Showing 141001 words to 144000 words out of 244445 words

Chapter 48 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16442

yadda zai k’ulleta da jijiyoyin jikinta ya tona mata aisiri kowa ya ganta…hacking wayarta kawai zai yi ta yadda ko typing take yi sai ya gani.A nan ne kawai zai ji komai da take yi ya ga komai ya kamata dumu dumu ya tabbatar da zarginsa a kanta.
He really can’t believe this!he can’t believe Mommy ta saka shi ya kashe Khadijah da hannunsa ba tare da laifin ta ba,dan kamar yadda ita ma Mommy ta fad’a idan mallan lawal ya samu ya yi making out alive ita Khadijah ba ta Isa ta fita da rai ba.

Tabbas kisan kai it’s too easy for Mommy…shi kansa yana jin tsoron abunda zai yi mata Wallahi.





Kasancewar Yassir a napep ya taho ya sanya sai yanzu ya samu ya shigo cikin gidan…..

Yana zuwa a fusace ya haye sama ya nufi d’akin Kausar,zuciyarsa tana wani irin tafarfasa.


Kausar ta na wani irin kuka haka nan ta shiga d’akin ta ta fad’a kan gado…..ta yi kuka a wannan rana kamar ranta zai fita kafin ta mik’e ta fad’a toilet ta shiga wanke fuskarta a ranta kuwa ta gama aiyyanawa “wallahi
daga yau ita ma ta kanta za ta yi farin cikin ta kawai za ta duba!kowa ya yi ya kansa….inshaaAllah sai ta mallaki Yashjub ko ta halin yaya ne,daga nan za ta nunawa Mommy wacece Kausar,sai ta san ta yi betraying d’inta wallahi daga kanta ko d’an aiki ba za ta sake betraying ba.”

Tana wannan lissafin ta fito daga toilet d’in…a d’akin ta tarar da Yasira,cikin rashin kwarin jiki Yassirar ta mik’e ta k’arasa ta ruko hannunta kafin tace “ta zo ne akan ta yi mata gargad’in ta bi Yassir a hankali kar ta bari ya fahimci wani abun gudun kar yaje ya yi mata kwab’a.Dan yadda ya yi mata d’azu a asibiti ita kanta ta d’an tsorata gaskiya”da “to” kawai ta bi ta daganan Yasirar ta juya ta fita dan ta fahimci kamar Kausar d’in ta na buk’atar space.
Tana fita Kausar d’in ta girgiza kai a ranta tace’’kwab’a kuma ta nawa?bayan abunda ya aikata,’’wannan shine karo na biyu da ya so ya kashe Yashjub kuma ta lura Mommy ma ta fahimci wani abun amma ta ga kamar k’ok’ari ma take yi ta b’oye…

A hankali tana jin kanta yana wani irin mahaukacin sarawa
ta nemi guri ta kwanta.
Lumshe idanuwanta tayi
atake hawaye suka shiga sintiri a kan farar fuskarta
Wannan wacce irin rana ce ta risketa?…ga ciki tana d’auke da shi,ga Mommy wadda ta juya mata baya ga kuma Yassir wanda take zargi da wannan
shirmen a karo na biyu
sannan bata Isa ta tunkare sa da maganar ba dan ba ta so ya
fahimci wani abun
Sannan ga rayuwar Yashjub dake a cikin hatsari ga Manubiya ga shi Yashjub d’in ma kansa har yanzu ta kasa samun sa!,ta Ina za ta fara ne?dan abubuwan sun yi mata yawa.

K’arar bud’e k’ofar d’akin nata ta ji da mugun k’arfi dan haka ta tashi a d’an rikice duk da kuwa da ma ta riga ta san waye ne.
A tsaye a bakin k’ofar ta gansa yana huci kafin ya juya ya rufe k’ofar ya murza key tukuna ya nufota gadan gadan…
Duk tsaurin idon Kausar sai da ta tsorata dan haka tun kafin ya k’araso ta mik’e tsaye tana mai gyara doguwar rigar jikinta ta hau inda inda cikin in’ina tace’’Yassir I’m sick dan Allah ka bar….’’
Mahaukacin marin da ya d’auke ta da shi ne ya sanya ta gagara k’arasa maganar tata,sai da numfashinta ya d’auke na y’an seconds tsabar tsananin shock d’in da ta shiga,a rikice ta d’ago fuskarta da ta yi jajir ga shatin y’an yatsunsa sun fito rad’o rad’o a fuskar tata tace ‘’Yassir ni ka mara??’’
Cikin karsashi yace‘’appetizer ne wannan kar ki damu,if you like ki bari in yi miki tambaya ki yi mini k’arya…’’
Ya fad’i hakan yana mai kunce belt d’in wandon sa.
Cikin fushi tace “dukana za ka yi?baka da hankali ne?duk abubuwan da ka yi basu ishe ka ba???’’

