Showing 144001 words to 147000 words out of 244445 words

Chapter 49 - MANNUBIYA COMPLETE HAUSA NOVEL PDF

24 Mar 2025

16437

yake confession d’innan da ta ajjiye as evidence d’in da za ta nuna ta tura sa prison bayan ya gama taimaka mata ta auri Yash…but with time inshaaAllah kafin ya gama taimaka mata amfaninsa ya k’are a wajenta za ta san yadda za ta yi ta sanya shi ya k’ara confessing!”

Ahankali ta gyara zamanta ta fuskancesa sosai
tukunna ta fara magana
“Yassir
Inaso ka cire kishi
da negative thinking ka duba future d’inka sannan Ina so ka san cewa ko ka yarda da wannan shawarar tawa da zan fad’i maka yanzu ko baka yarda ba ni dai ba zan tab’a zubar da cikin nan ba.

Akwai hanyar da za mu bi
mu haifi Babyn mu ya rayu cikin farin ciki…kuma hanyar ka sani itace silar warwarewar duk wani k’uncinka
amma we need to stick together sannan mu yarda da juna kafin komai”.

Jinjina kai yayi
alamun yana jinta kuma yana fahimta.

Ahankali ta sauk’e ajiyar zuciya tace”ka ce Daddy zai ji haushinka zai yi fushi da kai
watak’il forever idan har ya ji maganar cikin nan ko??”

Jin jina kai kawai yayi

“Good!
What if Yashjub ne a matsayinka??”

Da k’arfi yace
“What!!how??”

“Relax
I mean what if we frame him!.
Ka ga na farko
Ni kaina Daddy zai ji tausayi na
sannan zai yi fushi da Yashjub
Above all
zai shirya da kai ya janyoka a jikin sa sanna idan Yashjub yana tunanin wannan Babyn sa ne
tsaf za mu yi amfani da hakan
mu samu abunda mukeso”

Shiruuu kawai Yassir ya yi ya dafe kansa kafin chan ya d’ago ya kalleta tukunna yace
“Taya za ki yi hakan??
Taya hakan zai faru ??”

“Good
Bari kaji step one”
Ahankali ta matso ta zaiyyane masa komai…

Da farkon murmushi ya fara yi sai kuma ya mik’e tsaye yace
“Inaa! Kai!!!
no ba zai yiu ba.”

Mik’ewa ta yi ta rik’e hannunsa cikin son fahimtar da shi tace
“Nothing will happen between us”

“Yeah I know,but just the fact that za ki kwanta waje d’aya da shi that too n**kd,inaa Kausar ki kawo wani plan d’in gaskiya banda wannan.”

Murmushi ta yi tace
“Yasir a lokacin da abun zai faru fa ba ma ya cikin haiyyacin sa
balle ma ya gane komai.
Kuma that’s the only way da za a kamashi red handed.
Kar ka bari kishi ya rufe maka ido mu kasa cimma burin mu.”

Shiruu ya yi kafin yace
Kausar,ta ya zan bayar da d’a na a wani?
Tunda idan fa kika haihu
kowa Yashjub zai ce shine uban Yaron..ta yaya zan yi claiming rights d’ina a matsayin Uba?”

“Yassir ko wanne family suna da nasu secret d’in let’s this be ours(da ni da kai)..
Ka duba ka ga fa sau biyu kana attempting kashe Yashjub amma hakan bai yiu ba kuma dukiya har yanzu tana hannunsa,a gani na don ka hak’ura wannan Yaron ya zama nasa na shekara d’aya ko months mun samu da dabara da sharri da abubuwa komai ya dawo hannunka,it’s normal ai…
A da kai kad’ai ne ka ke ta had’a plans d’inka kana failing yanzu kuwa zan taimaka maka na san za mu yi winning.
Idan Daddy ya ga Yash ya mutu ga kuma jaririn Yaro mara gado bani da tantamar tashi d’aya Daddy zai tartara komai ya saka a sunan Yaron kar ka manta yadda Daddy ya ke ji da Yashjub dan wani abu ya shiga tsakaninsu sun yi fad’a ya daina kulasa ba shi zai sanya ya k’i son d’ansa bayan mutuwar sa ba.

