Showing 36001 words to 39000 words out of 244445 words

Chapter 13 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16456

ake jan numfashi da kyar ne ya sanya ta hak’ura,dan makwafta har sun fara shigowa,shiyasa suka yi musu sallama tare da fatan alkhairi bayan sunce”rana ita yau by this time inshaaAllah za su dawo su d’auki amarya su.

Hakanan aka rabu cikin mutunta juna,yayinda su Siyama Jidda da Aisha da Muhsin su ka yi musu rakiya da tray tray na pepper chicken daughnuts chin chin meatpie cakes da drinks…



Tunda suka zo ya yi parking ya kashe motar ya fara addu’a Allah ubangiji ya sa yau ma ya ganta….indai ya samu suka had’u yau to sai ya karb’i number ta,shi kad’ai ya san wahalar da ya sha a cikin watannni ukun nan,da tunanin ta yake kwana yake tashi. Kunyar Yashjub yake ji shiyasa ya gagara ce masa ya karb’a masa numberta a wajen Manubiya……MANNUBIYA
(Book 2)
Page 13
Na
Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.

Tunda suka zo ya yi parking ya kashe motar ya fara addu’a Allah ubangiji ya sa yau ma ya ganta….indai ya samu suka had’u yau to sai ya karb’i number ta,shi kad’ai ya san wahalar da ya sha a cikin watannni ukun nan,da tunanin ta yake kwana yake tashi. Kunyar Yashjub yake ji shiyasa ya gagara ce masa ya karb’a masa numberta a wajen Manubiya……


Yana cikin wannan tunanin ya ga sun fito ita da Jidda ririk’e da trays na gifts,da sauri ya yi wuff ya fice gudun kar ma su nufi wata motar da ba ta shi ba,yana fita suka hangoshi kuma sun gane sa Abokin Yash ne shiyasa suka nefesa da niyyar gaidashi sannan su saka gifts d’in a motarsa.
Kafin su k’arasa su Hajiya mama suka fito kare da waya a kunnenta wadda kallo d’aya zaka yiwa fuskarta ka fahimci tana cikin tsananin tashin hankali,da sauri duk d’insu suka nufi Najeeb dai dai suma su Siyama sun iso kenan.

Da sauri mom tace”Najeeb!hurry up and call Yash ku fara nema mana flight za mu wuce,Na’ima ta yi accident!”
Ta fad’i hakan tana dialing number Abhi kafin ta kara wayar a kunnenta.
Da sauri duk suka ce”subahanallah!”a gigice

Da sauri Najeeb d’in ya zaro waya ya fara k’ok’arin kiran Yash tukunna ya juya ya bud’ewa su Siyama gidan baya suka ajjiye gifts d’in….
Cikin rashin jin dad’i su Aisha suka shiga yi musu jaje dukda ba su san wacecen Na’iman ba,tare da add’uar Allah ya kare gaba.
Sai da suka ga tashin motocin su tukunna suka juya suka nufi cikin gidan.


Already su Hajiya mama suna da visa d’insu a hannu shiyasa suka ci sa’ar samun flight dan a ranar suka samu na dare. K’arfe 3:00am daidai jirginsu ya d’aga gaba d’ayansu har da Abhi suka wuce uk.Su Yasira ba k’aramin dad’i suka ji ba dan atleast sun rage zafi,Ummi kuwa kamar za ta yi kuka…ta so ta bi su amman kuma in aka ce itama sai an nema mata visa tukunna za su tafi to za ta b’ata musu lokaci,shiyasa ta hak’ura akan inshaaAllah za ta je ta ga jikin Na’iman in an shirya mata komai.

Mommy ce ta zauna a asibiti tare da Kausar dan suna zuwa aka basu gado sakamokon jininta da suka ga ya yi mahaukacin hawa.

12:00am daidai Kausar d’in ta farka lokacin duk su Yassira sun tafi,tun da ta farka kuwa sam ta k’i yarda ko da had’a idanu ne ta yi da Mommyn,babu kalar lallashin da Mommy ba ta yi mata ba amma ta k’i kulata hakanan ta hak’ura ta mik’e ta fita ta je ta kira Dr aka zo aka shiga dubata.