Dakatawa ya yi daga nad’e k’asan belt d’in da ya ke yi around his fingers kafin ya d’ago jajayen idanuwansa ya zuba su akanta tukunna yace ‘’abubuwan da na yi?me da me na yi kenan?’’
Ya fad’i hakan cikin matsowa daff da ita yana mai tsare ta da dara daram idanuwansa da suka yi jajir hatta fuskarsa ta yi jaaa tsabar bala’i.

Ahankali ta d’an ja da baya dan a mugun tsorace take dashi
Sai da ta d’an kauda kanta gefe tukunna ta yi k’asa da murya tace’’ Wallahi zan tona maka asiri,in har ka tab’a lafiya ta sai kowa ya san kai ne ka tura y’an fashi estate d’in Yashjub yau’’

Cak!haka ya k’ame,kafin ya juyo da fuskarta cikin karsashi yace ‘’Kausar ni za ki yiwa sharri da borin kunya saboda kinga na kama ki dumu dumu?’’

Ganin yadda jikinsa ya yi sanyi kuma ta ga ta d’an samu galaba a kansa ne yasanya ta fincike fuskar ta tace’’ba iya wannan ba ma Wallahi har tayar motar sa da ka cire kwanakin baya sai na fad’a kowa ya ji ,tun da dama son da nake yi maka ne yasanya nake rufa maka asiri amma in har zaka iya d’aga hannu ka mareni to na san ka daina sona dan haka nima ban ga amfanin ci gaba da son ka Ina bin bayan ka ba ,’’
Ta fad’i hakan tana mai rushewa da wani uban kuka wanda yayi tsananin tasiri akan Yassir.

Ganin kamar so take ta bugi cikinsa sannan kamar wayo take so ta yi masa ne yasanya ya dake yace’’ke!Kausar bana son hauka da shirme da sharri…idan ba so kike in yi miki more than abunda na yi niyyar yi ba to kawai ki bani amsoshina da na zo k’arba mu yi ta ta k’are,”
‘’How dare you!ta ya ma zaki k’ala mini sharri wai ni Ina so in kashe Yashjub! baki da hankali ne?kuma wa kike tunanin za ki gayawa wannan maganar ya yarda?bari ki ji ko Mommy idan kika gayawa wallahi ba za ta tab’a yarda da ke ba,za ki sha mamaki idan ta juya miki baya har abada ,dan babu uwar da za ta yarda wata tazo ta ce mata d’anta yanaso ya kashe d’anta!’’.

Goge hawaye Kausar ta yi ta d’ago ta fuskance sa tukunna tace’’Yassir cewa na yi ‘zan fad’awa kowa kaine ka cire tayar mota sannan zan fad’awa kowa kaine ka saka bomb a estate d’in Yashjub’.A kaff cikin maganata ka ji ta inda nace ‘kana so ka kashe Yashjub’?’’.

Cikin fushi hargagi da hargowa yace’’Kausar zan illataki fa! ni za ki yiwa wasa da tunani?ai indai aka ji kince na cire taya to an san kashe sa nake son yi kenan!’’
Tsit!haka muryarsa ta tsaya chak!yana mai recalculating what he just said yanzun a cikin kwakwalwar sa’’

Kafin ya yi cilli da belt d’in hannunsa tukunna ya d’aga hannu kamar zai damk’i wuyanta kamar kuma wanda ya tuna wani abun sai ya tsaya chak!! kafin ya juya mata baya yana wani irin huci kamar mayuncin zaki….