Ka fahimce ni Yassir wins ne da mu ta ko wanne angle a cikin plan d’innan fa…kaga Yaro dai yana hannu na kuma kai zan aura at last komai ya zama naka Yashjub ya tafi sannan Yaro kuma ya taso a hannnun iyayensa mu kula da shi mu haifi k’annensa ya taso cikin ahalinsa,mai ya fi wannan riba??”

Shiruu Yassir ya yi kafin yace
“but idan kuma ita wachchar matar tasa ta haihu kinga mun yi 2 zero ko?dan kowa d’anta zai kwallafawa rai na san.
Tunda by now he’s supposed to be dead ta yadda zan ga bayan cikin amma ya k’i mutuwa a yadda yake gadinta d’innan ni ko ke bamu isa zuwa ko kusa da ita ba ballantana mu yi wani abun….

Murmushi Kausar ta yi kafin tace”don’t ask me Y and how,kawai inaso ka cire cikin Manubiya a lissafi dan wallahi ba ta isa ta haihu ba…kawai ka yi trusting d’ina when I say cikin nan ko one month bai isa ya k’ara a jikinta ba….”

Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace”I trust you Kausar.”

Murmushi ta yi tace”Thankyou..na san maganin da xa mu yiwa Yash amfani da shi zan rubuta
sunan sai mu je tare da ni da Yasmeen
amman ita kanta ba zan bari ta gane menene ba kawai zan
ce mata wanda ya ke sakani bacci ne akai mini recommending sabo.
Za ta nuna id card d’inta mu siyo maganin saboda ba za su
tab’a bani ba ni it’s super strong.”

Kallonta yayi sai kuma yace
“Da wuri haka?”

D’an zaro ido ta yi kafin tace
“Yassir tou sai yaushe?
Ai ba wai yanzu yanzu ba but inaso komai ya zama ready
ta yadda Ina ganin opportunity komai zai kammala.
Manya manyan jajayen layukan da suka fito B’aro B’aro a kan tsinken
nan ya na nuni da cewa cikin nan ya kwana biyu a jikina
Idan ba da kyar ba ya fi 1 month.

Kuma kaga idan ma zan ce inada ciki sai fa kamar irin 2 weeks haka bayan incidence d’in…

Shiruu yayi kafin chan yace
“Okay kausar
duk yadda kika ce hakan za a yi”.


Murmushi ta yi kafin ta yi hugging d’insa tace “Thankyou Yassir.
Thanks for trusting and understanding me”

A ranta kuma tace”Ashe ba ka da wayo…wannan plan A ne dole da kai za’ayi plan B kuwa ni kad’ai zan yi abuna dan ana tabbatar da cikin nan aure Yash ba zai zama abu mai wahala a gareni ba sai dai kawai ka ji a salansa…
Ya zama dole nima in nemi farin cikina in tsayawa kaina kuma in yi protecting Yash daga sharrinka…….”

“Tabbas ya fahimci Kausar kuma ya yarda da plan d’in dan akwai nasarori a tattare da plan d’in…..sannan zaifi jin dad’i idan Yash ya mutu da tabo da mugun suna.”
Yassir ya aiyyana hakan a cikin ransa yana mai sake saka saka ta a cikin jikinsa





Yashjub yana fita,d’akin ya rage daga Manubiya sai Yahanasu….a hankali Yahanasu ta mik’e ta k’araso inda take ta zauna a gefen gadon tukunna tace”me zan zuba miki??”
Zama Manu ta gyara ta ruk’o hannun Yahanasu kafin tace”Yaha Ina buk’atar taimakonki”
Shiruu Yahanasu ta yi ta d’an k’ura mata ido dan kamar ta fahimci mai za ta ce,kafin da kyar tace”anything! Manu..”