Ko bayan fitar Dr d’in ma Mommy ci gaba da lallashin Kausar ta yi amman ko arzik’in kallo ba ta samu daga gareta ba.

Suna zaune a haka kira ya shigo wayar Mommy ganin sunan me kiran nata ne ya sanya ta saurin d’auka cike da
mamaki dan lokacin 2:00 ya wuce tace”Yasira har yanzu ba ku yi bacci ba?”
Cike da farin ciki Yasirar tace mata”Hajiya mama sun wuce,yanzun Yash ya tafi kai su airport gaba d’ayansu”.

Sai da Mommy ta tashi tsaye dan ba kad’an ba ta ji dad’in zancen Yassira tukunna tace”haka kurum suka tafi,Ina Larai?bata wayar….”

Sun jima sosai suna magana da Baba Larai….tukunna suka yi sallama,ta kashe wayar tana jin wani sanyi yana ratsata a ranta tace”inshaaAllah daga yanzu mun fara samun nasara akan duk wani mak’iyinmu kenan da izinin Allah.”

Ajiyar zuciya ta sauk’e tukunna ta koma kusa da Kausar ta zauna ta kamo hannunta kafin ta fara magana”Kausar a cikin kwana biyun nan da suka wuce kin b’ata min rai matuk’a dan ban tab’a tunanin zaki gaya min abunda kika fad’a ba…duba da yadda na rufe idanuna na ke bin bayanki a ko Ina sannan akan komai.Wallahi Allah Kausar yadda nake jin su Yassira haka nake jin ki a cikin zuciyata,kuma ko da ace su d’in ne a cikin situation d’in da kike ciki dole haka zan zuba idanu in hak’ura saboda babu yadda za mu yi.
Baba Larai ta yi iyakar bakin k’ok’arinta nima na yi amman abunda muke so d’in bai faru ba kuma tace ba ta da yadda zata yi no way out,ya kike so mu yi?”
Ba ta jira jin amsarta ba ta d’aura da cewa”na fad’a miki zan kuma sake fad’a miki cewa ki yi hak’uri a yi auren nan!
Bayan auren inshaAllah da ni da ke da su Yassira da baba larai za mu taru mu kwatar miki Yash,kuma na yi miki alk’awarin ba zan bari ki zauna da kishiya ba dan kafin ma ki shiga gidan na san ta dad’e da fita.
Amman fa idan kina so hakan ta faru dole sai kin kwantar da hankalinki kin nutsu kin yarda da mu an taru an yi abu d’aya tukunnan za mu taru mu taimaki juna.
Ban san me kike ji ba amman na san na fiki k’in auren nan,saboda ba ki san abunda auren ka iya janyomin ba shiyasa nake so ki yarda da ni saboda ko dan kai na ba zan tab’a barin Yarinyar nan ta yi lasting a gidan Yashjub ba dan zaman ta a tare da mu barazana ne ga duk wani farin ciki na da gata na.

Ahankali Kausar ta share hawayen ta tukunna tace”inshaaAllah Mommy zan yi yadda kike so.Sannan ki yi hak’uri da abunda na fad’a miki b’acin raine ya janyo hakan ba zan sake ba.”

Wani sanyi ne ya lullub’e Mommy tashi d’aya ta mik’e ta koma kan gadon ta yi hugging Kausar tace”that’s my girl….”
Daga nan ta ci gaba da kwantar mata da hankali tana yi mata nuni da yadda suka fara samun galaba a kan Yash ga shi Hajiya mama ma ta tafi, ta yi hak’uri ta bi komai a hankali za su yi nasara bi’izinillahi.

Jinjina kai kawai Kausar d’in take ta yi alamun fahimta,amma a ranta ta riga ta gama tsara ‘za ta bawa su Mommy second chance,za ta basu one month dukda tana jin kamar ba za ta iya bari a gaban idanunta Yash ya tare da wata ba amman za ta kwatanta fatanta shine Allah ya sa ta iya d’in.
After that one month indai har Manubiya ba ta bar gidan Yash ba to za ta bi ta ko wacce hanya ta fitar da ita,ko dai ta fitar da ita da ranta ko kuma a fitar da gawar ta…..