Wata bahaguwar ajiyar zuciya Kausar ta sauk’e kafin ta d’an matsa garesa tace’’ Bari kaji abunda baka sani ba! Ko da ace Mommy bata tab’a shiga aji ba,wallahi ba zan yi kaffara ba itama ta d’an fahimci wani abun,sakamokon yadda ka dinga k’ok’arin tonawa kan ka asiri tun a crime scene d’in,har sign na dinga yi maka da ido amma sam ka kasa fahimta
Shiyasa ka ga hankalina ya tashi raina ya b’aci,ga kuma rashin lafiyar da take damuna,’’
Ahankali ta sake taku d’aya ta kamo hannunsa ba tare da ta zagaya gaban sa ba ta ci gaba da cewa’’ranar a d’akinka na gaya maka we re on this together,Yassir tunda har na iya danne zuciyata na had’a ka da Munirat inaso ka san na d’auki mission d’innan da mahimmanci,duk da na san cewa kashe Yashjub ba ya cikin tsarinmu amma idan har ka gaya mini dalilinka zan goya maka baya,kai ko da ace ba za
ma ka gaya mini dalilin naka ba Yassir zan goya maka baya I love you I want to see u win akan komai kai kuma a ko da yaushe zargina kake yi ban san ta ya zan nuna maka ina sonka ka yarda da ni da gaske ba, da ace na san taimakon ka da muka yi da ni da Mommy zai janyo mini haka daga gareka da ban yi ba tunda na lura tun lokacin da na d’an ja baya da kai saboda mu samu a fasa aurenmu a k’ara maka share har gobe baka yarda da ni ba Yassir’’
Ta k’arashe maganar tana mai durk’ushewa a wajen ta fashe da kuka.

Ahankali Yassir ya sauk’e ajiyar zuciya tashi d’aya ya fara ganin rashin kyautarwar sa,how can he not trust Kausar?despite irin gogayyar da take yi wajen ganin ta taimaka masa,shi sai yanzu ma kwakwalwar sa ta d’au charji amma kwanaki da d’azu gaba d’aya duk kishi ya rufe masa ido,tabbas everything is fair in love and war!’they are at war’ dan haka komai is fair kamar yadda ta fad’a dan ta had’asa da Munirat saboda su samu su yi achieving abunda suke so bai kamata ya dasa ayar tambaya a kanta ba wanda hakan ne farkon zargin nata da ya fara,tunda in komai ya yi daidai ya tafi yadda suke so ai sune da win.

Ahankali ya juyo yana jin tsananin tausayi da k’aunarta suna ratsa sa ya ce ‘’stand up’’
A ranshi yana mai cewa “inshaaAllah zai yi k’ok’ari ya goge tunanin’watak’il Kausar tana son Yashjub’ daga cikin zuciyar sa.But for last time akwai abunda yake son confirming ta yadda zai yarda da ita d’ari bisa d’ari.
Ganin ta k’i tashi ne ya sanya shi ya durk’usa ya kamota ya d’ago da ita tashi d’aya ya sakata a jikinsa yana mai bubbuga bayanta alamun rarrashi,sun jima a haka sai da ya ji ta yi shiru tukunna yace “Kausar one last question….na ga kina kuka sannan na ga hankalinki ya tashi kuma muna shiga da kika ga Yashjub da Manubiya kika juya za ki fita which means you can’t take it ba zaki iya ganin su a haka ba kenan!,inaso ki faiyyace mini dalilin reaction d’inki ta yadda komai zai tafi normal a tsakani na da ke.”

Da d’an fushi sakamokon tuno mata da abunda ya fi komai d’aga mata hankali da yayi tace “Yassir bani da lafiya amai nake ji shiyasa na yi deciding in tafi”
Kallon ta ya yi kafin yace’’amai kuma?….wanne irin rashin lafiya kike yi da zai baiyyana kishi da b’acin rai a kan fuskar ki?ko dai ba zaki iya tolerating ganinsu…’’

Turesa ta yi da dukkannin ragowar k’arfin da take ji tukunna ta juya a fusace ta nufi toilet…bin ta shima ya yi dan bai gama da ita ba yet.

Tana d’auko pts d’in ta juya za ta fita suka yi kicib’is da shi,kallon sa ta yi ta kamo hannunsa ta damk’a masa still tana kallon cikin idanunsa tace
“Bani da lafiya!”