Ahankali Manubiya ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace”lokacin da aka kwancewa Ya Yash tayar mota kin san shi da kansa ya san kashesa ake so a yi ko?”
Ba ta jira jin me za ta ce ba ta d’aura da cewa”wannan karon ma kinga abunda ya faru ko? amma na ga kamar ba ya so na sani shiyasa nima ban nuna masa na sani d’in ba saboda inaso in taimaka nima kuma na san ba zai barni ba…. Yaha ba zan zauna in zuba ido in nad’e hannu ana wasa da rayuwar Mijina ba….”
Hawayen da suka zobo mata ne ya sa Yahanasu ta matso ta shiga goge mata fuska kafin da kyar ta samu ta iya cewa”yanzun ma haka kike suspecting ko!nima yanayin yadda na ga abun gaskiya dama na san hakan ne…”
Cikin jan hanci Manubiya ta zaiyyane mata abunda Yasira ta ji mutanen suna fad’a da suka shiga gidan k’awarta.
“Innalilla wa inna ilaihirrajiun”
Yahanasu take ta maimaitawa,tana jin gabanta yana wani irin bugawa..
Addu’arta d’aya Allah ya sa babu hannun Mommy a lamarin nan dan tabbas itakam za ta taimakawa Manubiya za su tsaya tsayin daka har sai sun gano gaskiyar lamari an kuma hukunta mai laifin kashe mutanen nan,justice must be served!.


A nan a take suka fara shirye shirye kuma suka yi alk’awarin ba za su bari Yash ya sani ba dan sun san zai yi yunk’urin ya hana su especially ma ita Manu da a yanzu ba shi da wani burin da ya wuce ta yi ta hutawa kawai.
Dama Yahanasu tana da connections kasancewar lawyer dan haka tun a lokacin ta shiga making phone calls aka fara shirye shiryen first step……


Yashjub ma sai chan dare ya samu ya dawo….Yahanasu ta wuce gida shi kuma ya nema waje ya zauna ya ruk’o hannun Manubiya….bai so Manubiya ta sani ba gudun kar ya d’aga mata hankali amma kuma ya yiwa kansa alk’awarin ba zai sake b’oye mata komai ba tun lokacin da su Yasira suka kusan had’a masa bomb da zancen Kausar,dan haka ya shiga zayyane mata yadda duk abunda ya faru da binciken da suka fara tun a yau…successfully cctv ta yi capturing incidence d’in tun shigowar y’an ta’addan har fitarsu kuma mutane biyu ogannnin cikinsu babu mask a fuskokinsu sannan an shaida guda d’aya dama ana neman san dead or alive…dan haka yanzu step d’in da suka d’auka shine na kama wannan mutumin ta wajen sa ne kawai za a gane waye ya turosu a ji komai dan muddin suka kamasa kalar interrogation d’in da za su yi masa dole ma ya fad’i gaskiya…….

Shiruuu Manubiya ta yi jikinta duk babu dad’i,kusan step d’in da ita da Yahanasu suka d’auka shi su Yash d’in suma suka d’auka amma su sun yi nisa dan su ko binciken cctv d’in ma ba su yi ba….kamar yadda ya ce ba ya so ya b’oye mata komai shiyasa itama ta fara k’ok’arin gaya masa shirinsu ita da Yahanasu amma sai ta ji yana cewa”dan Allah dan annabi ki kwantar da hankalinki,ba na son ki yi komai..if not because ba na son b’oye b’oye a tsakanin mu da ba zan gaya miki ba,dan haka dan Allah ki kwantar da hankalinki ki kular mun da ku..inshaaAllah all will be fine,ok?”

Ajiyar zuciya ta sauk’e,a take ta fasa gaya masa saboda har ga Allah tana son ta taimaka dan haka kawai ta jini jina kai a hankali ta yi huggin d’insa…


Ba dan Yash ne da kansa ba da babu abunda zai sa Doctor ya bar Manubiya ta fita ba tare da ya sallameta ba…sai da ya sake dubata tukunna suka tafi dubo
Baba ita da Yashjub…

Had’add’en private hospital mai kyau da tsada Yash ya kai sa dan har ya ma fi na family Doctor d’insu da Manubiyan take kwance.

