nan a k’auyen su ba ta gani,daga nan sai ta gayawa babbar k’awarta…tun daga ranar duk wani abu da k’awar take so sai da ta yi mata aiki a Kai ta samu!!
A b’oye suke yin abun kuma daga ita sai waenda ta yi trusting shiyasa abun bai baza gari ba.
Amma ta ce mini abu d’aya ne har yau ta kasa yiwa kanta aiki a kai shi ne mijin aure dan ko da ta koma wajen bokan ya koya mata duba da ta duba ranar aurenta ta ga ‘babu!’ hakan bai sa ta yi giving up ba hakanan har gobe take neman mijin aure ido a rufe amma babu shi babu alamarsa.
Ragowar k’awayenta da k’annen k’annen k’awayenta duk sun yi aure kuma ba laifi sun rik’e mata sirrinta ba su fad’awa kowa ba,Mutuwar wannan boka itace ta tona mata asiri dan da ya kusa mutuwa sai ya raba sunanta ma clients d’insa to ta hakane da wata mata ta zo wajenta ta sa ta yiwa d’an kishiyarta asiri ya yi ta rashin lafiya d’aga k’arshe Yaron har ya zo ya rasu..shine fa da bincike ya yi bincike aka ganota aka ce za a k’onata a k’auyen ai mayya ce tunda gashi da ma gata babu miji kuma zan iya ce miki kaff k’auyen mu har yau ba ayi mai kyan larai ba shiysa su kuwa suka ce mata mayya.
Ina gama jin labarinta ko wasi wasi ban tsaya yi ba na amince da tayinta muka fara aiki babu dare ba rana a kan Khadija da Imam.
Ba a yi sati d’aya ba kusan gaba d’aya hankalin Imam ya dawo kaina yaddda yake treating Khadija nima haka yake treating d’ina sai dai kuma ni kaina na san soyayyar Amaryarsa ta daban ce duba da yadda ba ya kishi na kamar yadda yake kishinta dan haka muka sake zage damtse aiki ba dare ba rana ga kuma kissa da muka bawa mahimmanci,dan ko
wani abun aka yi sai dai in shige d’aki in yi kuka in goge daga ni sai larai ba ma tab’a bari wani ya ji ko ya gani…
Haka kurum kwata kwata sai na kasa d’aukar ciki.
Hankalina bai gama tashi ba sai da Imam ya kwashe dukiyar sa gaba d’aya ya damk’awa d’an cikin anaryarsa !!!
dama chan ba so nake yi Yaron ya zo duniya ba saboda Larai ta ce mini tabbas Namiji za ta haifa…dan haka Ina jin wannan batun na jajirce na dinga yiwa Larai kuka har sai da ta taya ni muka kashe Yaron tun yana ciki saboda ita Larai ta ce za ta yi komai amman banda kisan Kai dan shi ya rabota daga garinsu ya kusan tona mata asiri bayaga haka ita har ga Allah ba ta son yin kisa..to kukan da na dinga yi mata da kuma zancen raba dukiya da ta ji ne ya sanya ta biye mini a wanchan lokacin.
Tun daga nan muka k’ara k’aimi akan asirin da muke yiwa Khadija akan ta bar gidan Imam,mu bata ta ci ta sha mu zuba mata a ruwan wanka amma sam abu ya k’i yin tasiri a kanta kwata kwata ba ta ma da shirin tafiya,abun yana kama ta ba wai ba ya kama ta kwata kwata ba kawai dai ba ya yin tasiri a kanta.
A kwana a tashi a haka har muka samu ciki a tare ni da ita…
Tunda muka samu ciikin Larai take aiki Akan ni in haifi Namiji ita kuma ta haihu babu rai kamar yadda ta yi na farko…cikin yana yin watanni biyar Larai ta fahimci Tabbas fa Khadija sai ta haihu kuma Namiji za ta haifa sannan Yaron mai tsananin albarka ne dukkannin abunda ya saka a gaba sai ya cimma kuma attajiri ne mai masifar kud’i sa’a da nasara ta ko wanne angle na rayuwarsa!.
Sai da na suma a tsaye dan hankalina ba k’aramin tashi ya yi ba saboda a ranar ne na lab’e musu na ji Imam d’in yana sake damk’awa cikin jikin Khadija dukiyar sa kamar yadda ya yi a na farko ita kuma tace ba zai you ba shine yace mata to a cikin mu ni da ita duk wadda ta haifi Namiji ita za a bawa shiyasa na nufi wajenta a hargitse dan na San idan muka yi kunnen doki tsaff Imam zai yi son kai.