Kwanan Abhi shida a Uk ya dawo Nigeria…..jikin Na’ima da sauk’i Alhamdulillah ba ta samu buguwa ko wani serious internal injury ba ta dai karye a k’afa ta kurje a hannu.Kuma shima Alhamdulillah abun ya zo da sauk’i ga kuma kwararrun likitoci a kanta….Ummi ta so zuwa kafin biki ko da kwana d’aya ne ta yi ta juyo,Daddy ma da farko tashi d’aya ya amince yanata murna ya cewa Yash ya biya musu kud’in jirgi ita da Mommy su tafi su je su yi kwana d’aya su dawo,cikin murna Ummi ta ci gaba da shirye shiryenta amman washegari da safe Daddy yana tashi ya ce babu inda za su je,da ta bishi d’aki domin ta sake rok’onshi ma sai ya rufeta da fad’a dan haka dolenta ta hak’ura ta fito ta kyaleshi da daddare ta sanarwa mom sun fasa zuwa,mom da hajiya maman ne ma suka d’an kwantar mata da hankali dan ba kad’an ba ranta ya b’aci.



Sosai Manubiya take karb’ar gyara dan mama da anty umma sun dage sosai,inna da Baba har ma da su Manubiyan sun ji dad’i kwarai akan yadda anty umma ta shigo jikinsu itama dan da ita ake yin komai na bikin ta tsaya tsayin daka,atleast sunsan an samu nasara sab’anin da da kowa takanssaa kawai yake yi,kuma suna addu’ar Allah ubangiji ya wayar da kan ragowar suma a samu a had’a kai a yi zumunci,dukda kuwa ba su hango alamar hakan daga garesu ba amman Allah suka ce!dan duk yadda ake ta kururuwar shigowa ganin lefen Manu kaff cikin matan uncle da baba habu babu guda d’aya da ta lek’o ko su ko y’ay’ansu.

Aisha da su Mama so sukayi sai washegari da safe idan aka d’aura aure tukunna su had’a da gadon da aka siya da su flask da kayan lefe su kai gidan
amarya duk a lokaci d’aya, amma yadda unguwar ta d’auka aketa zancen lefen da tsadar kayan da gwalagwalan ciki ne yasanya suka yanke shawara…..Aisha ta kira Yahanasu ta zo a take suka kwashe lefen kaff da ragowar kayayyakin da za’a tafi da su suka kai gidan amrya dan ya fi security….gadon ma dan sun samu matsala ne amma da tuni ankai, 3 months ago suka je suka zab’a sai suka barshi a wajen,to shekaran jiya suna zuwa d’auka me wajen ya hau kame kame,wai su yi hak’uri an yi order wasu yau da daddare za su k’araso shiyasa last month da ya samu mai siya ya siyar,amma kar su damu exactly irinsu d’aya kuma yau cikin dare kayan za su iso su yi hak’uri su jira dan Allah……..


……Aisha tana dawowa daga gidan amarya ta haukacewa su Siyama…labarin gidan take basu tana maimaitawa amman gani take yi kamar ba za su tab’a fahimtar kyan gidan ba sai sun gani a ido,shiyasa daga k’arshe ta hak’ura ta yi musu iyaka bayanin da za ta iya ta mik’e ta fita ta barsu ta tafi gurin su anty umma da suke ta rabon abincin sadaka na walima dan basu yi taro ba iyaka girki aka yi mai uban yawa aka kai asibiti da gidan marayu yanzun kuma ake rabawa almajirai…

…Suna zaune su uku a d’aki jidda Siyama da Manubiya lokacin k’arfe biyar daidai na yamma kowa ya gaji da hada hada,Muhsin ya shigo ya cewa Manubiya “wai ta je kaka mallan yana kiranta.”

Dariya Siyama ta yi kafin tace”tsohon nan fa neman shiri yake w,jiya Ina jinsa yana cewa ya Musbah wai yanayin tsarin bikin ya burgesa ai dama ba a so a yi ta kid’e kid’e a biki albarkar ake kwashewa.Ko wa ya tambayesa oho.”