A harabar asibitin suka tarar da Jidda a tsaye ta kauda kai gefe da wani,sai da suka k’arasa tukunna suka fahimci ashe Ya Yusuf ne…
Da mutuntawa suka gaisa shi da Yash kafin ya kalli Manu itama ya gaida ita daga haka ya yi musu sallama ya tafi…
Yashjub ne ya iya amsashi dan daga Manubiya har Jiddan babu wanda ya tanka masa, ita Jidda haushi da tsanar sa ne yasa tunda suka fito ba ta ce komai ba Manubiya kuwa tsantsar mamaki ne ya hanata yin magana dan ba ta yi expecting ganin Yusuf da Jidda a tare ba.
Sai da Yashjub ya rakasu bakin k’ofar d’akin tukunna ya juya bayan yace “su shiga zai je ya d’an siyo abu idan ya dawo sai ya ga jikin Baban su wuce..”
Da “to”suka amsa shi daga haka ya wuce…ko gama fita daga corridor d’in bai yi ba Manubiya tace”Jidda me kike yi da Yusuf a waje???”
Numfashi Jidda ta fesar kafin tace”Baba ne ya ce in rako sa…”
Kukan da ya taho mata ne ya sa ta yi shiru ta fara kokawar danne wa..cikin rashin jin dad’i da rashin fahimta Manubiya tace “Jidda ai da sai ku tsaya a nan da kika fito ya wuce ke kuna ki juya meye naki na yi masa rakiya har chan waje?? Jidda Yusuf ne fa!!!”

Cikin sauk’e ajiyar zuciya tace”da ya zo ya gama dubiyar ya tashi tafiya shine ya kalle ni yace wai ‘ba rakiya!’
‘In zo in rakasa’! a gaban Baba da Inna tsabar ba shi da tarbiyya.Sai da ya fad’a sau uku tukunna Baba ya kalle ni yace”mu raka sa da ni da Muhsin amma muna fitowa ya cewa Muhsin d’in ya koma ni kuma ya kamo hannu na ya jani kamar wata kayan wanki saboda ya ga Ina shirin komawar,ko da muka fita da na fara k’ok’arin juyawa gani na yi yana shirin runguma ta shiyasa na tsaya kawai.
Tsabar rashin sanin darajar manya saboda Allah adda Manu ta ya Baba zai ce mu rakosa amma ya kora Muhsin.”

Cikin rashin Jin dad’i Manubiya tace”kuma wai a haka ace Baba ba ya ganin laifin Yusuf??”

Ajiyar zuciya Jidda ta sauk’e kafin tace”yana gani fa! kawai kawar da kai yake yi wasu lokutan saboda gudun magana amma ni na san yana gani…ba ki da lafiya ne shiysa ban gaya miki abunda ya faru ba….kin san tunda ya yi kud’i ba shi da Aboki sama da Kaka mallan to shekaran jiya Kaka mallan d’in ya nemi ganin ya Nafi’u da ya musbah,Ya musbah bai je ba sai ya Nafi’u,shine fa tsabar rainin wayo kaka mallan d’in yake ce masa wai ya fad’i ko nawa yake so su basa ya saka baki a yi aurena da Ya Yusuf,wai duba da abunda yake ta faruwa a tsakanin Baba da su Baba habu ya san Baba maybe ya chanza ra’ayi dan haka Ya Nafi’u ya yi naming price ko nawa su bashi ya yi convincing Baba. Shi kuma kaka mallan zai tsayawa Ya Yusuf ko su Uncle ba su yarda ba a d’aura.”

Cikin takaici Manubiya tace”kutt me ya ce masa shi kuma?”

“Kema kin san ai ya Nafi’u ba zai yarda ba…wane tudu wane gangare suka bi daga haka dai hayaniya ta fara tashi,shine fa akayi fad’a da ya Nafi’u da kaka mallan har da Uncle a case d’in wanda da ga jin hayaniya ya afka parlourn ya yi ruwa ya yi tsaki.To dai daga k’arshe Baba ne ya je ya raba da kyar ta hanyar janye ya Nafi’un …shine fa cikin dare wajajen k’arfe d’aya kamar waenda aljanunsu suka tashi haka kurum Uncle ya zo ya shigo har cikin d’aki wai Baba ya zab’a ko su ko ya Nafi’u,saboda ba zai you Yaro ya yi musu rashin mutunci ba kuma ya ci gaba da huld’a da shi yana shigo musu cikin gidan ba. Haka nan dai suka yi ta hayaniya wallahi kamar mata daga k’arshe Baba ya ja bargo ya kwanta kawai ya rabu da su,shine suka yanke mana wutar d’akin da na d’akin Muhsin kuma suka d’auko wasu takardu wai d’akin Muhsin d’in ma rushesa za su yi filin rabi ne na Baba rabi kuma nasu…a ranar babu wanda ya runtsa.Ya Yusuf dai shi yake ta k’ok’arin hanasu Anty Umma ma har kuka ta yi tana lallab’asu tana so ta ga an rufe case d’in amma sai tujara suke yi kaka mallan yana gefe yana mana gori kala kala..har da cewa ya Musbah ya gudu ya barmu,kema wai an bi kwad’ayi an aura miki mai kud’i gashi ba ya tsinana mana uwar komai ko kwayar shinkafa bamu da ita rabon da ya ga mun yi girki har ya manta,wai dama shiyasa ya ke so a aurar da ni a Ya Yusuf ya rufa mana asiri ya dinga ciyar da mu amma mu kuma mun k’i yarda.”