Shiyasa na nufi wajen larai direct mu samu mu tattauna ita kuma ina shiga
shine ta tare ni da wannan zancen….
Da kyar sai da Larai ta yayyafa mini ruwa tukunna na dawo haiyyaci na da kyar.
Ganin Ina shirin had’iyar zuciya in mutu ne ya sanya tace mini Y not mu musanya Yaran ni in karb’i mai albarkar..tashi d’aya tun kafin ta k’arasa na k’i amincewa na ce kawai a cigaba da aiki a kansa ta yadda ba zai yi albarka ba kuma ya yi rayuwa mara dad’i mara nasara ya mutu wulak’antacciyar mutuwa,tunda mun riga mun san sai fa ya zo duniya.
Wani babban tashin hankalin saida na yi scanning na tabbatar ni mace zan haifa saboda ban tab’a kawowa zan haifi mace ba duba da yadda muka dinga aiki a akan in haifi Namiji.
A wannan lokacin ma Baba larai ce ta sake bani shawara kamar farko a kan mu musanya Yaran idan bayan mun haihu an bayar da dukiyar idan ma kashe Yaron za mu yi sai mu yi tunda dai Yaro yana a hannunmu ai tsaf za mu iya yin kome muka ga dama sab’anin yanzu da yake a ciki.
Tashi d’aya na amince dan na gamsu kuma na fahimta…tun a lokacin muka san yadda muka yi muka siye likitan da muke zuwa asibitin wajensa ta hanyar yarda da shi da Baba Larai ta yi bayan ya fad’i mana hakan kawai yake da buk’ata daga garemu.
A ranar da na fara labour muka bata magani itama muka tayar mata da labour ta hanyar ba ta kwayar da ya bamu a ruwa ta sha ba tare da ta sani ba.
Tana shiga d’akin haihuwa gudun kar ta fahimci wani abun aka shak’a mata anesthesia aka yi mata cs
Kusan a tare muka haihu
Ita aka fito mata da Yashjub ni kuma na haifoki Likitan da nurse d’in da Baba larai suka yi sauri suka sauya aka fitar da ke a matsayin Y’ar da ta haifa ni kuma bayan y’an mintuna aka fitar da Yashjub aka ce na haihu.
Daddy ya bada rabin dukiya kamar yadda ya yi alk’awari amma fa ba ni da burin mallakar wannan dukiya kamar yadda nake da burin kashe Yashjub saboda kwata kwata ko fuskarsa ba na son kalla gashi aka tilasta mini hakanan Ina ji Ina gani na dinga shayar da shi.
Kwatsam!!ina ta shirye shiryen yadda za a yi in raba shi da duniya ba tare da kowa ya zargemu ba sai ga ciki a jikina cikin y’an biyu mai wahalar laulayi.
Tun cikin yana da watanni hud’u Baba Larai ta fara mafarkai marasa dad’i game da Yaron da zan haifa..Tabbas mun fahimci Namiji ne kam wannan karon ammafa Yaron kwata kwata bashi da albarka ga kuma mutuwa da zai yi wulak’antacciya idan har bai yi arzik’i ba!!! sannan duk abunda ya soma to ba zai yi albarka ba…hankalina ba k’aramin tashi ya yi ba dan sai da jini na ya hau na kwanta a asibiti sau bakwai saboda wannan duba da Baba larai ta yi ta gano mini bala’i..sai da muka nutsu muka yi lissafi Sosai muka bincika tukunna muka gano Ashe asirin da muka yiwa Yashjub tun kafin ya zo duniya ne ya fad’a a kan Yassir tunda asirin an yi sa ne a d’an Khadija matar Imam kuma kinga nima sunana Khadija sannan ko bayan da muka fahimci abun bai kama Yashjub ba bamu damu mu yi wani abun a kai ba dan kwata kwata ba mu kawo cewa zai fad’a kan Yassir ba bayaga haka babu ma ta yadda za a yi mu karya abun saboda ba zamu iya nemosaba dan a babban ruwa mai tafiya muka jefa dan haka kinga la shakkah ba ma ya cikin Nigeria ya bi ruwa.
Babu abunda ba mu yi ba babu abunda bamu gwada ba amma idan muka yi