Murmushi Manubiya ta yi hakama Jidda daga haka Manubiyan ta mik’e ta gyara zaman 3D vail d’in da ta rufa akan tsaddaden lace d’in da ke a jikinta tace musu”bara in je in dawo”

Tana fita Jidda ta kalli Siyama tace”har yau kema ba ki ganshi ba?”

Jinjina kai Siyama ta yi kafin tace”kema kin cika damuwa wallahi,da kyar ma idan Muhsin d’in ba tsokanar ki yake yi ba dan ni Wallahi ko kyallin ya Yusuf ban gani a cikin gidan nan ba.Besides idan ma ya dawo ai shi ya sani ke ina ruwanki?”

Wata nannuyar ajiyar zuciya Jidda ta sauk’e kafin tace”ba wasa Muhsin yake yi ba,d’azunnan na ji inna tana gayawa Baba wai ya bita har d’akin ummanku yayi mata murnar warkewarta da Allah ya sanya alkhairi.”
Ahankali ta sauk’e numfashi kafin ta ci gaba da cewa” Siyama ya Yusuf ba alkhairi bane ba Ina tuna yadda ya tsundumamu a bala’i kwanakin baya shiyasa kika ga duk na tsure kuma inajin tsoro kar Baba ya aura masa ni…”
Da sauri Siyama ta katse ta tace”a’uzubillahi,Jidda dan Allah kar ma ki fad’a wani ya ji,inshaaAllah ya Yusuf ba shine mijin ki ba,sannan ki kwantar da hankalinki da yardar Allah ba abunda ya Isa ya yi muku”.

Shiruu kawai Jidda ta yi dan ita gaba d’aya kwana biyun nan sai a hankali tunda Muhsin ya ce mata yaga ya Yusuf shikenan gaba d’aya hankalinta ya yi masifar tashi,jiya kuma tsautsayi ya sanya ta ta shigo d’akin lokacin mama tana ciki suna waya da Al’ameen,kuma wayar maman irin me muryar nan ce shisysa ta jiyo dadd’ad’ar muryarsa rad’au…after abunda Ammi ta yi musu da kuma yadda shi kansa Al’ameen d’in
ya yi watsi da ita sam bata yi tunanin za ta ji haka dangane da shi ba dan tun jiya da ta ji muryarsa suna waya da Mama shikenan komai nata ya tsaya chak!lissafinta wayonta fushin da tayi da shi da komai tashi d’aya duk ya tsaya chak ta ji ita kawai all she needs and want is him!him alone nothing more….tun jiya take k’okarin ta yi controlling kanta ta b’intike tunanin Al’ameen a ranta smma ta gagara,shiyasa tashi d’aya tausayi da haushin kanta suka lullub’eta ga kuma fargabar had’uwarta da ya Yusuf….
Tunanin nan da take yi ne ya janyo har ba ta san lokacin da ta fashe da wani irin kuka ba.
Da sauri Siyama ta matso ta dafa ta tace”subahanallah Jidda lafiya kuwa,wai duk akan Yusuf d’in dai??”
Girgiza kai Jidda tayi,cikin son ragewa kanta damuwa tace”Siyama Al’ameen bai kyauta min ba,ki duba ki ga yadda ya watsar da al’amurana,da ya san ya daina sona ai kamata ya yi ya fito fili ya gaya min ba wai ya share ni ba,ba abunda ya fi b’ata min rai irin yadda ya san ya bani waya kuma nasan ya kira ya ji shiru amma har yau sama da watanni biyar bai damu ya san me ya faru ba,Ina raye ko bana raye sam shi ba damuwarsa bane..”
Kukan da ya taho mata ne ya sanya ta kasa ci gaba da magana,
shiruu Siyama ta yi tana jiyo tsananin k’auna da son Al’ameen k’arara a cikin zantukan Jidda,dan haka ahanakali ta shiga rarrashinta dan ta ma rasa ta Ina za ta fara nuna mata ‘hakan fa ba daidai bane ba!”.
Sun jima Siyama tana aikin lallashi kafin dakyar tukunna aka samu Jidda ta yi shiru.
Siyama tanaso Jidda ta d’an huce kafin su yi maganar Al’ameen shiyasa ba ta sake yin maganar ba,instead sai ce mata ta yi”am…ni kam Jidda ko kin san abunda yake damun ya Musbah?naga gaba d’aya ya chanza tun watanni uku ko ma ince hud’u baya gaba d’aya na lura a fusace yake kuma kamar haushin kowa yake ji,ko dai matar sa yak….”
Cikin katseta Jidda tace”tab! Allah ya kiyaye”
Dariya Siyama ta yi kafin tace”kar dai ki yi halin dangin miji,indai har yanzu yana son abarsa a ganina gara kawai ku bashi shawara ya dawo da itan…”