Had’e girar sama da k’asa ya yi
kafin ya d’ago abunda ya ji ta saka masa a cikin hannunsa,sai da ya kai hannun nasa saitin fuskarsa kafin ya
janye idanunsa
a cikin nata
ya mayar kan tsinken.
Da mamaki k’arara kwance a kan fuskarsa yace
“What!!”
Sai kuma ya kalleta yace
“How?”

Cikin fushi tace
“Kut!!!tambaya ta ma kakeyi
‘How??’.“
Tsabar takaici kasa ma cigaba da tsayuwa tayi dan haka ta bangaje sa ta wuce.

Lumshe idanunsa yayi ya furzar da iska kafin ya bud’e ya juya da sauri ya bi bayanta.
Har ta kusan kaiwa bakin k’ofar d’akinta dan haka ya bi bayanta da d’an gudu ya cafkota ya juyo da ita.

Takaicine ya sanya ta fashewa da wani sabon kuka gwanin ban tausayi.
Tashi d’aya jikin Yassir ya sake yin sanyi,bai ma san lokacin da ya janyota ya sake rungume ta ba,yana mai jin tausayi da k’aunar.
Cikin muryar lallashi
yace “Haba Kausar,sai kace wata k’aramar Yarinya?
kar ki damu kanki mana just like last time wannan d’in ma za mu san yadda za mu yi da shi,plss ki daina kukan nan.”

Cikin kuka tace”Yassir ka cuceni!
Shikenan ni na zama sarauniyar zubar da ciki kenan???
kaf gidan nan
a kaff cikin y’an uwan ka mata
ko missing period babu wadda ta tab’a yi amman ni k’iri k’iri ka maidani karuwar k’arfi da yaji
saboda ni ba y’ar uwarka baceba ko?
Idan nace ‘A’a’ kuma
ka dasa ayar tambaya a kaina.”

Kamar zai yi kuka yace
“Not at all Kausar,kawai dama I was thinking ne”
shiruu ya yi
sai kuma yace
“Shikenan
I trust you now na fahimci komai komai ya wuce,na yi trusting d’inki daga yau inshaaAllah”

Turesa ta sake yi
tana kuka kamar ranta zai fita
da kyar ta iya cewa Yassir
what were you thinking before a kaina?”

Sake ruk’ota yayi
cikin sigar lallashi yace
“Na fad’a miki ki manta kawai”

A karo na uku ta sake turesa itama tukunna tace
“You have to tell me
me kake tunani a kaina da! Ba ya ga tunanin ka na bana sonka ba na kishin ka?what is it?”

Runtse idanunsa yayi ya d’an sunkuyar da kansa
tukunna ya d’ago ya furzar da iska ya bud’e idanuwan nasa sannan yace
“Okay fine!
Da Ina tunanin kamar kina son Yashjub ne.”


Da k’arfi tace
“What,sai kuma ta sake fashewa da kuka
kafin ta sa hannu ta kamo sa sai da suka isa k’ofar d’akin ta murza key ta bud’e tukunna tace
“Get out Yassir!
Tunda dak’ik’in tunaninka
da kishi sun rufe maka ido
ba na jin akwai abunda zan gaya maka kuma ka yarda da ni.Think what ever you want to think ban damu ba tunda duk bayanin da na yi maka ranar a d’akinka ba ka yarda ba
htta sirrin da Mommy ta gaya mana wanda ba kowa ake so ya ji ba duk sai da na gaya maka..amma shine still ba m yarda da ni ba??
shikenan!!
Ba komai.”

Ahankali yace “Kausar”

Cikin fushi tace
“trust is a very important thing Yassir taya ma za ka yi wannan tunanin a kaina?.
Baka san yadda ka yi hurting d’ina ba yau!
Just get out of my room”

Matsowa ya yi da sauri yai hugging d’inta yasa k’afa ya tura k’ofar ya rufe.

Ba yadda ba ta yi da shi ba
amman sam ta kasa kwatar kanta,dan haka ta fashe da wani sabon kuka.

Lallashinta ya shiga yi a chan k’asan zuciyarsa kuma yana daya sanin zarginta da yayi…

Sai da ya ji ta d’anyi shiru
tukunna ya cikata ya ce”na yi laifi
For the first time gashi na yi accepting na yarda na yi miki laifi,ki yi hak’uri
InshaaAllah ba zan sake ba
sannan daga yau ba zan sake dasa ayar tambaya a kanki game da komai ba I promise!
Duk abunda kika yi I’m going to trust you ko menene.
Pls Kausar forgive me”
Ya fad’i hakan ya na k’ok’arin durk’usawa.