Mun d’auka maganar d’akin Muhsin fad’i kawai suke yi ashe su sun d’auki abun serious dan da muka zo duba ki bricklayers suka nemo wajen mutun shidda suka nuna musu d’akin aka fara rushewa…Baba yana d’aki sai jin rushe rushe ya yi da hayaniya,baya so ya kula su yace tun last two weeks ya lura kawai neman masifa suke yi da shi shiyasa ya k’i fitowa ya tsaya a d’aki ya yi ta kiran Ya Musbah shi kuma ya k’i d’auka to inaga bak’in cikin hakan ne ya sa muka shigo muka tarar da shi a sume……

“Innalillahi wa Ina ilaihirrajiun”
Manu ta ke ta maimaitawa kafin ta share hawayenta ita ta ma rasa bakin magana,chan tace”kuma har yau bai zo ba?”
Jinjina kai Jidda ta yi alamun “eh”kafin tace “inna tace mini d’azu da na fita siyo mana abinci ya kira Baba ya yi masa ya jiki inaga message d’in da na yi masa ya gani sannnan ya ce gobe zai zo….”
A hankali Manu tace”da ke da Muhsin mu je gidana mana kafin mu ga yadda hali zai yi su Inna kuma tunda suna nan they are safe dan gaskiya Jidda ba za ku koma gidan nan ba abun ya yi yawa an kai peak!”

Murmushi Jidda ta yi cikin jin tsananin tausayin kansu tace”Adda Manu kin manta su waye dangin mijin na ki ne?ai kema kin san zamn mu a cikin gidan ki ba abu mai yiwuwa bane ba….”

Shiruu duk suka yi kafin Jidda ta sake cewa”Ya Yusuf dai tunda ya zo ya ke ta bada hak’uri kuma ya kawo takardu wai ya siye mana gaba d’aya filin daga wajensu har ya kira an fara gyarawa…..
To dai wannan karon gaskiya Baba ya zuciya dan tunda Ya Yusuf ya zo bai sake da shi ba daga amsa gaisuwa ya ja bakinsa ya yi gum!Inna ce ma ta d’an saurare sa kad’an,har da cewa wai ya sayi sabon fili zai yi maaana gini waye waye Baba ya yi hak’uri kar ya damu dan ya Musbah ya daina kula mu inshaaAllah indai yana raye da shi da Inna ba za su yi kukan rashin d’a ba.”

“Wai shi Yusuf yana nufin aikin bankin ne duk ya azurtashi haka??”

“Hmm”Jidda tace kafin ta d’aura da cewa”Siyama ta ce mini idan fa kika shiga side d’in Baba Habu za ki d’auka a hotel kike tsabar yadda ya gyara sa,ya yi interlock a gaba d’aya compound d’in gidan ya sakawa iyayensa solar shi kuwa gidan da ya gama ya koma akace har abun tsoro hawa biyu fa,motocin sa fa uku,wayar sa wadda ta fito last month ita yake rik’ewa…y’an unguwa sai magana ake yi amma iyayensa da kaka mallan sunce hassada ce ya ci gaba da business d’insa ya dage da addu’a kawai ya yi harkar gabansa kar ya kula kowa….”

“Ha’a Manu yaushe kika zo??”
cewar Inna wadda ta fito da niyyar bin bayan Jidda dan ta ji shirun ya yi yawa…a hankali Manu ta tafi jikinta ta rungume ta…cikin rashin jin dad’i inna tace “yanzu Yarinyar nan sai da kika fito?duba fa hannunki har da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login