“Hmm”kawai Jidda tace daga nan bata sake cewa komai ba,dan ta san inda ace ita kanta Siyama ta san me Baraka ta yi da ko zancen ta ba za ta sake yi ba….


Manubiya tana zuwa wajen kaka mallan ya karb’eta hannu bibbiyu abunda bai tab’a yi ba,tunda Manubiya take bata tab’a sanin cewa kaka mallam yana da wannan hankalin kuma ya san me yake yi ba sau yau
Dan nasiha yayi mata mai ma’ana da tsananin ratsa jiki har sai da ya sakata kuka…..MANNUBIYA
(Book 2)
Page 14
Na
Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.


Manubiya tana zuwa wajen kaka mallan ya karb’eta hannu bibbiyu abunda bai tab’a yi ba,tunda Manubiya take bata tab’a sanin cewa kaka mallam yana da wannan hankalin kuma ya san me yake yi ba sai yau
Dan nasiha yayi mata mai ma’ana da tsananin ratsa jiki har sai da ya sakata kuka,kafin ya sallameta yanata saka mata albarka.


Kamar yadda ta fita ta bar su Jidda a zaune haka ta shigo ta same su,sallama kawai ta yi suka amsa daga haka ta nemi guri ta zauna,suna ganin idanunta suka fahimci kuka ta yi,sun san idan suka fara bata hak’uri sake b’arkewa za ta yi da wani kukan shiyasa suka ja bakunan su suka yi shiru amma dukda haka ba su tsira ba dan kamar wadda aka daka hakanan ta fashe musu da kuka tashi d’aya. Hakan ya yi dai dai da shigowar su Aisha da anty umma da Mama da inna cikin d’akin,ahankali Aisha ta zauna a kusa da ita ta kamo hannunta tukunna tace”haba mana Manu kanki fa zai yi ciwo ki yi hak’uri haka nan mana,ke ki godewa Allah ma a garin za ‘a ajjiyeki waenda ake d’aukar su a kaisu wani garin daban su kuma su ce me??”

Cikin karb’ar zancen anty umma tace”wasu ma k’asar gaba d’aya ake bari da su kuma haka suke zuwa su zauna su rayu,ke kam gidanki ko da k’afa idan mutum ya zage tsaf zai je,ki yi hak’uri ki yi shiru karki ja wa kanki zazzab’i dama indai sunan ki mace to wannan rana tana jiranki……mu kanmu sai hankalinmu ya fi kwanciya idan muka kai ki d’akinki gobe inshaaAllah fatanmu shine ki yi biyayya ki nuna cewa mun baki tarbiyya mai kyau.”

Kamar zuga Manubiya sukeyi haka ta sake fashewa da kuka shiyasa suka hak’ura suka kyaleta anty umma suka fita ita da inna dan su ci gaba da shirye shiryen gobe Mama kuma Ammi ta kirata tace ta zo ta taya ta girki tana da bak’on cikin dare.

Suna fita d’akin ya rage daga Manubiya sai Aisha
Siyama da Jidda,sai da Aisha ta lallab’a Manu ta yi shiru da kyar tukunnan ta bud’e mata abunda ta shigo mata da shi
a flask ta bata tace “ta ci.”

Har ga Allah kayan nan sun fara Isar Manu dan wani irin ciwon mara take yi amma ta san ba ta Isa ta cewa Aishar A’a ba shiyasa ta hak’ura da kyar ta danna tana ji kamar za ta yi amai marar ta kamarza ta fashe.

Ahankali ahanakali Aisha ta samu ta d’an kwantar mata da hankali

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login