Da sauri ta rikesa ta d’an girgiza masa kai…sake yunk’urawa yayi zai durk’usa dan haka tace
“Ya wuce ba komai”

Ahankali yace “thanks love..sosai sosai”
Sai kuma ya d’an kalli flat tummy d’inta yace”mu zauna sai mu yi magana ko?”

Jinjina kai kawai ta yi
daga haka ta wucesa ta isa
bakin gadonta ta zauna

Tana zama shima ya zauna
Ba tare da b’ata lokaci ba yace
“Yaushe kike so mu je asibitin??”

Sai da ta d’an d’auki lokaci tukunna tace”ba zan je asibiti ba,idan cikin ya kai wata biyar sai in fara zuwa awo
InshaaAllah”

Da sauri yace “Kausar pls
kar mu yi haka da ke mana!
Wacce irin magana ce wannan??”

Girgiza kai ta yi kafin tace
“Yassir ba zan iya yin wani abortion d’in ba fa,ai ka ji dai da kunnenka abunda Doctor yace mana the last time ko?…ko kana so mahaifata ta lalace tun kafin na fara tara iyali??
Besides
ai ni na sha gaya maka dama a ko da yaushe ba son rabuwa da babyna nake yi ba hak’uri kawai nakeyi ina biyeka.”
A hankali ta kamo hannunsa ta d’aura a kan cikinta tace
“This is our child,
kasancewarsa jininka ya sa na ji Ina matuk’ar k’aunarsa
saboda tsananin son da nake yi maka ba zan iya rabuwa da shi ba,wallahi ban tab’a jin so da k’auna bayan wanda nake yi maka ba sai a kan cikin nan!”

Damk’e hannunta ya yi da k’arfi dan ba kad’an ba
maganganunta sun shige sa sun yi tsananin tasiri sun ci galaba a kansa.
Ya jima maganganunta suna ratsa sa kafin a hankali cikin kwantar da murya yace
“Kausar!!
Daddy will kill me
Mommy ma Allah kad’ai ya san mai za ta ce…me”

Cikin katseshi tace
“Are u just thinking about yourself??”

Da sauri yace
“Of course not!.
Baby I’m also thinking about you mana
ban san wanne kallo duniya za ta yi miki ba!sannan kema ba wai sauk’i za ki samu daga wajen su Daddy ba.
Kinga dama da ni da ke muna da bak’in jini a wajen Daddy idan ya ji wannan batun ban san mai zai yi mana ba.
Ke da kanki kince 1% kawai gareni,na tabbatar idan Daddy ya ji wannan batu tou kashina ya bushe
Ni da shi babu taimako babu zaman lafiya daganan har abada
In that case
Yash will remain the king!…
Tayaya kike tunanin zan kula da ke da Baby idan hakan ya faru?
Kausar my company is not that good sannan a wajen Daddy ma 1% gare ni,idan muka haihu
while not yet stable
ya kike so Babyn namu ya rayu??
I love you sannan nima inason Babyn nan amman
we need to make sure munada plan da better future d’in da za mu bashi kafin mu yanke shawarar kawosa duniya”.


Shiruu duk sukayi kafin chan Kausar tace”Yassir na san abunda zan yi but har yanzu bani da tabbacin ko ka yarda dani d’ari bisa d’ari…”

Ahankali yace”Kausar mun rufe maganar nan fa!na yarda da ke mana”

“Ka tabbatar?”

“Na tabbatar“
Ya bata amsar yana kallonta
sannan ya d’aura da cewa
“Na fad’a miki na riga na yarda da ke Kausar,kawai dama inaso in yi confirming ne shiyasa na sake yi miki wachchar tambayr amman tun shigowata cikin d’akin nan da kika fara yi mini maganar farko tashi d’aya na yarda dake.Baki ga ban yi miki denying batun estate da cire taya ba?ko so kike in yi miki confessing??”
Ba tare da ya jira jin mai zata ce ba yace ‘’ok I did it’’
“If to say
ban yi trusting d’in ki ba kina tunanin zan fad’a miki haka ne?”

Ahankali ta sauke ajiyar zuciya tana ji inama ta saita record a lokacin da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login